< 2 Sama’ila 16 >

1 Sa’ad da Dawuda ya yi ɗan nesa da ƙwanƙolin, sai ga Ziba mai hidimar Mefiboshet, yana jira yă tarye shi. Yana da jerin jakuna da sirdi suna ɗauke da dunƙulen burodi ɗari biyu, da ƙosai busasshen inabi ɗari ɗaya, da kosan’ya’yan itace ɓaure guda ɗari, da salka ruwan inabi.
Davut tepenin doruğunu biraz geçince, Mefiboşet'in hizmetkârı Siva palan vurulmuş ve üzerlerine iki yüz ekmek, yüz salkım kuru üzüm, yüz tane taze meyve ve bir tulum şarap yüklü iki eşekle onu karşıladı.
2 Sarki ya ce wa Ziba, “Me ya sa ka kawo waɗannan?” Ziba ya ce, “Jakuna domin iyalin gidan sarki su hau ne, burodi da’ya’yan itace domin mutane su ci, ruwan inabi kuma domin waɗanda suka gaji a hamada.”
Kral, Siva'ya, “Bunları niçin getirdin?” diye sordu. Siva, “Eşekler kral ailesinin binmesi, ekmekle taze meyve hizmetkârların yemesi, şarapsa kırda yorgun düşenlerin içmesi için” diye yanıtladı.
3 Sai sarki ya ce, “Ina jikar maigidanka?” Ziba ya ce, “Yana zaune a Urushalima gama yana tsammani cewa, ‘Yau gidan Isra’ila za su mayar mini da sarautar kakana.’”
Kral, “Efendin Saul'un torunu nerede?” diye sordu. Siva, “Yeruşalim'de kalıyor” diye yanıtladı, “Çünkü ‘İsrail halkı bugün atamın krallığını bana geri verecek’ diye düşünüyor.”
4 Sai sarki ya ce wa Ziba, “Duk abin da yake na Mefiboshet, ya zama naka.” Ziba ya rusuna ya ce, “Bari in dinga samun tagomashi a gabanka ranka yă daɗe.”
Kral, “Mefiboşet'in her şeyi senindir” dedi. Siva, “Önünde eğilirim, efendim kral! Dilerim her zaman benden hoşnut kalırsın” dedi.
5 Yayinda Sarki Dawuda ya kusato Bahurim, sai ga wani mutumin dangin Shawulu ya fito daga can, sunansa Shimeyi ɗan Gera. Ya fito yana ta la’anta yayinda yake fitowa.
Kral Davut Bahurim'e vardığında, Saul ailesinin geldiği boydan Gera oğlu Şimi adında biri lanetler okuyarak ortaya çıktı.
6 Ya jajjefi Dawuda da dukan fadawan sarki da duwatsu, ko da yake sojoji da masu gadin sarki na musamman suna kewaye da sarki dama da hagu.
Bütün askerler ve koruyucular Kral Davut'un sağında, solunda olmasına karşın, Şimi Davut'la askerlerini taşlıyordu.
7 Yayinda yake la’antar, Shimeyi ya ce, “Tafi daga nan, tafi daga nan, mai kisankai, mutumin banza kawai!
Şimi lanetler okuyarak, “Çekil git, ey eli kanlı, alçak adam!” diyordu,
8 Ubangiji ya kama ka saboda alhakin jinin gidan Shawulu, wanda kake sarauta a maimakonsa. Ubangiji ya ba da masarautar ga ɗanka Absalom. Hallaka ta zo maka domin kai mai kisankai ne!”
“RAB, yerine kral olduğun Saul ailesinin dökülen kanlarının karşılığını sana verdi. RAB krallığı oğlun Avşalom'a verdi. Sen eli kanlı bir adam olduğun için bu yıkıma uğradın!”
9 Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce wa sarki, “Ranka yă daɗe, don me wannan mataccen kare yake la’antarka? Bari in je in datse kansa.”
Seruya oğlu Avişay krala, “Bu ölü köpek neden efendim krala lanet okusun?” dedi, “İzin ver de gidip başını uçurayım.”
10 Amma sarki ya ce, “Ba ruwana da ku, ku’ya’yan Zeruhiya. Idan yana la’ana ne domin Ubangiji ya ce masa, ‘La’anci Dawuda,’ wa zai ce, ‘Don me kake haka?’”
Ama kral, “Bu sizin işiniz değil, ey Seruya oğulları!” dedi, “RAB ona, ‘Davut'a lanet oku’ dediği için lanet okuyorsa, kim, ‘Bunu neden yapıyorsun’ diye sorabilir?”
11 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Abishai da dukan fadawansa, “Ɗana, na cikina, yana ƙoƙari yă kashe ni. Balle wannan mutumin Benyamin! Ku ƙyale shi, yă yi ta zargi, Ubangiji ne ya ce masa yă yi haka.
Sonra Davut Avişay'la askerlerine, “Öz oğlum beni öldürmeye çalışırken, şu Benyaminli'nin yaptığına şaşmamalı” dedi, “Bırakın onu, lanet okusun, çünkü ona böyle yapmasını RAB buyurmuştur.
12 Mai yiwuwa Ubangiji yă ga azabata, yă sāka mini da alheri saboda la’anar da nake sha a yau.”
Belki RAB sıkıntımı görür de, bugün okunan lanetlerin karşılığını iyilikle verir.”
13 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka ci gaba da tafiyarsu yayinda Shimeyi yana tafiya ɗaura da shi a gefen tudu, yana zagi, yana jifansa da duwatsu, yana tayar masa da ƙura.
Davut'la adamları yollarına devam ettiler. Davut'un karşısında, dağın yamacında yürüyen Şimi, giderken ona lanet okuyor, taş, toprak atıyordu.
14 Sarki da dukan mutanen da suke tare da shi suka isa masauƙinsu a gajiye. A can fa ya huta.
Gidecekleri yere yorgun argın varan kralla yanındaki halk orada dinlendiler.
15 Ana cikin haka, Absalom da dukan Isra’ila suka iso Urushalima, Ahitofel kuwa yana tare da shi.
Avşalom'la İsrail halkı Yeruşalim'e girmişlerdi. Ahitofel de Avşalom'la birlikteydi.
16 Sai Hushai mutumin Arkitawa, abokin Dawuda ya je wurin Absalom ya ce masa, “Ran sarki yă daɗe! Ran sarki yă daɗe!”
Davut'un dostu Arklı Huşay, Avşalom'un yanına varınca, “Yaşasın kral! Yaşasın kral!” diye bağırdı.
17 Absalom ya ce wa Hushai, “Ƙaunar da kake nuna wa abokinka ke nan? Me ya sa ba ka tafi tare da abokinka ba?”
Avşalom Huşay'a, “Dostuna bağlılığın bu mu? Neden dostunla gitmedin?” diye sordu.
18 Hushai ya ce wa Absalom, “A’a, ai, wanda Ubangiji ya zaɓa ta wurin waɗannan mutane, da kuma ta wurin dukan mutane Isra’ila, shi zan zama nasa, zan kuma kasance tare da shi.
Huşay, “Hayır” diye yanıtladı, “Ben RAB'bin, bu halkın ve bütün İsrailliler'in seçtiği kişiden yana olacağım, onun yanında kalacağım.
19 Ban da haka ma, wane ne zan bauta wa? Ashe, ba ɗan ne zan bauta wa ba? Kamar dai yadda na bauta wa mahaifinka, haka zan bauta maka.”
Üstelik Davut oğlu Avşalom'dan başka kime hizmet edeceğim? Babana nasıl hizmet ettiysem, sana da öyle hizmet edeceğim.”
20 Absalom ya ce wa Ahitofel, “Ba mu shawararka. Me za mu yi?”
Avşalom Ahitofel'e, “Ne yapmalıyız, bize öğüt ver” dedi.
21 Ahitofel ya ce wa Absalom, “Je ka kwana da ƙwarƙwaran mahaifinka waɗanda ya bari su lura da fada. Ta haka dukan Isra’ila za su ji cewa ka mai da kanka abin wari a hancin mahaifinka, dukan hannuwan waɗanda suke tare da kai kuwa za su sami ƙarfi.”
Ahitofel, “Babanın saraya bakmak için bıraktığı cariyelerle yat” diye karşılık verdi, “Böylece bütün İsrail babanın nefretini kazandığını duyacak ve seni destekleyenlerin tümü kendilerini daha da güçlenmiş bulacaklar.”
22 Saboda haka suka kafa wa Absalom tenti a bisa rufin ɗaki, a can ya kwana da ƙwarƙwaran mahaifinsa a gaban dukan Isra’ila.
Sarayın damında Avşalom için bir çadır kurdular. Avşalom bütün İsrailliler'in gözü önünde babasının cariyelerinin yanına girdi.
23 To, a kwanakin nan shawarar da Ahitofel yakan bayar takan zama kamar wadda aka nemi daga Allah ne. Haka Dawuda da Absalom duk suke ɗaukan dukan shawarar Ahitofel.
O günlerde Ahitofel'in verdiği öğüt, Tanrı sözünü ileten bir adamınki gibiydi. Davut da, Avşalom da onun öğüdünü öyle kabul ederlerdi.

< 2 Sama’ila 16 >