< 2 Sama’ila 15 >

1 Ana nan sai Absalom ya samo wa kansa wata keken yaƙi da dawakai tare da mutum hamsin da za su sha gabansa.
Kwasekusithi emva kwalokhu uAbisalomu wazilungisela izinqola lamabhiza, labantu abangamatshumi amahlanu begijima phambi kwakhe.
2 Absalom yakan tashi da sassafe yă tsaya a gefen hanyar shigar ƙofar birni. Duk sa’ad da wani ya zo da ƙara don a kai gaban sarki yă yi shari’a, Absalom yakan kira shi yă ce, “Daga wane gari ka fito?” Sai mutumin yă amsa yă ce, “Bawanka ya fito a ɗaya daga cikin kabilan Isra’ila.”
UAbisalomu wayesevuka ekuseni kakhulu eme eceleni kwendlela yesango; kwakusithi wonke umuntu olecala lomthetho eliya enkosini ukwahlulelwa, uAbisalomu ambize athi: Ungowawuphi umuzi? Lapho esithi: Inceku yakho ingowesinye sezizwe zakoIsrayeli;
3 Sai Absalom yă ce masa, “Ga shi, ƙararka daidai ne, tana kuma da gaskiya, sai dai ba wakilin sarkin da zai ji ka.”
uAbisalomu abesesithi kuye: Bona, indaba zakho zinhle zilungile, kodwa kakho owenkosi ukuthi akuzwe.
4 Absalom kuwa yakan ƙara da cewa, “Da a ce an naɗa ni alƙali a ƙasar mana! Da duk mai ƙara, ko kuka wanda zai zo wurina, zan in tabbatar an yi masa adalci.”
UAbisalomu abesesithi: Kungathi ngabe ngibekwe umahluleli elizweni, ukuthi wonke umuntu olecala lomthetho lodaba angeza kimi, njalo bengizamlungisela.
5 Kuma duk sa’ad da wani ya zo wurin Absalom ya rusuna don yă gaishe shi, sai Absalom yă sa hannunsa yă ta da shi, yă kuma rungume shi.
Kwakusithi lapho kusondela umuntu ukumkhothamela, elule isandla sakhe, ambambe, amange.
6 Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
UAbisalomu wasesenza ngalindlela kuIsrayeli wonke, bona abeza enkosini ukwahlulelwa; ngalokho uAbisalomu wathumba inhliziyo yamadoda akoIsrayeli.
7 A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
Kwasekusithi ekupheleni kweminyaka engamatshumi amane uAbisalomu wathi enkosini: Ake ngiyekhokha isithembiso sami engasithembisa eNkosini eHebroni.
8 Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’”
Ngoba inceku yakho yathembisa isithembiso ngisahlala eGeshuri eSiriya ngisithi: Uba iNkosi ingibuyisela lokungibuyisela eJerusalema, ngizayikhonza iNkosi.
9 Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
Inkosi yasisithi kuye: Hamba ngokuthula. Wasesukuma waya eHebroni.
10 Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’”
Kodwa uAbisalomu wathuma izinhloli ezizweni zonke zakoIsrayeli esithi: Lapho lisizwa ukukhala kophondo, lizakuthi: UAbisalomu uyinkosi eHebroni!
11 Mutum ɗari biyu daga Urushalima suka raka Absalom. An gayyace su a matsayin baƙi, suka kuwa tafi cikin rashin sani, ba su san wani abu game da al’amarin ba.
Kwasekuhamba loAbisalomu amadoda angamakhulu amabili esuka eJerusalema, anxusiweyo, ahamba ebuqothweni bawo, njalo engazi lutho.
12 Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
UAbisalomu wasethumela wabiza uAhithofeli weGilo, umeluleki kaDavida, esuka emzini wakhe, eGilo, esahlaba imihlatshelo. Njalo ugobe lwaqina, labantu bahamba banda kuAbisalomu.
13 Wani manzo ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra’ila sun koma wajen Absalom.”
Kwasekufika isithunywa kuDavida, sisithi: Inhliziyo yabantu bakoIsrayeli ilandela uAbisalomu.
14 Sai Dawuda ya ce wa dukan fadawansa da suke tare da shi a Urushalima, “Ku zo! Mu gudu, in ba haka ba, babu wanda zai tsira daga hannun Absalom. Dole mu bar nan, nan da nan, in ba haka ba zai tashi da sauri yă fāɗa mana, yă kuma hallaka garin da takobi.”
Wasesithi uDavida ezincekwini zakhe zonke ezazilaye eJerusalema: Sukumani, sibaleke, ngoba kasilakuphepha ebusweni bukaAbisalomu. Phangisani ukuhamba, hlezi aphangise asifice, asehlisele okubi, atshaye umuzi ngobukhali benkemba.
15 Sai fadawan sarki suka ce masa, “Barorinka suna a shirye su yi duk abin da ranka yă daɗe, ya zaɓa.”
Izinceku zenkosi zasezisithi enkosini: Njengakho konke inkosi, inkosi yami, ekukhethayo, khangela, nanzi inceku zakho.
16 Sarki ya kama hanya, dukan gidansa kuwa suna biye da shi; amma ya bar ƙwarƙwarai goma su lura da fada.
Yasiphuma inkosi, layo yonke indlu yayo iyilandela. Inkosi yasitshiya abafazi abalitshumi, abafazi abancane, ukuze balinde indlu.
17 Ta haka sarki ya kama hanya da dukan mutane suna biye da shi, suka yi sansani a wani wuri mai ɗan nisa da Urushalima.
Yasiphuma inkosi, labo bonke abantu beyilandela; bema endlini ekhatshana.
18 Dukan mutanensa suka wuce gabansa, tare da dukan Keretawa da Feletiyawa; da dukan mutane ɗari shida na Gittiyawan da suka raka shi daga Gat, suka wuce gaban sarki.
Lazo zonke inceku zayo zedlula eceleni kwayo, njalo wonke amaKerethi lawo wonke amaPelethi lawo wonke amaGiti, amadoda angamakhulu ayisithupha, eza amlandela evela eGati, edlula phambi kwenkosi.
19 Sarki ya ce wa Ittai mutumin Gat, “Don me za ka zo tare da mu? Ka koma ka zauna tare da Sarki Absalom. Kai baƙo ne, ɗan gudun hijira daga garinka.
Inkosi yasisithi kuIthayi umGiti: Lawe uhambelani lathi? Buyela uhlale lenkosi, ngoba ungowezizweni njalo ungumxotshwa endaweni yakho.
20 Jiya-jiya ka zo. Yau kuma in sa ka yi ta yawo tare da mu, ga shi ban ma san inda za ni ba? Koma, ka tafi da’yan’uwanka. Bari alheri da amincin Ubangiji su kasance tare da kai.”
Ufike izolo; pho, lamuhla ngikuzulazulise ngokuhamba lathi, njengoba ngiya lapho engiya khona? Buyela ubuyisele abafowenu. Umusa leqiniso kakube lawe.
21 Amma Ittai ya ce wa sarki, “Muddin Ubangiji yana a raye kuma muddin ranka yă daɗe yana a raye, duk inda ranka yă daɗe sarki zai kasance, ko a yi rai ko a mutu, a can bawanka zai kasance.”
Kodwa uIthayi wayiphendula inkosi wathi: Kuphila kukaJehova, njalo kuphila kwenkosi yami, inkosi, isibili kuleyondawo lapho inkosi yami, inkosi, ezakuba kiyo, loba kusekufeni loba kusekuphileni, lalapho izakuba khona inceku yakho.
22 Dawuda ya ce wa Ittai, “Wuce gaba, taka mu je.” Sai Ittai mutumin Gat ya shiga layi tare da dukan mutanensa da iyalan da suke tare da shi.
UDavida wasesithi kuIthayi: Hamba, uchaphe. UIthayi umGiti wasechapha kanye labantu bakhe bonke labantwanyana ababelaye.
23 Dukan ƙauyuka suka yi ta kururuwa yayinda mutanen suke wucewa. Sarki shi ma ya haye ta Kwarin Kidron, mutane kuma suka ci gaba da tafiya zuwa wajen hamada.
Ilizwe lonke lakhala inyembezi ngelizwi elikhulu, njalo abantu bonke bachapha. Inkosi yasichapha isifula iKidroni, labantu bonke bachapha, ngasendleleni yenkangala.
24 Zadok yana nan tare da su, kuma dukan Lawiyawan da suke tare da shi kuwa suna ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka sauke akwatin alkawarin Allah, Abiyatar ya miƙa hadaya sai da mutane suka gama fita daga birnin.
Njalo khangela, uZadoki laye lawo wonke amaLevi elaye, bethwele umtshokotsho wesivumelwano sikaNkulunkulu, bawubeka phansi umtshokotsho kaNkulunkulu; uAbhiyatha wasesenyuka, abantu bonke baze baphela ukudlula bephuma emzini.
25 Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
Inkosi yasisithi kuZadoki: Buyisela umtshokotsho kaNkulunkulu emzini. Uba ngizathola umusa emehlweni eNkosi, izangibuyisa ingitshengise wona kanye lendawo yayo yokuhlala.
26 Amma in ya ce, ‘Ina baƙin ciki da kai,’ to, ina a shirye; bari yă yi abin da ya fi masa.”
Kodwa uba isitsho njalo, ithi: Kangithokozi ngawe; khangela ngilapha, kayenze kimi njengokuhle emehlweni ayo.
27 Sarki ya kuma ce wa Zadok firist, “Ashe, kai ba mai duba ba ne? Ka koma cikin birnin lafiya, tare da ɗanka Ahimawaz, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar. Kai da Abiyatar ku tafi da’ya’yanku biyu.
Inkosi yasisithi kuZadoki umpristi: Ungumboni yini? Buyela emzini ngokuthula, loAhimahazi indodana yakho loJonathani indodana kaAbhiyatha, amadodana enu womabili elani.
28 Zan kuwa jira a mashigai a hamada, sai na ji daga gare ku.”
Bona, ngizalinda emazibukweni enkangala, kuze kufike ilizwi elivela kini lokungibikela.
29 Saboda haka Zadok da Abiyatar suka ɗauki akwatin alkawarin Allah suka komar da shi Urushalima, suka zauna a can.
Ngakho uZadoki loAbhiyatha bawubuyisela umtshokotsho kaNkulunkulu eJerusalema, bahlala khona.
30 Amma Dawuda ya ci gaba yana hawan Dutsen Zaitun, yana kuka yayinda yake tafiya; kansa a rufe, kuma babu takalma a ƙafafunsa. Dukan mutanen da suke tare da shi suka rufe kawunansu suna ta kuka yayinda suke haurawa.
UDavida wasesenyuka ngomqanso wemihlwathi, esenyuka ekhala inyembezi, embomboze ikhanda lakhe, wahamba engelamanyathela; labo bonke abantu ababelaye bambomboza, ngulowo lalowo ikhanda lakhe, benyuka, besenyuka bekhala inyembezi.
31 To, an gaya wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin waɗanda suka hadasa maƙarƙashiya tare da Absalom.” Saboda haka Dawuda ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji ka mai da shawarar Ahitofel ta zama shiririta.”
Kwasekubikwa kuDavida kwathiwa: UAhithofeli uphakathi kwabakugobe loAbisalomu. UDavida wasesithi: Nkosi, ake enze icebo likaAhithofeli libe yibuthutha.
32 Da Dawuda ya isa ƙwanƙoli, inda mutane sun saba yi wa Allah sujada, Hushai, mutumin Arkitawa kuwa yana can don yă tarye shi, taguwarsa a yage, ga kuma ƙura a kansa.
Kwasekusithi uDavida esefike engqongeni lapho ayekhonza khona uNkulunkulu, khangela, uHushayi umArki wamhlangabeza, isembatho sakhe sidatshuliwe, lenhlabathi isekhanda lakhe.
33 Sai Dawuda ya ce masa, “In ka tafi tare da ni, za ka zama mini kaya.
UDavida wasesithi kuye: Uba usedlula lami, uzakuba ngumthwalo kimi.
34 Amma in ka koma birni, ka gaya wa Absalom, ‘Zan zama bawanka, ya sarki; dā ni bawan mahaifinka ne, amma yanzu zan zama bawanka,’ ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel.
Kodwa uba ubuyela emzini uthi kuAbisalomu: Ngizakuba yinceku yakho, nkosi; kade ngiyinceku kayihlo, kodwa khathesi sengizakuba yinceku yakho; khona uzangichithela icebo likaAhithofeli.
35 Ba Zadok da Abiyatar firistocin nan suna nan tare da kai ba? Ka gaya musu duk abin da ka ji a fadan sarki.
Njalo kabakho yini kanye lawe lapho oZadoki loAbhiyatha abapristi? Ngakho kuzakuthi yonke indaba oyizwayo endlini yenkosi, uyitshele oZadoki loAbhiyatha abapristi.
36 ’Ya’yansu biyu maza, Ahimawaz ɗan Zadok, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar, suna can tare da su. Ka aike su wurina da duk abin da ka ji.”
Khangela, kukhona lapho kanye labo amadodana abo amabili, uAhimahazi okaZadoki, loJonathani okaAbhiyatha; njalo uzathumela ngesandla sabo kimi yonke into ozayizwa.
37 Saboda haka Hushai abokin Dawuda ya isa Urushalima yayinda Absalom yake shigowa birnin.
UHushayi umngane kaDavida wasefika emzini, loAbisalomu wafika eJerusalema.

< 2 Sama’ila 15 >