< 2 Sama’ila 15 >

1 Ana nan sai Absalom ya samo wa kansa wata keken yaƙi da dawakai tare da mutum hamsin da za su sha gabansa.
Therfor aftir these thingis Absolon made a chaar to hym, and knyytis, and fifti men, that schulden go bifor hym.
2 Absalom yakan tashi da sassafe yă tsaya a gefen hanyar shigar ƙofar birni. Duk sa’ad da wani ya zo da ƙara don a kai gaban sarki yă yi shari’a, Absalom yakan kira shi yă ce, “Daga wane gari ka fito?” Sai mutumin yă amsa yă ce, “Bawanka ya fito a ɗaya daga cikin kabilan Isra’ila.”
And Absolon roos eerli, and stood bisidis the entryng of the yate in the weie; and Absolon clepide to hym ech man, that hadde a cause that he schulde come to the doom of the kyng, and Absolon seide, Of what citee art thou? Which answeride, and seide, Of o lynage of Israel Y am, thi seruaunt.
3 Sai Absalom yă ce masa, “Ga shi, ƙararka daidai ne, tana kuma da gaskiya, sai dai ba wakilin sarkin da zai ji ka.”
And Absolon answeride to hym, Thi wordis semen to me good and iust, but noon is ordeyned of the kyng to here thee. And Absolon seide, Who schal ordeyne me iuge on the lond,
4 Absalom kuwa yakan ƙara da cewa, “Da a ce an naɗa ni alƙali a ƙasar mana! Da duk mai ƙara, ko kuka wanda zai zo wurina, zan in tabbatar an yi masa adalci.”
that alle men that han cause come to me, and Y deme iustly?
5 Kuma duk sa’ad da wani ya zo wurin Absalom ya rusuna don yă gaishe shi, sai Absalom yă sa hannunsa yă ta da shi, yă kuma rungume shi.
But whanne a man cam to Absolon to greete hym, he helde forth the hond, and took, and kisside that man;
6 Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
and Absolon dide this to al Israel, that cam to doom to be herd of the kyng; and Absolon drow awei the hertis of men of Israel.
7 A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
Forsothe aftir foure yeer Absolon seide to kyng Dauid, Y schal go, and Y schal yelde my vowis, whiche Y vowide to the Lord in Ebron;
8 Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’”
for thi seruaunt vowynge vowide, whanne he was in Gessur of Sirie, and seide, If the Lord bryngith ayen me in to Jerusalem, Y schal make sacrifice to the Lord.
9 Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
And the kyng seide to hym, Go thou in pees. And Absolon roos, and yede in to Ebron.
10 Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’”
Forsothe Absolon sente aspieris in to al the lynage of Israel, and seide, Anoon as ye heren the sown of clarioun, seye ye, Absolon schal regne in Ebron.
11 Mutum ɗari biyu daga Urushalima suka raka Absalom. An gayyace su a matsayin baƙi, suka kuwa tafi cikin rashin sani, ba su san wani abu game da al’amarin ba.
Forsothe twei hundrid men clepid of Jerusalem yeden with Absolon, and yede with symple herte, and outirli thei knewen not the cause.
12 Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
Also Absolon clepide Achitofel of Gilo, the councelour of Dauid, fro his citee Gilo. And whanne he offride sacrifices a strong swerynge togidere was maad, and the puple rennynge togidere was encreessid with Absolon.
13 Wani manzo ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra’ila sun koma wajen Absalom.”
Therfor a messanger cam to Dauid, and seide, With al herte al Israel sueth Absolon.
14 Sai Dawuda ya ce wa dukan fadawansa da suke tare da shi a Urushalima, “Ku zo! Mu gudu, in ba haka ba, babu wanda zai tsira daga hannun Absalom. Dole mu bar nan, nan da nan, in ba haka ba zai tashi da sauri yă fāɗa mana, yă kuma hallaka garin da takobi.”
And Dauid seide to hise seruauntis that weren with hym in Jerusalem, Rise ye, and flee we; for noon ascaping schal be to us fro the face of Absolon; therfor haste ye to go out, lest he come, and ocupie vs, and fille on vs fallynge, and smyte the citee bi the scharpnesse of swerd.
15 Sai fadawan sarki suka ce masa, “Barorinka suna a shirye su yi duk abin da ranka yă daɗe, ya zaɓa.”
And the seruauntis of the kyng seiden to hym, We thi seruauntis schulen performe gladli alle thingis, what euer thingis oure lord the kyng schal comaunde.
16 Sarki ya kama hanya, dukan gidansa kuwa suna biye da shi; amma ya bar ƙwarƙwarai goma su lura da fada.
Therfor the kyng yede out, and al his hous, on her feet; and the king lefte ten wymmen concubyns, `that is, secundarie wyues, to kepe the hous.
17 Ta haka sarki ya kama hanya da dukan mutane suna biye da shi, suka yi sansani a wani wuri mai ɗan nisa da Urushalima.
And the king yede out, and al Israel, on her feet, and the kyng stood fer fro the hous.
18 Dukan mutanensa suka wuce gabansa, tare da dukan Keretawa da Feletiyawa; da dukan mutane ɗari shida na Gittiyawan da suka raka shi daga Gat, suka wuce gaban sarki.
And alle hise seruauntis yeden bisidis him, and the legiouns of Cerethi and of Ferethi, and alle men of Geth `strong fiyters, sixe hundrid men, that sueden him fro Geth, yeden on foote bifor the kyng.
19 Sarki ya ce wa Ittai mutumin Gat, “Don me za ka zo tare da mu? Ka koma ka zauna tare da Sarki Absalom. Kai baƙo ne, ɗan gudun hijira daga garinka.
Forsothe the kyng seide to Ethai of Geth, Whi comest thou with vs? Turne thou ayen, and dwelle with the kyng, for thou art a pilgrym, and thou yedist out fro thi place.
20 Jiya-jiya ka zo. Yau kuma in sa ka yi ta yawo tare da mu, ga shi ban ma san inda za ni ba? Koma, ka tafi da’yan’uwanka. Bari alheri da amincin Ubangiji su kasance tare da kai.”
Thou camest yistirdai, and to dai thou art compellid to go out with vs. Sotheli Y schal go, whidur Y schal go; turne ayen, and lede ayen thi britheren with thee, and the Lord do mercy and treuthe with thee, for thou schewidist grace and feith.
21 Amma Ittai ya ce wa sarki, “Muddin Ubangiji yana a raye kuma muddin ranka yă daɗe yana a raye, duk inda ranka yă daɗe sarki zai kasance, ko a yi rai ko a mutu, a can bawanka zai kasance.”
And Ethai answeride to the kyng, and seide, The Lord lyueth, and my lord the kyng lyueth, for in what euer place thou schalt be, my lord the kyng, ether in deeth ethir in lijf, there thi seruaunt schal be.
22 Dawuda ya ce wa Ittai, “Wuce gaba, taka mu je.” Sai Ittai mutumin Gat ya shiga layi tare da dukan mutanensa da iyalan da suke tare da shi.
And Dauid seide to Ethay, Come thou, and passe. And Ethai of Geth passide, and the kyng, and alle men that weren with hym, and the tother multitude.
23 Dukan ƙauyuka suka yi ta kururuwa yayinda mutanen suke wucewa. Sarki shi ma ya haye ta Kwarin Kidron, mutane kuma suka ci gaba da tafiya zuwa wajen hamada.
And alle men wepten with greet vois, and al the puple passide; and the kyng yede ouer the strond of Cedron, and al the puple yede ayens the weie of the olyue tree, that biholdith to deseert.
24 Zadok yana nan tare da su, kuma dukan Lawiyawan da suke tare da shi kuwa suna ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka sauke akwatin alkawarin Allah, Abiyatar ya miƙa hadaya sai da mutane suka gama fita daga birnin.
Forsothe and Sadoch the preest cam, and alle the dekenes with hym, and thei baren the arke of boond of pees of God, and thei diden doun the arke of God; and Abiathar stiede, til al the puple was passid that yede out of the citee.
25 Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
And the kyng seide to Sadoch, Bere ayen the arke of God in to the citee; if Y schal fynde grace in the iyen of the Lord, he schal lede me ayen, and he schal schewe to me that arke and his tabernacle.
26 Amma in ya ce, ‘Ina baƙin ciki da kai,’ to, ina a shirye; bari yă yi abin da ya fi masa.”
Sotheli if the Lord seith, Thou plesist not me; Y am redi, do he that, that is good bifor hym silf.
27 Sarki ya kuma ce wa Zadok firist, “Ashe, kai ba mai duba ba ne? Ka koma cikin birnin lafiya, tare da ɗanka Ahimawaz, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar. Kai da Abiyatar ku tafi da’ya’yanku biyu.
And the kyng seide to Sadoch, preest, A! thou seere, `that is, profete, turne ayen in to the citee, with pees; and Achymaas, thi sone, and Jonathas, the sone of Abiathar, youre twei sones, be with you.
28 Zan kuwa jira a mashigai a hamada, sai na ji daga gare ku.”
Lo! Y schal be hid in the feeldi places of deseert, til word come fro you, and schewe to me.
29 Saboda haka Zadok da Abiyatar suka ɗauki akwatin alkawarin Allah suka komar da shi Urushalima, suka zauna a can.
Therfor Sadoch and Abiathar baren ayen the arke of God in to Jerusalem, and dwelliden there.
30 Amma Dawuda ya ci gaba yana hawan Dutsen Zaitun, yana kuka yayinda yake tafiya; kansa a rufe, kuma babu takalma a ƙafafunsa. Dukan mutanen da suke tare da shi suka rufe kawunansu suna ta kuka yayinda suke haurawa.
Forsothe Dauid stiede on the hil of olyue trees, stiynge and wepynge, with the heed hilyd, and `goynge with nakid feet; but also al the puple that was with hym, stiede with the heed hilid, and wepte.
31 To, an gaya wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin waɗanda suka hadasa maƙarƙashiya tare da Absalom.” Saboda haka Dawuda ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji ka mai da shawarar Ahitofel ta zama shiririta.”
Forsothe it was teld to Dauid, that Achitofel was in the sweryng togidere with Absolon; and Dauid seide, Lord, Y byseche, make thou fonned the counsel of Achitofel.
32 Da Dawuda ya isa ƙwanƙoli, inda mutane sun saba yi wa Allah sujada, Hushai, mutumin Arkitawa kuwa yana can don yă tarye shi, taguwarsa a yage, ga kuma ƙura a kansa.
And whanne Dauid stiede in to the hiyenesse of the hil, in which he schulde worschipe the Lord, lo! Cusi of Arath, with the cloth to-rent, and with the heed ful of erthe, cam to hym.
33 Sai Dawuda ya ce masa, “In ka tafi tare da ni, za ka zama mini kaya.
And Dauid seide to hym, If thou comest with me, thou schalt be to me to charge; sotheli if thou turnest ayen in to the citee,
34 Amma in ka koma birni, ka gaya wa Absalom, ‘Zan zama bawanka, ya sarki; dā ni bawan mahaifinka ne, amma yanzu zan zama bawanka,’ ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel.
and seist to Absolon, Y am thi seruaunt, kyng, suffre thou me to lyue; as Y was the seruaunt of thi fadir, so Y schal be thi seruaunt; thou schalt distrye the counsel of Achitofel.
35 Ba Zadok da Abiyatar firistocin nan suna nan tare da kai ba? Ka gaya musu duk abin da ka ji a fadan sarki.
Forsothe thou hast with thee Sadoch and Abiathar, preestis; and `thou schalt schewe ech word, what euer word thou schalt here in the hows of the kyng, to Sadoch and Abiathar, preestis.
36 ’Ya’yansu biyu maza, Ahimawaz ɗan Zadok, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar, suna can tare da su. Ka aike su wurina da duk abin da ka ji.”
Sotheli twei sones `of hem ben with hem, Achymaas, sone of Sadoch, and Jonathan, sone of Abiathar; and ye schulen sende bi hem to me ech word which ye schulen here.
37 Saboda haka Hushai abokin Dawuda ya isa Urushalima yayinda Absalom yake shigowa birnin.
Therfor whanne Chusi, freend of Dauid, cam in to the citee, also Absolon entryde in to Jerusalem.

< 2 Sama’ila 15 >