< 2 Sama’ila 15 >

1 Ana nan sai Absalom ya samo wa kansa wata keken yaƙi da dawakai tare da mutum hamsin da za su sha gabansa.
Some time later, Absalom acquired a chariot and horses [to pull it]. He [hired] 50 men to run in front of him [to honor him while he was riding around Jerusalem in the chariot].
2 Absalom yakan tashi da sassafe yă tsaya a gefen hanyar shigar ƙofar birni. Duk sa’ad da wani ya zo da ƙara don a kai gaban sarki yă yi shari’a, Absalom yakan kira shi yă ce, “Daga wane gari ka fito?” Sai mutumin yă amsa yă ce, “Bawanka ya fito a ɗaya daga cikin kabilan Isra’ila.”
Furthermore, he always rose early [each morning] and stood by the city gate. Whenever someone came there with a dispute/quarrel that he wanted the king to decide, Absalom would call out to him, asking “What city are you from?” When the person told him what [city and] tribe he was from,
3 Sai Absalom yă ce masa, “Ga shi, ƙararka daidai ne, tana kuma da gaskiya, sai dai ba wakilin sarkin da zai ji ka.”
Absalom would say to him, “Listen, [I am sure that] what you are saying/claiming is right. But there is no one whom the king has appointed/authorized to listen to [people like] you.”
4 Absalom kuwa yakan ƙara da cewa, “Da a ce an naɗa ni alƙali a ƙasar mana! Da duk mai ƙara, ko kuka wanda zai zo wurina, zan in tabbatar an yi masa adalci.”
Absalom would then add, “I wish that I were a judge in this land. If I were a judge, anyone who had a dispute could come to me, and I would decide it fairly/justly.”
5 Kuma duk sa’ad da wani ya zo wurin Absalom ya rusuna don yă gaishe shi, sai Absalom yă sa hannunsa yă ta da shi, yă kuma rungume shi.
And whenever anyone came near to Absalom to bow respectfully in front of him, Absalom would reach out and embrace him and kiss him.
6 Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
Absalom did this to everyone in Israel who came to the king because of having a dispute with someone. In that way, Absalom persuaded all the Israeli people to be more pleased with him [IDM] [than they were pleased with David].
7 A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
Four years later, Absalom [went to] the king and said, “Please allow me to go to Hebron [city], in order that I can do what I promised Yahweh that I would do.
8 Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’”
When I was living in Geshur, in Syria, I promised Yahweh that if he brought me back to Jerusalem, I would worship him [in Hebron].”
9 Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
The king replied, “You may go.” So Absalom went to Hebron.
10 Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’”
But [while he was there, ] he secretly sent messengers to all the tribes in Israel, to tell them, “When you hear the sound of the trumpets [being blown], shout ‘Absalom has become the king at Hebron!’”
11 Mutum ɗari biyu daga Urushalima suka raka Absalom. An gayyace su a matsayin baƙi, suka kuwa tafi cikin rashin sani, ba su san wani abu game da al’amarin ba.
Absalom had taken with him to Hebron 200 men from Jerusalem, but they did not know [what Absalom was planning to do].
12 Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
While Absalom was offering sacrifices [at Hebron], he sent a message to Ahithophel, from Giloh [town], requesting him to come. Ahithophel was one of the king’s advisors. So the number of people who joined Absalom and who were ready to rebel [against David] became larger.
13 Wani manzo ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra’ila sun koma wajen Absalom.”
Soon a messenger came to David and said to him, “All [HYP] the Israeli people [SYN] are joining Absalom to rebel against you!”
14 Sai Dawuda ya ce wa dukan fadawansa da suke tare da shi a Urushalima, “Ku zo! Mu gudu, in ba haka ba, babu wanda zai tsira daga hannun Absalom. Dole mu bar nan, nan da nan, in ba haka ba zai tashi da sauri yă fāɗa mana, yă kuma hallaka garin da takobi.”
So David said to all his officials, “We must leave immediately if we want to escape from Absalom! We must go quickly, before he [and his men] arrive. If we do not do that, they will kill us and everyone else in the city!”
15 Sai fadawan sarki suka ce masa, “Barorinka suna a shirye su yi duk abin da ranka yă daɗe, ya zaɓa.”
The king’s officials said, “Okay, your majesty, we are ready to do whatever you decide.”
16 Sarki ya kama hanya, dukan gidansa kuwa suna biye da shi; amma ya bar ƙwarƙwarai goma su lura da fada.
So the king left ten of his slave wives there to take care of the palace, but all the other people in his palace went with him.
17 Ta haka sarki ya kama hanya da dukan mutane suna biye da shi, suka yi sansani a wani wuri mai ɗan nisa da Urushalima.
When they all were leaving [the city], they stopped at the last house.
18 Dukan mutanensa suka wuce gabansa, tare da dukan Keretawa da Feletiyawa; da dukan mutane ɗari shida na Gittiyawan da suka raka shi daga Gat, suka wuce gaban sarki.
The king and his officials stood there while his bodyguards went by in front of him. 600 soldiers from Gath [city] also walked by in front of him.
19 Sarki ya ce wa Ittai mutumin Gat, “Don me za ka zo tare da mu? Ka koma ka zauna tare da Sarki Absalom. Kai baƙo ne, ɗan gudun hijira daga garinka.
Then David said to Ittai, [the leader of the soldiers] from Gath, “(Why are you going with us?/You should not be going with us.) [RHQ] Go back and stay with [Absalom] the [new] king. You are not an Israeli; you are living away from your own land.
20 Jiya-jiya ka zo. Yau kuma in sa ka yi ta yawo tare da mu, ga shi ban ma san inda za ni ba? Koma, ka tafi da’yan’uwanka. Bari alheri da amincin Ubangiji su kasance tare da kai.”
You have lived here [in Israel] for only a short time [HYP]. And we do not even know where we will be going. So it is not right [RHQ] for me to force you to wander around with us. And take your troops with you. And I hope/wish that Yahweh will faithfully love and be loyal to you.”
21 Amma Ittai ya ce wa sarki, “Muddin Ubangiji yana a raye kuma muddin ranka yă daɗe yana a raye, duk inda ranka yă daɗe sarki zai kasance, ko a yi rai ko a mutu, a can bawanka zai kasance.”
But Ittai replied, “Your Majesty, as surely as you live, wherever you go, I will go; I will stay with you, whether they kill me or allow me to live.”
22 Dawuda ya ce wa Ittai, “Wuce gaba, taka mu je.” Sai Ittai mutumin Gat ya shiga layi tare da dukan mutanensa da iyalan da suke tare da shi.
David replied to Ittai, “Okay, march with us!” So Ittai and all his troops and their families went [with David].
23 Dukan ƙauyuka suka yi ta kururuwa yayinda mutanen suke wucewa. Sarki shi ma ya haye ta Kwarin Kidron, mutane kuma suka ci gaba da tafiya zuwa wajen hamada.
All the people [along the road] cried when they saw them walking by. The king and all the others crossed the Kidron Valley and then they all went [up the hill] toward the desert.
24 Zadok yana nan tare da su, kuma dukan Lawiyawan da suke tare da shi kuwa suna ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka sauke akwatin alkawarin Allah, Abiyatar ya miƙa hadaya sai da mutane suka gama fita daga birnin.
Abiathar and Zadok, [the priests, ] were walking with them. The descendants of Levi [who helped the priests] also went with them, carrying the sacred chest that contained the Ten Commandments. But they set it on the ground until all the others had left the city.
25 Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
Then the king said to Zadok, “You and Abiathar take the sacred chest back into the city. If Yahweh is pleased with me, he will some day allow me to return to see it and the place where it is kept.
26 Amma in ya ce, ‘Ina baƙin ciki da kai,’ to, ina a shirye; bari yă yi abin da ya fi masa.”
But if he says that he is not pleased with me, then I am willing for him to do to me whatever he thinks is good.”
27 Sarki ya kuma ce wa Zadok firist, “Ashe, kai ba mai duba ba ne? Ka koma cikin birnin lafiya, tare da ɗanka Ahimawaz, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar. Kai da Abiyatar ku tafi da’ya’yanku biyu.
He also said to Zadok, “Listen [to what I suggest]. You and Abiathar return to the city peacefully/safely, and take your son Ahimaaz and Abiathar’s son Jonathan with you.
28 Zan kuwa jira a mashigai a hamada, sai na ji daga gare ku.”
I will wait in the desert at the place where people can walk across the river, until you send a message to me.”
29 Saboda haka Zadok da Abiyatar suka ɗauki akwatin alkawarin Allah suka komar da shi Urushalima, suka zauna a can.
So Zadok and Abiathar carried the sacred chest back to Jerusalem, and they stayed there.
30 Amma Dawuda ya ci gaba yana hawan Dutsen Zaitun, yana kuka yayinda yake tafiya; kansa a rufe, kuma babu takalma a ƙafafunsa. Dukan mutanen da suke tare da shi suka rufe kawunansu suna ta kuka yayinda suke haurawa.
David [and those with him] went up Olive [Tree] Hill. David was crying while he walked. He was walking barefoot and had something covering his head [to show that he was sorrowful]. All those who were going with him also covered their heads and were crying while they walked.
31 To, an gaya wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin waɗanda suka hadasa maƙarƙashiya tare da Absalom.” Saboda haka Dawuda ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji ka mai da shawarar Ahitofel ta zama shiririta.”
Someone told David that Ahithophel had joined with those who were rebelling against David. So David prayed, “Yahweh, cause whatever Ahithophel suggests to Absalom [that he should do to be considered] to be foolish!”
32 Da Dawuda ya isa ƙwanƙoli, inda mutane sun saba yi wa Allah sujada, Hushai, mutumin Arkitawa kuwa yana can don yă tarye shi, taguwarsa a yage, ga kuma ƙura a kansa.
When they arrived at the top of the hill, where there was a place where the people worshiped [God], suddenly Hushai, from the Arki people-group, met David. He had torn his clothes and put dirt on his head [to show that he was very sad].
33 Sai Dawuda ya ce masa, “In ka tafi tare da ni, za ka zama mini kaya.
David said to him, “If you go with me, you will not be able to help me.
34 Amma in ka koma birni, ka gaya wa Absalom, ‘Zan zama bawanka, ya sarki; dā ni bawan mahaifinka ne, amma yanzu zan zama bawanka,’ ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel.
But if you return to the city, [you can help me by] saying to Absalom, ‘Your Majesty, I will serve you as faithfully as I served your father.’ If you do that [and stay near Absalom], you will be able to oppose any advice that Ahithophel gives to Absalom.
35 Ba Zadok da Abiyatar firistocin nan suna nan tare da kai ba? Ka gaya musu duk abin da ka ji a fadan sarki.
Zadok and Abiathar the priests are already there [RHQ]. Whatever you hear people say in the king’s palace, tell it to Zadok and Abiathar.
36 ’Ya’yansu biyu maza, Ahimawaz ɗan Zadok, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar, suna can tare da su. Ka aike su wurina da duk abin da ka ji.”
Keep in mind that Zadok’s son Ahimaaz and Abiathar’s son Jonathan are also there. You can tell them whatever you find out, and send them to report it to me.”
37 Saboda haka Hushai abokin Dawuda ya isa Urushalima yayinda Absalom yake shigowa birnin.
So David’s friend Hushai returned to the city, at the same time that Absalom was entering Jerusalem.

< 2 Sama’ila 15 >