< 2 Sama’ila 17 >
1 Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
And Ahithophel said to Absalom, “Please let me choose twelve thousand men, and I arise and pursue after David tonight,
2 Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
and come on him, and he [will be] weary and feeble-handed, and I have caused him to tremble, and all the people who [are] with him have fled, and I have struck the king by himself,
3 in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
and I bring back all the people to you—as the turning back of the whole [except] the man whom you are seeking—[then] all the people are [at] peace.”
4 Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
And the word is right in the eyes of Absalom, and in the eyes of all [the] elderly of Israel.
5 Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
And Absalom says, “Now call for Hushai the Archite also, and we hear what [is] in his mouth—even he.”
6 Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
And Hushai comes to Absalom, and Absalom speaks to him, saying, “According to this word Ahithophel has spoken; do we do his word? If not, you—speak.”
7 Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
And Hushai says to Absalom, “The counsel that Ahithophel has counseled [is] not good at this time.”
8 Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
And Hushai says, “You have known your father and his men, that they [are] heroes, and they are bitter in soul as a bereaved bear in a field, and your father [is] a man of war, and does not lodge with the people;
9 Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
behold, now, he is hidden in one of the pits, or in one of the places, and it has been at the falling among them at the commencement, that the hearer has heard and said, There has been a slaughter among the people who [are] after Absalom;
10 Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
and he also, the son of valor, whose heart [is] as the heart of the lion, utterly melts, for all Israel knows that your father is a hero, and those with him [are] sons of valor.
11 “Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
So that I have counseled: let all Israel be diligently gathered to you, from Dan even to Beer-Sheba, as the sand that [is] by the sea for multitude, and you yourself are going in the midst;
12 Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
and we have come to him in one of the places where he is found, and we [are] on him as the dew falls on the ground, and there has not been left of him and of all the men who [are] with him even one.
13 In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
And if he is gathered to a city, then they have caused all Israel to carry ropes to that city, and we have drawn it to the brook until there has not even been found a stone there.”
14 Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
And Absalom says—and all the men of Israel, “The counsel of Hushai the Archite [is] better than the counsel of Ahithophel”; and YHWH willed to make void the good counsel of Ahithophel for the sake of YHWH’s bringing the calamity to Absalom.
15 Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
And Hushai says to Zadok and to Abiathar the priests, “Thus and thus Ahithophel has counseled Absalom and the elderly of Israel, and thus and thus I have counseled;
16 Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
and now, send quickly, and declare [it] to David, saying, Do not lodge in the plains of the wilderness tonight, and also, certainly pass over, lest there is a swallowing up of the king and of all the people who are with him.”
17 Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
And Jonathan and Ahimaaz are standing at En-Rogel, and the maidservant has gone and declared [it] to them—and they go and have declared [it] to King David—for they are not able to be seen to go into the city.
18 Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
And a youth sees them, and declares [it] to Absalom; and both of them go on quickly, and come to the house of a man in Bahurim, and he has a well in his court, and they go down there,
19 Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
and the woman takes and spreads the covering over the face of the well, and spreads the ground grain on it, and the thing has not been known.
20 Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
And the servants of Absalom come to the woman at the house, and say, “Where [are] Ahimaaz and Jonathan?” And the woman says to them, “They passed over the brook of water”; and they seek, and have not found, and return to Jerusalem.
21 Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
And it comes to pass, after their going on, that they come up out of the well, and go and declare [it] to King David, and say to David, “Rise, and pass over the waters quickly, for thus has Ahithophel counseled against you.”
22 Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
And David rises, and all the people who [are] with him, and they pass over the Jordan, until the morning light, until not one has been lacking who has not passed over the Jordan.
23 Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
And Ahithophel has seen that his counsel was not done, and he saddles the donkey, and rises and goes to his house, to his city, and gives charge to his household, and strangles himself, and dies, and he is buried in the burying-place of his father.
24 Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
And David came to Mahanaim, and Absalom passed over the Jordan, he and all the men of Israel with him;
25 Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
and Absalom has set Amasa over the host instead of Joab, and Amasa [is] a man’s son whose name is Ithra the Israeli who has gone in to Abigail, daughter of Nahash, sister of Zeruiah, mother of Joab;
26 Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
and Israel encamps with Absalom [in] the land of Gilead.
27 Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
And it comes to pass at the coming in of David to Mahanaim, that Shobi son of Nahash, from Rabbah of the sons of Ammon, and Machir son of Ammiel, from Behold-Debar, and Barzillai the Gileadite, from Rogelim,
28 suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
[have brought] bed, and basin, and earthen vessel, and wheat, and barley, and flour, and roasted [grain], and beans, and lentiles, and roasted [pulse],
29 da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”
and honey, and butter, and sheep, and cheese of cows; they have brought [these] near for David, and for the people who [are] with him to eat, for they said, “Your people [are] hungry, and weary, and thirsty, in the wilderness.”