< 2 Sama’ila 17 >

1 Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
Řekl ještě Achitofel Absolonovi: Nechť medle vyberu dvanácte tisíc mužů, abych vstana, honil Davida noci této.
2 Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
A dostihna ho, dokudž jest ustalý a zemdlené má ruce, předěsím jej, a uteče všecken lid, kterýž jest s ním, i zamorduji krále samého.
3 in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
A tak obrátím všecken lid k tobě; nebo jako bych je všecky obrátil, když zhyne ten muž, kteréhož ty hledáš. O lid ty se nic nestarej.
4 Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
I líbila se ta řeč Absolonovi i všechněm starším Izraelským.
5 Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
A však řekl Absolon: Zavolej sem hned Chusai Architského, abychom slyšeli, co i on mluviti bude.
6 Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
Když pak přišel Chusai k Absolonovi, mluvil k němu Absolon, řka: Takto mluvil Achitofel. Máme-li učiniti vedlé řeči jeho, čili nic? Pověz ty.
7 Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
Tedy řekl Chusai Absolonovi: Neníť dobrá rada, kterouž dal Achitofel nyní.
8 Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
Dále mluvil Chusai: Ty víš o otci svém i mužích jeho, že jsou udatní, k tomu zjitření na mysli, jako nedvědice osiřelá v poli. Nadto otec tvůj jest muž válečný, kterýž nebude nocovati s lidem.
9 Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
Nýbrž nyní spíše v záloze stojí v nějaké jeskyni, aneb v některém jiném místě. I stalo by se, jestliže by kteří padli z těch tvých při začátku, že každý, kdož by o tom uslyšel, řekl by: Stala se porážka v lidu, kterýž postoupil po Absolonovi.
10 Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
A tak by i silných reků srdce, kteréž jest jako srdce lva, škodlivě osláblo; nebo ví všecken Izrael, že jest zmužilý otec tvůj, a silní ti, kteříž jsou s ním.
11 “Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
Ale radím, abys, shromáždě k sobě všecken Izrael od Dan až do Bersabé, kterýž v množství jest jako písek při moři, ty sám životně vytáhl k boji.
12 Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
A tak potáhneme proti němu, na kterém by koli místě nalezen býti mohl, a připadneme na něj, jako padá rosa na zemi; i nepozůstaneť z něho, totiž ze všech mužů, kteříž jsou při něm, ani jednoho.
13 In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
Jestliže by se pak shrnul do města, snesou všecken lid Izraelský k tomu městu provazy, a vtrhneme je až do potoka, tak aby tam ani kaménka nebylo lze najíti.
14 Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
I řekl Absolon a všickni muži Izraelští: Lepšíť jest rada Chusai Architského, než rada Achitofelova. Hospodin zajisté to způsobil, aby zrušena byla rada Achitofelova, kteráž sic dobrá byla, aby tak uvedl Hospodin na Absolona zlé věci.
15 Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
Oznámil pak to Chusai Sádochovi a Abiatarovi kněžím: Tak a tak radil Achitofel Absolonovi a starším Izraelským, ale já takto a takto jsem radil.
16 Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
Nyní tedy pošlete rychle a oznamte Davidovi, řkouce: Nezůstavej přes noc na rovinách pouště, ale přeprav se bez meškání, aby snad nebyl sehlcen král i všecken lid, kterýž jest s ním.
17 Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
Jonata pak a Achimaas stáli u studnice Rogel. I šla tam děvečka a pověděla jim, aby oni jdouce, oznámili to králi Davidovi; nebo nesměli se ukázati aneb vjíti do města.
18 Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
A však uzřel je služebník, a oznámil Absolonovi. Pročež odšedše oba rychle, vešli do domu muže v Bahurim, kterýž měl studnici na dvoře svém. I spustili se do ní.
19 Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
A žena vzavši plachtu, rozestřela ji na vrch studnice, a nasypala na ni krup. A tak nebyla ta věc spatřína.
20 Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
Nebo když přišli služebníci Absolonovi k ženě do domu a řekli: Kde jest Achimaas a Jonata? odpověděla jim žena: Přešliť jsou ten potok. Hledavše tedy a nic nenalezše, navrátili se do Jeruzaléma.
21 Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
A když oni odešli, tito vystoupivše z studnice, šli a oznámili králi Davidovi a řekli jemu: Vstaňte a přepravte se rychle přes vodu, nebo toto radil proti vám Achitofel.
22 Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
Protož vstav David a všecken lid, kterýž byl s ním, přepravili se přes Jordán, prvé než se rozednilo; a nezůstal ani jeden, ješto by se nepřepravil přes Jordán.
23 Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
Tedy Achitofel vida, že se nestalo vedlé rady jeho, osedlal osla, a vstav, odjel do domu svého, do města svého. A učiniv pořízení v čeledi své, oběsil se a umřel; i pochován jest v hrobě otce svého.
24 Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
David pak byl již přišel do Mahanaim, když se Absolon přepravil přes Jordán, on i všecken lid Izraelský s ním.
25 Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
A tu ustanovil Absolon Amazu místo Joába nad vojskem. (Byl pak Amaza syn muže, jehož jméno bylo Jetra Izraelský, kterýž všel k Abigail dceři Náchas, sestře Sarvie matky Joábovy.)
26 Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
I položil se Izrael a Absolon v zemi Galád.
27 Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
Stalo se pak, když přišel David do Mahanaim, že Sobi syn Náchas z Rabbat synů Ammon, a Machir syn Amielův z Lodebar, a Barzillai Galádský z Rogelim,
28 suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
Lůže, číše a nádoby hliněné, též pšenice, ječmene, mouky, krup, bobu, šocovice a pražmy,
29 da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”
Ano i medu, másla a ovcí i syrů kravských přinesli Davidovi a lidu, kterýž s ním byl, aby jedli. Nebo řekli: Lid ten jest hladovitý a ustalý, i žíznivý na té poušti.

< 2 Sama’ila 17 >