< 2 Sama’ila 16 >

1 Sa’ad da Dawuda ya yi ɗan nesa da ƙwanƙolin, sai ga Ziba mai hidimar Mefiboshet, yana jira yă tarye shi. Yana da jerin jakuna da sirdi suna ɗauke da dunƙulen burodi ɗari biyu, da ƙosai busasshen inabi ɗari ɗaya, da kosan’ya’yan itace ɓaure guda ɗari, da salka ruwan inabi.
David avait à peine dépassé le sommet qu’il rencontra Ciba, serviteur de Mephiboseth, qui conduisait une paire d’ânes sanglés, portant deux cents pains, cent gâteaux de raisins secs, cent gâteaux de figues et une outre de vin.
2 Sarki ya ce wa Ziba, “Me ya sa ka kawo waɗannan?” Ziba ya ce, “Jakuna domin iyalin gidan sarki su hau ne, burodi da’ya’yan itace domin mutane su ci, ruwan inabi kuma domin waɗanda suka gaji a hamada.”
Le roi dit à Ciba: "Que fais-tu de ces objets?" Ciba répondit: "Les ânes sont destinés, comme montures, à la maison du roi, le pain et les fruits secs à la nourriture des serviteurs, et le vin pour désaltérer ceux qu’a fatigués la marche au désert."
3 Sai sarki ya ce, “Ina jikar maigidanka?” Ziba ya ce, “Yana zaune a Urushalima gama yana tsammani cewa, ‘Yau gidan Isra’ila za su mayar mini da sarautar kakana.’”
Le roi reprit: "Et où est le fils de ton maître?" Ciba répondit: "Il se tient à Jérusalem, parce que, a-t-il dit, maintenant la maison d’Israël va me rendre la royauté de mon père."
4 Sai sarki ya ce wa Ziba, “Duk abin da yake na Mefiboshet, ya zama naka.” Ziba ya rusuna ya ce, “Bari in dinga samun tagomashi a gabanka ranka yă daɗe.”
Le roi dit à Ciba: "Tous les biens de Mephiboseth sont maintenant pour toi." Et Ciba dit: "Je me prosterne devant toi, mon royal maître, et puissé-je conserver ta faveur!"
5 Yayinda Sarki Dawuda ya kusato Bahurim, sai ga wani mutumin dangin Shawulu ya fito daga can, sunansa Shimeyi ɗan Gera. Ya fito yana ta la’anta yayinda yake fitowa.
Le roi David venait d’atteindre Bahourim lorsqu’il en vit sortir un homme de la famille de Saül, nommé Séméi, fils de Ghêra, qui, tout en s’avançant, l’accablait d’injures,
6 Ya jajjefi Dawuda da dukan fadawan sarki da duwatsu, ko da yake sojoji da masu gadin sarki na musamman suna kewaye da sarki dama da hagu.
lançait des pierres à David et à tous ses serviteurs, à toute la foule et à tous les guerriers qui l’entouraient à droite et à gauche.
7 Yayinda yake la’antar, Shimeyi ya ce, “Tafi daga nan, tafi daga nan, mai kisankai, mutumin banza kawai!
Et Séméi s’exprimait ainsi dans ses imprécations: "Va-t’en, va-t’en, homme de sang, homme indigne!
8 Ubangiji ya kama ka saboda alhakin jinin gidan Shawulu, wanda kake sarauta a maimakonsa. Ubangiji ya ba da masarautar ga ɗanka Absalom. Hallaka ta zo maka domin kai mai kisankai ne!”
Le Seigneur a fait retomber sur toi tout le sang de la maison de Saül dont tu occupes le trône, et a fait passer la royauté aux mains de ton fils Absalon. Te voilà puni de ta méchanceté, homme de sang que tu es!"
9 Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce wa sarki, “Ranka yă daɗe, don me wannan mataccen kare yake la’antarka? Bari in je in datse kansa.”
Abisaï, fils de Cerouya, dit au roi: "Pourquoi laisse-t-on ce chien mort insulter le roi mon maître? Permets-moi d’avancer et de lui trancher la tête."
10 Amma sarki ya ce, “Ba ruwana da ku, ku’ya’yan Zeruhiya. Idan yana la’ana ne domin Ubangiji ya ce masa, ‘La’anci Dawuda,’ wa zai ce, ‘Don me kake haka?’”
Le roi répondit: "Qu’ai-je affaire de vous, enfants de Cerouya? S’Il insulte ainsi, c’est que Dieu lui aura inspiré d’insulter David; qui lui demandera compte de sa conduite?"
11 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Abishai da dukan fadawansa, “Ɗana, na cikina, yana ƙoƙari yă kashe ni. Balle wannan mutumin Benyamin! Ku ƙyale shi, yă yi ta zargi, Ubangiji ne ya ce masa yă yi haka.
Puis il dit à Abïsaï et à tous ses serviteurs: "Si mon propre fils, sorti de mes entrailles, en veut à ma vie, qu’attendre de ce Benjamite? Laissez-le prodiguer l’injure, si Dieu le lui a dit!
12 Mai yiwuwa Ubangiji yă ga azabata, yă sāka mini da alheri saboda la’anar da nake sha a yau.”
Peut-être le Seigneur considérera-t-il ma situation et me rendra-t-il du bonheur en échange des outrages que je subis en ce jour."
13 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka ci gaba da tafiyarsu yayinda Shimeyi yana tafiya ɗaura da shi a gefen tudu, yana zagi, yana jifansa da duwatsu, yana tayar masa da ƙura.
David, avec ses gens, poursuivit sa route. Cependant Séméi suivait du même pas le flanc de la montagne, continuant à l’insulter, lançant des pierres et faisant voler de la poussière dans sa direction.
14 Sarki da dukan mutanen da suke tare da shi suka isa masauƙinsu a gajiye. A can fa ya huta.
Le roi avec toute sa suite, tous fatigués, arriva, et l’on s’y reposa.
15 Ana cikin haka, Absalom da dukan Isra’ila suka iso Urushalima, Ahitofel kuwa yana tare da shi.
Or, Absalon, suivi de tout le peuple israélite, était entré dans Jérusalem, et Ahitofel avec lui.
16 Sai Hushai mutumin Arkitawa, abokin Dawuda ya je wurin Absalom ya ce masa, “Ran sarki yă daɗe! Ran sarki yă daɗe!”
Lorsque Houchaï l’Arkéen, ami de David, arriva auprès d’Absalon, il s’écria devant lui: "Vive le roi! Vive le roi!"
17 Absalom ya ce wa Hushai, “Ƙaunar da kake nuna wa abokinka ke nan? Me ya sa ba ka tafi tare da abokinka ba?”
Absalon lui dit: "C’Est là ton dévouement pour ton ami? Pourquoi n’as-tu pas suivi ton ami?"
18 Hushai ya ce wa Absalom, “A’a, ai, wanda Ubangiji ya zaɓa ta wurin waɗannan mutane, da kuma ta wurin dukan mutane Isra’ila, shi zan zama nasa, zan kuma kasance tare da shi.
Houchaï répondit à Absalon: "Point du tout; celui qui a été adopté par l’Eternel et par ce peuple, par tous les Israélites, c’est à lui que j’appartiens, c’est avec lui que je demeure.
19 Ban da haka ma, wane ne zan bauta wa? Ashe, ba ɗan ne zan bauta wa ba? Kamar dai yadda na bauta wa mahaifinka, haka zan bauta maka.”
En second lieu, qui vais-je servir? N’Est-ce pas le fils de David? Comme j’ai servi ton père, ainsi serai-je à ton égard."
20 Absalom ya ce wa Ahitofel, “Ba mu shawararka. Me za mu yi?”
Absalon dit à Ahitofel: "Délibérez entre vous sur ce que nous avons à faire."
21 Ahitofel ya ce wa Absalom, “Je ka kwana da ƙwarƙwaran mahaifinka waɗanda ya bari su lura da fada. Ta haka dukan Isra’ila za su ji cewa ka mai da kanka abin wari a hancin mahaifinka, dukan hannuwan waɗanda suke tare da kai kuwa za su sami ƙarfi.”
Ahitofel répondit à Absalon: "Aie commerce avec les concubines de ton père, laissées par lui pour garder sa demeure; tout Israël saura que tu t’es rendu odieux à ton père, et tous ceux qui sont avec toi en seront plus résolus."
22 Saboda haka suka kafa wa Absalom tenti a bisa rufin ɗaki, a can ya kwana da ƙwarƙwaran mahaifinsa a gaban dukan Isra’ila.
On dressa donc pour Absalon une tente sur la terrasse, et il eut commerce avec les concubines de son père à la vue de tout Israël.
23 To, a kwanakin nan shawarar da Ahitofel yakan bayar takan zama kamar wadda aka nemi daga Allah ne. Haka Dawuda da Absalom duk suke ɗaukan dukan shawarar Ahitofel.
Les avis que donnait Ahitofel en ce temps-là étaient respectés comme la parole de Dieu même; il en était ainsi de tous ses avis et pour David et pour Absalon.

< 2 Sama’ila 16 >