< 2 Sama’ila 17 >

1 Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
اخیتوفل به ابشالوم گفت: «دوازده هزار سرباز به من بده تا همین امشب داوود را تعقیب کنم.
2 Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
حال که او خسته و درمانده است به او حمله می‌کنم تا افرادش پراکنده شوند. آنگاه فقط پادشاه را می‌کشم
3 in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
و تمام افرادش را به نزد تو باز می‌گردانم. با کشته شدن پادشاه بدون شک همهٔ همراهانش بدون اینکه آسیبی ببینند نزد تو برخواهند گشت.»
4 Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
ابشالوم و همهٔ بزرگان اسرائیل این نقشه را پسندیدند.
5 Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
ولی ابشالوم گفت: «نظر حوشای ارکی را نیز در این باره بپرسید.»
6 Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
وقتی حوشای آمد، ابشالوم نقشهٔ اخیتوفل را برای او تعریف کرد و از او پرسید: «نظر تو چیست؟ آیا با نقشهٔ او موافقی یا طرح دیگری داری؟»
7 Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
حوشای جواب داد: «فکر می‌کنم پیشنهادی که این بار اخیتوفل داده خوب نیست.
8 Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
پدرت و افراد او را خوب می‌شناسی. آنها جنگجویان شجاعی هستند. حال، مانند خرس ماده‌ای که بچه‌هایش را دزدیده باشند خشمگین هستند. پدرت سرباز کهنه‌کار و با تجربه‌ای است و شب در میان سربازان خود نمی‌ماند.
9 Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
احتمالاً در غاری یا جای دیگری مخفی شده است. کافی است بیرون بیاید و حمله کند و چند نفر از افراد تو را بکشد، آنگاه همه جا شایع می‌شود که پیروان تو سرکوب شده‌اند.
10 Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
آنگاه شجاعترین افرادت، حتی اگر دل شیر هم داشته باشند، از ترس روحیهٔ خود را خواهند باخت. چون تمام اسرائیلی‌ها می‌دانند که پدرت چه مرد جنگاوری است و سربازانش چقدر شجاع هستند.
11 “Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
پس پیشنهاد من این است که تمام سربازان اسرائیل را از سراسر کشور، یعنی از دان تا بئرشبع، جمع کنی تا نیروی بزرگی داشته باشی، و خودت هم شخصاً فرماندهی آنها را به عهده بگیری.
12 Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
داوود و افرادش را هر جا باشند، پیدا می‌کنیم و آنها را غافلگیر کرده، همه را از بین می‌بریم تا یک نفرشان هم زنده نماند.
13 In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
اگر داوود به شهری فرار کند، تمام سپاه اسرائیل که در اختیار تو است دیوارهای شهر را با کمند به نزدیکترین دره سرنگون می‌کنند تا با خاک یکسان شود و سنگی در آن نماند.»
14 Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
پس ابشالوم و تمام مردان اسرائیل گفتند: «پیشنهاد حوشای بهتر از پیشنهاد اخیتوفل است.» خداوند ترتیبی داده بود که پیشنهاد خوب اخیتوفل پذیرفته نشود تا به این وسیله ابشالوم را گرفتار مصیبت سازد.
15 Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
بعد حوشای نظر اخیتوفل و پیشنهادی را که خودش به جای آن کرده بود، به صادوق و اَبیّاتار کاهن گزارش داد.
16 Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
حوشای به آنها گفت: «زود باشید! داوود را پیدا کنید و به او بگویید که امشب در کنار رود اردن نماند، بلکه هر چه زودتر از رود عبور کند و گرنه او و تمام همراهانش کشته خواهند شد.»
17 Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
یوناتان و اخیمعص، برای اینکه دیده نشوند کنار چشمه عین روجل پنهان شده بودند و کنیزی برای ایشان خبر می‌آورد تا آنها نیز خبر را به داوود پادشاه برسانند.
18 Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
اما وقتی می‌خواستند از عین روجل پیش داوود بروند، پسری آنها را دید و به ابشالوم خبر داد. پس یوناتان و اخیمعص به بحوریم گریختند و شخصی آنها را در چاهی که در حیات خانه‌اش بود پنهان کرد.
19 Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
زن او سرپوشی روی چاه گذاشت و مقداری حبوبات روی آن ریخت تا کسی از موضوع باخبر نشود.
20 Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
وقتی افراد ابشالوم آمدند و سراغ اخیمعص و یوناتان را از آن زن گرفتند او گفت: «از رودخانه عبور کردند.» آنها پس از جستجوی زیاد، دست خالی به اورشلیم برگشتند.
21 Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
بعد از رفتن افراد ابشالوم، اخیمعص و یوناتان از چاه بیرون آمدند و بدون معطلی پیش پادشاه رفتند و گفتند: «زود باشید امشب از رود عبور کنید!» سپس برایش تعریف کردند که چگونه اخیتوفل نقشهٔ کشتن او را کشیده است.
22 Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
پس داوود و همراهانش شبانه از رود اردن عبور کردند و قبل از سپیدهٔ صبح، همه به آن طرف رسیدند.
23 Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
وقتی اخیتوفل دید ابشالوم پیشنهاد او را رد کرده است، الاغ خود را پالان کرد و به شهر خود رفت. او به کارهایش سروسامان بخشید و رفت خود را به دار آویخت. مردم جنازهٔ او را در کنار قبر پدرش به خاک سپردند.
24 Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
طولی نکشید که داوود به محنایم رسید. ابشالوم هم تمام سپاه اسرائیل را بسیج کرد و به آن طرف رود اردن برد.
25 Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
ابشالوم، عماسا را به جای یوآب به فرماندهی سپاه تعیین کرد. (عماسا پسر خالهٔ یوآب بود. پدرش یترای اسماعیلی و مادرش ابیجایل، دختر ناحاش و خواهر صرویه مادر یوآب بود.)
26 Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
ابشالوم و سپاه اسرائیل در سرزمین جلعاد اردو زدند.
27 Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
وقتی داوود به محنایم رسید، شوبی (پسر ناحاش که از اهالی شهر ربهٔ عمون بود) و ماخیر (پسر عمی‌ئیل از لودبار) و برزلائی جلعادی (از روجلیم) به استقبال او آمدند.
28 suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
آنها برای داوود و همراهانش وسایل خواب و خوراک آوردند، از جمله دیگهای خوراک‌پزی، کاسه‌ها، گندم و آرد جو، غلهٔ برشته، باقلا، عدس، نخود، عسل، کره، پنیر و چند گوسفند. آنها می‌دانستند بعد از این راهپیمایی طولانی در بیابان، بدون شک خسته و گرسنه و تشنه هستند.
29 da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”

< 2 Sama’ila 17 >