< 2 Sama’ila 15 >

1 Ana nan sai Absalom ya samo wa kansa wata keken yaƙi da dawakai tare da mutum hamsin da za su sha gabansa.
And it was from after thus and he acquired for himself Absalom a chariot and horses and fifty man [who] ran before him.
2 Absalom yakan tashi da sassafe yă tsaya a gefen hanyar shigar ƙofar birni. Duk sa’ad da wani ya zo da ƙara don a kai gaban sarki yă yi shari’a, Absalom yakan kira shi yă ce, “Daga wane gari ka fito?” Sai mutumin yă amsa yă ce, “Bawanka ya fito a ɗaya daga cikin kabilan Isra’ila.”
And he rose early Absalom and he stood at [the] side of [the] road of the gate and it was every person whom it belonged to him a case at law to come to the king for judgment and he called out Absalom to him and he said where? from this city [are] you and he said [is] from one of [the] tribes of Israel servant your.
3 Sai Absalom yă ce masa, “Ga shi, ƙararka daidai ne, tana kuma da gaskiya, sai dai ba wakilin sarkin da zai ji ka.”
And he said to him Absalom see matter your [are] good and right and [one who] hears not [belongs] to you from with the king.
4 Absalom kuwa yakan ƙara da cewa, “Da a ce an naɗa ni alƙali a ƙasar mana! Da duk mai ƙara, ko kuka wanda zai zo wurina, zan in tabbatar an yi masa adalci.”
And he said Absalom who? will he make me a judge in the land and to me he will come every person whom it belongs to him a case at law and a judgment and I will do justice him.
5 Kuma duk sa’ad da wani ya zo wurin Absalom ya rusuna don yă gaishe shi, sai Absalom yă sa hannunsa yă ta da shi, yă kuma rungume shi.
And it was when drew near anyone to bow down to him and he stretched out hand his and he took hold of him and he kissed him.
6 Absalom ya yi ta yin haka ga dukan Isra’ilawan da suka zo wurin sarki don neman adalci, ta haka kuwa ya saci zukatan mutanen Isra’ila.
And he did Absalom according to the manner this to all Israel who they came for judgment to the king and he stole Absalom [the] heart of [the] men of Israel.
7 A ƙarshen shekara huɗu, Absalom ya ce wa sarki, “Bari in tafi Hebron in cika alkawarin da na yi wa Ubangiji.
And it was from [the] end of forty year[s] and he said Absalom to the king let me go please so I may pay vow my which I vowed to Yahweh in Hebron.
8 Yayinda bawanka yake zama a Geshur, a Aram, na yi wannan alkawari, na ce, ‘In Ubangiji ya komo da ni Urushalima, zan yi wa Ubangiji sujada a Hebron.’”
For a vow he vowed servant your when dwelt I at Geshur in Aram saying if (certainly *Q(K)*) he will bring back me Yahweh Jerusalem and I will serve Yahweh (in Hebron. *X*)
9 Sarki ya ce, “Ka sauka lafiya.” Sai ya tafi Hebron.
And he said to him the king go in peace and he arose and he went Hebron towards.
10 Sai Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra’ila, ya ce musu su ce, “Da zarar kuka ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom sarki ne a Hebron.’”
And he sent Absalom spies in all [the] tribes of Israel saying when hear you [the] sound of the ram's horn and you will say he has become king Absalom in Hebron.
11 Mutum ɗari biyu daga Urushalima suka raka Absalom. An gayyace su a matsayin baƙi, suka kuwa tafi cikin rashin sani, ba su san wani abu game da al’amarin ba.
And with Absalom they went two hundred man from Jerusalem [those who] were invited and [those who] were going to innocence their and not they knew any thing.
12 Yayinda Absalom yake miƙa hadaya, ya aika a kira Ahitofel mutumin Gilo, mai ba wa Dawuda shawara, yă zo daga Gilo garinsa. Ta haka makircin ya ƙara ƙarfi, masu bin Absalom kuma suka yi ta ƙaruwa.
And he sent Absalom Ahithophel the Gilonite [the] counselor of David from city his from Giloh when sacrificed he the sacrifices and it was the conspiracy strong and the people [was] going and numerous with Absalom.
13 Wani manzo ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra’ila sun koma wajen Absalom.”
And he came the messenger to David saying it is [the] heart of [the] man of Israel after Absalom.
14 Sai Dawuda ya ce wa dukan fadawansa da suke tare da shi a Urushalima, “Ku zo! Mu gudu, in ba haka ba, babu wanda zai tsira daga hannun Absalom. Dole mu bar nan, nan da nan, in ba haka ba zai tashi da sauri yă fāɗa mana, yă kuma hallaka garin da takobi.”
And he said David to all servants his who [were] with him in Jerusalem arise so let us flee for not it will belong to us an escape from before Absalom hurry to go lest he should hurry and he will overtake us and he will thrust on us calamity and he will strike the city to [the] mouth of [the] sword.
15 Sai fadawan sarki suka ce masa, “Barorinka suna a shirye su yi duk abin da ranka yă daɗe, ya zaɓa.”
And they said [the] servants of the king to the king according to all that he will choose lord my the king here! [are] servants your.
16 Sarki ya kama hanya, dukan gidansa kuwa suna biye da shi; amma ya bar ƙwarƙwarai goma su lura da fada.
And he went out the king and all household his at feet his and he left the king ten women concubines to keep the house.
17 Ta haka sarki ya kama hanya da dukan mutane suna biye da shi, suka yi sansani a wani wuri mai ɗan nisa da Urushalima.
And he went out the king and all the people at feet his and they stood [the] house of the distance.
18 Dukan mutanensa suka wuce gabansa, tare da dukan Keretawa da Feletiyawa; da dukan mutane ɗari shida na Gittiyawan da suka raka shi daga Gat, suka wuce gaban sarki.
And all servants his [were] passing by at side his and all the Kerethite[s] and all the Pelethite[s] and all the Gittites six hundred man who they had come at foot his from Gath [were] passing by at [the] face of the king.
19 Sarki ya ce wa Ittai mutumin Gat, “Don me za ka zo tare da mu? Ka koma ka zauna tare da Sarki Absalom. Kai baƙo ne, ɗan gudun hijira daga garinka.
And he said the king to Ittai the Gittite why? will you go also you with us return and dwell with the king for [are] a foreigner you and also [are] an exile you to place your.
20 Jiya-jiya ka zo. Yau kuma in sa ka yi ta yawo tare da mu, ga shi ban ma san inda za ni ba? Koma, ka tafi da’yan’uwanka. Bari alheri da amincin Ubangiji su kasance tare da kai.”
[was] yesterday - Coming you and this day (will I make wander? you *Q(K)*) with us to go and I [am] going to where I [am] going return and take back brothers your [be] with you covenant loyalty and truth.
21 Amma Ittai ya ce wa sarki, “Muddin Ubangiji yana a raye kuma muddin ranka yă daɗe yana a raye, duk inda ranka yă daɗe sarki zai kasance, ko a yi rai ko a mutu, a can bawanka zai kasance.”
And he answered Ittai the king and he said [by] [the] life of Yahweh and [by] [the] life of lord my the king that except in [the] place where he will be there - lord my the king whether for death or for life for there he will be servant your.
22 Dawuda ya ce wa Ittai, “Wuce gaba, taka mu je.” Sai Ittai mutumin Gat ya shiga layi tare da dukan mutanensa da iyalan da suke tare da shi.
And he said David to Ittai come and pass on and he passed on Ittai the Gittite and all men his and all the little one[s] who [were] with him.
23 Dukan ƙauyuka suka yi ta kururuwa yayinda mutanen suke wucewa. Sarki shi ma ya haye ta Kwarin Kidron, mutane kuma suka ci gaba da tafiya zuwa wajen hamada.
And all the land [were] weeping a voice great and all the people [were] passing by and the king [was] passing in [the] wadi of Kidron and all the people [were] passing on on [the] face of [the] road the wilderness.
24 Zadok yana nan tare da su, kuma dukan Lawiyawan da suke tare da shi kuwa suna ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka sauke akwatin alkawarin Allah, Abiyatar ya miƙa hadaya sai da mutane suka gama fita daga birnin.
And there! also Zadok and all the Levites with him [were] carrying [the] ark of [the] covenant of God and they set down [the] ark of God and he went up Abiathar until was finished all the people to pass out from the city.
25 Sa’an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka komar da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a idon Ubangiji, zai dawo da ni, yă kuma sa in sāke gan shi a mazauninsa.
And he said the king to Zadok take back [the] ark of God the city if I will find favor in [the] eyes of Yahweh and he will bring back me and he will show me it and habitation his.
26 Amma in ya ce, ‘Ina baƙin ciki da kai,’ to, ina a shirye; bari yă yi abin da ya fi masa.”
And if thus he will say not I delight in you here [am] I let him do to me just as it is good in view his.
27 Sarki ya kuma ce wa Zadok firist, “Ashe, kai ba mai duba ba ne? Ka koma cikin birnin lafiya, tare da ɗanka Ahimawaz, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar. Kai da Abiyatar ku tafi da’ya’yanku biyu.
And he said the king to Zadok the priest ¿ a seer [are] you return! the city in peace and Ahimaaz son your and Jonathan [the] son of Abiathar [the] two sons your with you.
28 Zan kuwa jira a mashigai a hamada, sai na ji daga gare ku.”
See I [will] delay (in [the] desert plains of *Q(K)*) the wilderness until comes word from with you to tell to me.
29 Saboda haka Zadok da Abiyatar suka ɗauki akwatin alkawarin Allah suka komar da shi Urushalima, suka zauna a can.
And he took back Zadok and Abiathar [the] ark of God Jerusalem and they remained there.
30 Amma Dawuda ya ci gaba yana hawan Dutsen Zaitun, yana kuka yayinda yake tafiya; kansa a rufe, kuma babu takalma a ƙafafunsa. Dukan mutanen da suke tare da shi suka rufe kawunansu suna ta kuka yayinda suke haurawa.
And David [was] going up on [the] ascent of the olive trees going up - and weeping and head of him [was] covered and he [was] walking barefoot and all the people which [was] with him they covered each head his and they went up continuously and wept.
31 To, an gaya wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin waɗanda suka hadasa maƙarƙashiya tare da Absalom.” Saboda haka Dawuda ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji ka mai da shawarar Ahitofel ta zama shiririta.”
And David someone told saying Ahithophel [is] among the conspirators with Absalom and he said David make foolish please [the] counsel of Ahithophel O Yahweh.
32 Da Dawuda ya isa ƙwanƙoli, inda mutane sun saba yi wa Allah sujada, Hushai, mutumin Arkitawa kuwa yana can don yă tarye shi, taguwarsa a yage, ga kuma ƙura a kansa.
And he was David coming to the top where he bowed down there to God and there! to meet him Hushai the Arkite [was] torn tunic his and earth [was] on head his.
33 Sai Dawuda ya ce masa, “In ka tafi tare da ni, za ka zama mini kaya.
And he said to him David if you pass over with me and you will become on me a burden.
34 Amma in ka koma birni, ka gaya wa Absalom, ‘Zan zama bawanka, ya sarki; dā ni bawan mahaifinka ne, amma yanzu zan zama bawanka,’ ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel.
And if the city you will return and you will say to Absalom servant your I O king I will be [was] [the] servant of father your I from then and now I [will be] servant your and you will frustrate for me [the] counsel of Ahithophel.
35 Ba Zadok da Abiyatar firistocin nan suna nan tare da kai ba? Ka gaya musu duk abin da ka ji a fadan sarki.
And ¿ not with you there [are] Zadok and Abiathar the priests and it will be every word which you will hear from [the] house of the king you will tell to Zadok and to Abiathar the priests.
36 ’Ya’yansu biyu maza, Ahimawaz ɗan Zadok, da kuma Yonatan ɗan Abiyatar, suna can tare da su. Ka aike su wurina da duk abin da ka ji.”
There! there [are] with them [the] two sons their Ahimaaz of Zadok and Jonathan of Abiathar and you will send by hand their to me every word which you will hear.
37 Saboda haka Hushai abokin Dawuda ya isa Urushalima yayinda Absalom yake shigowa birnin.
And he came Hushai [the] friend of David the city and Absalom he came Jerusalem.

< 2 Sama’ila 15 >