< 2 Sama’ila 15 >

1 Ana nan sai Absalom ya samo wa kansa wata keken yaƙi da dawakai tare da mutum hamsin da za su sha gabansa.
It came about after this that Absalom prepared a chariot and horses for himself, with fifty men to run before him.
2 Absalom yakan tashi da sassafe yă tsaya a gefen hanyar shigar ƙofar birni. Duk sa’ad da wani ya zo da ƙara don a kai gaban sarki yă yi shari’a, Absalom yakan kira shi yă ce, “Daga wane gari ka fito?” Sai mutumin yă amsa yă ce, “Bawanka ya fito a ɗaya daga cikin kabilan Isra’ila.”
Absalom would get up early and stand beside the road leading to the city gate. When any man had a dispute to come to the king for judgment, Absalom called to him and said, “From what city have you come?” Then the man would answer, “Your servant is from one of the tribes of Israel.”
3 Sai Absalom yă ce masa, “Ga shi, ƙararka daidai ne, tana kuma da gaskiya, sai dai ba wakilin sarkin da zai ji ka.”
So Absalom would say to him, “Look, your case is good and right, but there is no one empowered by the king to hear your case.”
4 Absalom kuwa yakan ƙara da cewa, “Da a ce an naɗa ni alƙali a ƙasar mana! Da duk mai ƙara, ko kuka wanda zai zo wurina, zan in tabbatar an yi masa adalci.”
Absalom added, “I wish that I were made judge in the land, so that every man who had any dispute or cause might come to me, and I would bring him justice!”
5 Kuma duk sa’ad da wani ya zo wurin Absalom ya rusuna don yă gaishe shi, sai Absalom yă sa hannunsa yă ta da shi, yă kuma rungume shi.
So it came about that when any man came to Absalom to honor him, Absalom would put out his hand and take hold of him and kiss him.
6 Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
Absalom acted in this way to all Israel who came to the king for judgment. So Absalom stole the hearts of the men of Israel.
7 A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
It came about at the end of four years that Absalom said to the king, “Please let me go and pay a vow that I have made to Yahweh in Hebron.
8 Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’”
For your servant made a vow while I was living at Geshur in Aram, saying,' If Yahweh will indeed bring me again to Jerusalem, then I will worship Yahweh.'”
9 Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
So the king said to him, “Go in peace.” So Absalom arose and went to Hebron.
10 Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’”
But then Absalom sent spies throughout all the tribes of Israel, saying, “As soon as you hear the sound of the trumpet, then you must say, 'Absalom is king in Hebron.'”
11 Mutum ɗari biyu daga Urushalima suka raka Absalom. An gayyace su a matsayin baƙi, suka kuwa tafi cikin rashin sani, ba su san wani abu game da al’amarin ba.
With Absalom went two hundred men from Jerusalem, who were invited. They went in their innocence, not knowing anything that Absalom had planned.
12 Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
While Absalom offered sacrfices, he sent for Ahithophel from his hometown of Giloh. He was David's counselor. Absalom's conspiracy was strong, for the people following Absalom were constantly increasing.
13 Wani manzo ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra’ila sun koma wajen Absalom.”
A messenger came to David saying, “The hearts of the men of Israel are following after Absalom.”
14 Sai Dawuda ya ce wa dukan fadawansa da suke tare da shi a Urushalima, “Ku zo! Mu gudu, in ba haka ba, babu wanda zai tsira daga hannun Absalom. Dole mu bar nan, nan da nan, in ba haka ba zai tashi da sauri yă fāɗa mana, yă kuma hallaka garin da takobi.”
So David said to all his servants who were with him at Jerusalem, “Arise and let us flee, or none of us will escape from Absalom. Prepare to leave immediately, or he will quickly overtake us, and he will bring down disaster on us and attack the city with the edge of the sword.”
15 Sai fadawan sarki suka ce masa, “Barorinka suna a shirye su yi duk abin da ranka yă daɗe, ya zaɓa.”
The king's servants said to the king, “Look, your servants are ready to do whatever our master the king decides.”
16 Sarki ya kama hanya, dukan gidansa kuwa suna biye da shi; amma ya bar ƙwarƙwarai goma su lura da fada.
The king left and all his family after him, but the king left ten women, who were concubines, to keep the palace.
17 Ta haka sarki ya kama hanya da dukan mutane suna biye da shi, suka yi sansani a wani wuri mai ɗan nisa da Urushalima.
After the king went out and all the people after him, they stopped at the last house.
18 Dukan mutanensa suka wuce gabansa, tare da dukan Keretawa da Feletiyawa; da dukan mutane ɗari shida na Gittiyawan da suka raka shi daga Gat, suka wuce gaban sarki.
All his army marched with him, and before him went all the Kerethites, and all the Pelethites, and all the Gittites—six hundred men who had followed him from Gath.
19 Sarki ya ce wa Ittai mutumin Gat, “Don me za ka zo tare da mu? Ka koma ka zauna tare da Sarki Absalom. Kai baƙo ne, ɗan gudun hijira daga garinka.
Then the king said to Ittai the Gittite, “Why will you come with us? Return and stay with the king, for you are a foreigner and an exile. Return to your own place.
20 Jiya-jiya ka zo. Yau kuma in sa ka yi ta yawo tare da mu, ga shi ban ma san inda za ni ba? Koma, ka tafi da’yan’uwanka. Bari alheri da amincin Ubangiji su kasance tare da kai.”
Since you just left yesterday, why should I make you wander all over with us? I do not even know where I am going. So return and take your fellow countrymen back. May loyalty and faithfulness go with you.”
21 Amma Ittai ya ce wa sarki, “Muddin Ubangiji yana a raye kuma muddin ranka yă daɗe yana a raye, duk inda ranka yă daɗe sarki zai kasance, ko a yi rai ko a mutu, a can bawanka zai kasance.”
But Ittai answered the king and said, “As Yahweh lives, and as my master the king lives, surely in whatever place where my master the king goes, there also will your servant go, whether that means living or dying.”
22 Dawuda ya ce wa Ittai, “Wuce gaba, taka mu je.” Sai Ittai mutumin Gat ya shiga layi tare da dukan mutanensa da iyalan da suke tare da shi.
So David said to Ittai, “Go ahead and continue with us.” So Ittai the Gittite marched with the king, along with all his men and all the families who were with him.
23 Dukan ƙauyuka suka yi ta kururuwa yayinda mutanen suke wucewa. Sarki shi ma ya haye ta Kwarin Kidron, mutane kuma suka ci gaba da tafiya zuwa wajen hamada.
All the country wept with a loud voice as all the people passed by over the Kidron Valley, and as the king also himself crossed over. All the people traveled on the road toward the wilderness.
24 Zadok yana nan tare da su, kuma dukan Lawiyawan da suke tare da shi kuwa suna ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka sauke akwatin alkawarin Allah, Abiyatar ya miƙa hadaya sai da mutane suka gama fita daga birnin.
Even Zadok with all the Levites, carrying the ark of the covenant of God, were present. They set the ark of God down, and then Abiathar joined them. They waited until all the people had passed by out of the city.
25 Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
The king said to Zadok, “Carry the ark of God back into the city. If I find favor in the eyes of Yahweh, he will bring me back here and show me again the ark and the place where he lives.
26 Amma in ya ce, ‘Ina baƙin ciki da kai,’ to, ina a shirye; bari yă yi abin da ya fi masa.”
But if he says, 'I am not pleased with you,' look, here am I, let him do to me whatever seems good to him.”
27 Sarki ya kuma ce wa Zadok firist, “Ashe, kai ba mai duba ba ne? Ka koma cikin birnin lafiya, tare da ɗanka Ahimawaz, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar. Kai da Abiyatar ku tafi da’ya’yanku biyu.
The king also said to Zadok the priest, “Are you not a seer? Return into the city in peace, and your two sons with you, Ahimaaz your son, and Jonathan son of Abiathar.
28 Zan kuwa jira a mashigai a hamada, sai na ji daga gare ku.”
See, I will wait at the fords of the Arabah until word comes from you to inform me.”
29 Saboda haka Zadok da Abiyatar suka ɗauki akwatin alkawarin Allah suka komar da shi Urushalima, suka zauna a can.
So Zadok and Abiathar carried the ark of God back into Jerusalem, and they stayed there.
30 Amma Dawuda ya ci gaba yana hawan Dutsen Zaitun, yana kuka yayinda yake tafiya; kansa a rufe, kuma babu takalma a ƙafafunsa. Dukan mutanen da suke tare da shi suka rufe kawunansu suna ta kuka yayinda suke haurawa.
But David ascended barefoot and weeping up the Mount of Olives, and he had his head covered. Every man of the people who were with him covered his head, and they went up weeping as they walked.
31 To, an gaya wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin waɗanda suka hadasa maƙarƙashiya tare da Absalom.” Saboda haka Dawuda ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji ka mai da shawarar Ahitofel ta zama shiririta.”
Someone told David saying, “Ahithophel is among the conspirators with Absalom.” So David prayed, “O Yahweh, please turn Ahithophel's advice into foolishness.”
32 Da Dawuda ya isa ƙwanƙoli, inda mutane sun saba yi wa Allah sujada, Hushai, mutumin Arkitawa kuwa yana can don yă tarye shi, taguwarsa a yage, ga kuma ƙura a kansa.
It came about that when David arrived at the top of the road, where God used to be worshiped, Hushai the Arkite came to meet him with his coat torn and earth on his head.
33 Sai Dawuda ya ce masa, “In ka tafi tare da ni, za ka zama mini kaya.
David said to him, “If you travel with me, then you will be a burden to me.
34 Amma in ka koma birni, ka gaya wa Absalom, ‘Zan zama bawanka, ya sarki; dā ni bawan mahaifinka ne, amma yanzu zan zama bawanka,’ ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel.
But if you return to the city and say to Absalom, 'I will be your servant, king, as I have been your father's servant in time past, so will I now be your servant,' then you will confuse Ahithophel's advice for me.
35 Ba Zadok da Abiyatar firistocin nan suna nan tare da kai ba? Ka gaya musu duk abin da ka ji a fadan sarki.
Will you not have the priests Zadok and Abiathar with you? So whatever you hear in the king's palace, you must tell it to Zadok and Abiathar the priests.
36 ’Ya’yansu biyu maza, Ahimawaz ɗan Zadok, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar, suna can tare da su. Ka aike su wurina da duk abin da ka ji.”
See that they have there with them their two sons, Ahimaaz, Zadok's son, and Jonathan, Abiathar's son. You must send to me by their hand everything that you hear.”
37 Saboda haka Hushai abokin Dawuda ya isa Urushalima yayinda Absalom yake shigowa birnin.
So Hushai, David's friend, came into the city as Absalom arrived and entered into Jerusalem.

< 2 Sama’ila 15 >