< 2 Sama’ila 16 >

1 Sa’ad da Dawuda ya yi ɗan nesa da ƙwanƙolin, sai ga Ziba mai hidimar Mefiboshet, yana jira yă tarye shi. Yana da jerin jakuna da sirdi suna ɗauke da dunƙulen burodi ɗari biyu, da ƙosai busasshen inabi ɗari ɗaya, da kosan’ya’yan itace ɓaure guda ɗari, da salka ruwan inabi.
Or, lorsque David eut dépassé un peu le haut de la montagne, parut à sa rencontre Siba, serviteur de Miphiboseth, avec deux ânes, qui étaient chargés de deux cents pains, et de cent grappes de raisins secs, et de cent panerées de figues sèches, et d’une outre de vin.
2 Sarki ya ce wa Ziba, “Me ya sa ka kawo waɗannan?” Ziba ya ce, “Jakuna domin iyalin gidan sarki su hau ne, burodi da’ya’yan itace domin mutane su ci, ruwan inabi kuma domin waɗanda suka gaji a hamada.”
Et le roi dit à Siba: Que veut dire cela? Et Siba répondit: Les ânes sont pour les serviteurs du roi, afin qu’ils y montent; les pains et les figues pour nourrir vos serviteurs; mais le vin, pour boire, si quelqu’un tombe en défaillance dans le désert.
3 Sai sarki ya ce, “Ina jikar maigidanka?” Ziba ya ce, “Yana zaune a Urushalima gama yana tsammani cewa, ‘Yau gidan Isra’ila za su mayar mini da sarautar kakana.’”
Et le roi reprit: Où est le fils de ton seigneur? Et Siba répondit au roi: Il est demeuré à Jérusalem, disant: Aujourd’hui la maison d’Israël me rendra le royaume de mon père.
4 Sai sarki ya ce wa Ziba, “Duk abin da yake na Mefiboshet, ya zama naka.” Ziba ya rusuna ya ce, “Bari in dinga samun tagomashi a gabanka ranka yă daɗe.”
Le roi dit encore à Siba: Tout ce qui était à Miphiboseth est à toi. Et Siba répondit: Je prie, que je trouve grâce devant vous, mon seigneur le roi.
5 Yayinda Sarki Dawuda ya kusato Bahurim, sai ga wani mutumin dangin Shawulu ya fito daga can, sunansa Shimeyi ɗan Gera. Ya fito yana ta la’anta yayinda yake fitowa.
Le roi David vint donc jusqu’à Bahurim; et voilà qu’en sortait un homme de la parenté de la maison de Saül, du nom de Séméi, fils de Géra; et sortant, il s’avançait maudissant,
6 Ya jajjefi Dawuda da dukan fadawan sarki da duwatsu, ko da yake sojoji da masu gadin sarki na musamman suna kewaye da sarki dama da hagu.
Et il jetait des pierres contre David et contre tous les serviteurs du roi David: or, tout le peuple et tous les combattants marchaient à droite et à gauche à côté du roi.
7 Yayinda yake la’antar, Shimeyi ya ce, “Tafi daga nan, tafi daga nan, mai kisankai, mutumin banza kawai!
Et Séméi parlait ainsi lorsqu’il maudissait le roi: Sors, sors, homme de sang et homme de Bélial.
8 Ubangiji ya kama ka saboda alhakin jinin gidan Shawulu, wanda kake sarauta a maimakonsa. Ubangiji ya ba da masarautar ga ɗanka Absalom. Hallaka ta zo maka domin kai mai kisankai ne!”
Le Seigneur t’a rendu tout le sang de la maison de Saül, parce que tu t’es emparé du royaume en sa place; et le Seigneur a mis le royaume en la main d’Absalom ton fils; et voilà que t’accablent tes propres maux, parce que tu es un homme de sang.
9 Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce wa sarki, “Ranka yă daɗe, don me wannan mataccen kare yake la’antarka? Bari in je in datse kansa.”
Alors Abisaï, fils de Sarvia, dit au roi: Pourquoi ce chien mort maudit-il mon seigneurie roi? J’irai, et lui couperai la tête.
10 Amma sarki ya ce, “Ba ruwana da ku, ku’ya’yan Zeruhiya. Idan yana la’ana ne domin Ubangiji ya ce masa, ‘La’anci Dawuda,’ wa zai ce, ‘Don me kake haka?’”
Et le roi répondit: Qu’importe à moi et à vous, fils de Sarvia? Laissez-le maudire; car le Seigneur lui a ordonné qu’il maudisse David. Et quel est celui qui osera dire: Pourquoi a-t-il fait ainsi?
11 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Abishai da dukan fadawansa, “Ɗana, na cikina, yana ƙoƙari yă kashe ni. Balle wannan mutumin Benyamin! Ku ƙyale shi, yă yi ta zargi, Ubangiji ne ya ce masa yă yi haka.
Et le roi dit à Abisaï et à tous ses serviteurs: Voilà que mon fils, qui est sorti de mes entrailles, cherche mon âme; combien plus maintenant un fils de Jémini! Laissez-le, qu’il maudisse selon l’ordre du Seigneur;
12 Mai yiwuwa Ubangiji yă ga azabata, yă sāka mini da alheri saboda la’anar da nake sha a yau.”
Peut-être que le Seigneur regardera mon affliction, et que le Seigneur me rendra quelque bien pour cette malédiction d’aujourd’hui.
13 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka ci gaba da tafiyarsu yayinda Shimeyi yana tafiya ɗaura da shi a gefen tudu, yana zagi, yana jifansa da duwatsu, yana tayar masa da ƙura.
C’est pourquoi David allait par son chemin et ses gens avec lui; mais Séméi marchait du même côté, sur la crête de la montagne, maudissant, lançant des pierres contre lui, et répandant de la poussière en l’air.
14 Sarki da dukan mutanen da suke tare da shi suka isa masauƙinsu a gajiye. A can fa ya huta.
Et ainsi le roi vint, et tout le peuple avec lui, accablé de lassitude, et ils reprirent là des forces.
15 Ana cikin haka, Absalom da dukan Isra’ila suka iso Urushalima, Ahitofel kuwa yana tare da shi.
Cependant Absalom et tout son peuple entrèrent à Jérusalem, et Achitophel aussi avec lui.
16 Sai Hushai mutumin Arkitawa, abokin Dawuda ya je wurin Absalom ya ce masa, “Ran sarki yă daɗe! Ran sarki yă daɗe!”
Or, lorsque Chusaï, l’Arachite, ami de David, fut venu vers Absalom, il lui dit: Je vous salue, ô roi; je vous salue, ô roi.
17 Absalom ya ce wa Hushai, “Ƙaunar da kake nuna wa abokinka ke nan? Me ya sa ba ka tafi tare da abokinka ba?”
Et Absalom: Est-ce là, lui dit-il, ta reconnaissance envers ton ami? pourquoi n’es-tu pas allé avec ton ami?
18 Hushai ya ce wa Absalom, “A’a, ai, wanda Ubangiji ya zaɓa ta wurin waɗannan mutane, da kuma ta wurin dukan mutane Isra’ila, shi zan zama nasa, zan kuma kasance tare da shi.
Et Chusaï répondit à Absalom: Point du tout, parce que je serai à celui que le Seigneur a élu, ainsi que tout ce peuple, et tous ceux d’Israël, et c’est avec lui que je demeurerai.
19 Ban da haka ma, wane ne zan bauta wa? Ashe, ba ɗan ne zan bauta wa ba? Kamar dai yadda na bauta wa mahaifinka, haka zan bauta maka.”
Mais pour ajouter encore ceci: Qui vais-je servir? N’est-ce pas le fils du roi? Comme j’ai obéi à votre père, ainsi je vous obéirai.
20 Absalom ya ce wa Ahitofel, “Ba mu shawararka. Me za mu yi?”
Or Absalom dit à Achitophel: Délibérez sur ce que nous devons faire.
21 Ahitofel ya ce wa Absalom, “Je ka kwana da ƙwarƙwaran mahaifinka waɗanda ya bari su lura da fada. Ta haka dukan Isra’ila za su ji cewa ka mai da kanka abin wari a hancin mahaifinka, dukan hannuwan waɗanda suke tare da kai kuwa za su sami ƙarfi.”
Et Achitophel dit à Absalom: Approchez-vous des femmes de votre père, qu’il a laissées pour garder la maison, afin que, lorsque tout Israël aura ouï que vous avez déshonoré votre père, leurs mains se fortifient avec vous.
22 Saboda haka suka kafa wa Absalom tenti a bisa rufin ɗaki, a can ya kwana da ƙwarƙwaran mahaifinsa a gaban dukan Isra’ila.
Ils dressèrent donc une tente pour Absalom sur la terrasse, et il s’approcha des femmes de son père devant tout Israël.
23 To, a kwanakin nan shawarar da Ahitofel yakan bayar takan zama kamar wadda aka nemi daga Allah ne. Haka Dawuda da Absalom duk suke ɗaukan dukan shawarar Ahitofel.
Et les conseils qu’Achitophel donnait en ces jours-là, étaient comme si quelqu’un consultait Dieu. Tel était tout conseil d’Achitophel, et lorsqu’il était avec David, et lorsqu’il était avec Absalom.

< 2 Sama’ila 16 >