< 2 Sama’ila 17 >

1 Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
Moreover Ahithophel disse a Absalom: “Deixe-me agora escolher doze mil homens, e me levantarei e perseguirei depois de David esta noite”.
2 Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
Eu irei atrás dele enquanto ele estiver cansado e exausto, e o farei ter medo”. Todas as pessoas que estão com ele fugirão. Eu atacarei apenas o rei,
3 in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
e trarei de volta todo o povo até você. O homem que vocês procuram é como se todos tivessem voltado. Todo o povo deve estar em paz”.
4 Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
O ditado agradou bem a Absalom, e a todos os anciãos de Israel.
5 Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
Então Absalom disse: “Agora chame Hushai de Arquiteto também, e vamos ouvir o mesmo que ele diz”.
6 Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
Quando Hushai chegou a Absalom, Absalom falou com ele, dizendo: “Ahithophel falou assim”. Devemos fazer o que ele diz? Se não, fale mais alto”.
7 Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
Hushai disse a Absalom: “O conselho que Ahithophel deu desta vez não é bom”.
8 Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
Hushai disse ainda: “Você conhece seu pai e seus homens, que são homens poderosos, e que são ferozes em suas mentes, como um urso roubado de seus filhotes no campo. Seu pai é um homem de guerra e não vai se alojar com o povo.
9 Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
Eis que ele está agora escondido em algum buraco, ou em algum outro lugar. Acontecerá, quando alguns deles tiverem caído no início, que quem o ouvir dirá: “Há uma matança entre o povo que segue Absalom!
10 Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
Mesmo aquele que é valente, cujo coração é como o coração de um leão, derreterá totalmente; pois todo Israel sabe que seu pai é um homem poderoso, e aqueles que estão com ele são homens valentes.
11 “Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
Mas aconselho que todo Israel esteja reunido a vocês, desde Dan até Berseba, como a areia que está junto ao mar para a multidão; e que vocês vão à batalha em sua própria pessoa.
12 Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
Portanto, iremos sobre ele em algum lugar onde ele será encontrado, e o iluminaremos quando o orvalho cair no chão, então não deixaremos tanto como um dele e de todos os homens que estão com ele.
13 In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
Além disso, se ele entrou em uma cidade, então todo Israel trará cordas para aquela cidade, e nós a puxaremos para dentro do rio, até que não haja uma pequena pedra encontrada lá”.
14 Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
Absalom e todos os homens de Israel disseram: “O conselho de Hushai, o Arquiteto, é melhor do que o conselho de Ahithophel”. Pois Javé tinha ordenado a derrotar o bom conselho de Aitofel, com a intenção de que Javé pudesse trazer o mal sobre Absalão.
15 Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
Então Hushai disse a Zadok e a Abiathar, os sacerdotes: “Ahithophel aconselhou Absalom e os anciãos de Israel dessa forma; e eu aconselhei dessa forma.
16 Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
Agora, portanto, envie rapidamente, e diga a David, dizendo: “Não se hospedem esta noite nos vaus do deserto, mas por todos os meios passem, para que o rei não seja engolido, e todo o povo que estiver com ele””.
17 Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
Agora Jonathan e Ahimaaz estavam hospedados por En Rogel; e uma criada costumava ir e se reportar a eles, e eles foram e disseram ao rei David; pois não podiam arriscar ser vistos entrando na cidade.
18 Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
Mas um menino os viu, e disse a Absalom. Então os dois foram embora rapidamente e chegaram à casa de um homem em Bahurim, que tinha um poço em sua corte; e foram até lá.
19 Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
A mulher pegou e espalhou a cobertura sobre a boca do poço, e espalhou grãos esmagados sobre ele; e nada se sabia.
20 Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
Os servos de Absalom foram até a casa da mulher; e disseram: “Onde estão Ahimaaz e Jonathan? A mulher disse-lhes: “Eles passaram por cima do riacho de água”. Quando os procuraram e não puderam encontrá-los, voltaram a Jerusalém.
21 Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
Depois de terem partido, saíram do poço e foram dizer ao rei Davi; e disseram a Davi: “Levantem-se e passem rapidamente sobre a água; pois assim Ahithophel aconselhou contra vocês”.
22 Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
Então David se levantou, e todas as pessoas que estavam com ele, e passaram por cima do Jordão. À luz da manhã não faltava nenhum deles que não tivesse passado sobre o Jordão.
23 Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
Quando Ahithophel viu que seu conselho não foi seguido, selou seu burro, levantou-se, foi para casa, arrumou sua casa e enforcou-se; e morreu, e foi enterrado no túmulo de seu pai.
24 Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
Então David veio para Mahanaim. Absalom passou sobre o Jordão, ele e todos os homens de Israel com ele.
25 Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
Absalom colocou Amasa sobre o exército em vez de Joab. Agora Amasa era filho de um homem cujo nome era Ithra, o israelita, que foi para Abigail, filha de Naash, irmã de Zeruia, mãe de Joab.
26 Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
Israel e Absalão acamparam na terra de Gileade.
27 Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
Quando David veio a Mahanaim, Shobi filho de Nahash de Rabbah dos filhos de Ammon, e Machir filho de Ammiel de Lodebar, e Barzillai o Gileadita de Rogelim,
28 suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
brought camas, bacias, vasos de barro, trigo, cevada, farinha, grão torrado, feijão, lentilhas, grão torrado,
29 da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”
mel, manteiga, ovelhas e queijo do rebanho, para David e para as pessoas que estavam com ele para comer; pois eles disseram: “O povo está faminto, cansado e sedento no deserto”.”

< 2 Sama’ila 17 >