< 2 Sama’ila 14 >

1 Yowab, ɗan Zeruhiya ya gane cewa zuriyar sarki ta koma ga Absalom.
Et Joab, fils de Tseruïa, comprenait que le cœur du Roi revenait à l'égard d'Absalom.
2 Saboda haka Yowab ya aiki wani zuwa Tekowa, ya sa a zo da wata mace mai hikima. Ya ce mata, “Ki yi kamar kina makoki. Ki sa rigar makoki, kada kuwa ki shafa mai. Ki yi kamar macen da ta yi kwanaki da yawa, tana makokin matattu.
Alors Joab dépêcha à Thékôa et en fit venir une femme avisée; et il lui dit: Prends donc le deuil et revêts des habits de deuil, et ne t'oins pas d'huile, et aie l'attitude d'une femme depuis longtemps en deuil d'un mort;
3 Sa’an nan ki je wurin sarki, ki ce masa haka.” Sai Yowab ya faɗa mata duk abin da za tă faɗa.
puis présente-toi au Roi et lui parle de telle et telle manière. Et il lui mit dans la bouche le discours à tenir.
4 Da macen da ta fito daga Tekowa ta je wajen sarki, sai ta rusuna har ƙasa don bangirma, sai ta ce, “Ka taimake ni, ya sarki!”
La femme Thékôïte vint donc parler au Roi, et elle se jeta le visage contre terre et se prosterna et dit: Sois secourable, ô Roi!
5 Sarki ya ce mata, “Mece ce matsalarki?” Sai ta ce, “Tabbatacce, ni gwauruwa ce; mijina ya mutu.
et le Roi lui dit: Qu'as-tu? Et elle dit: Au vrai, je suis veuve et mon mari est mort.
6 Baiwarka tana da’ya’ya maza biyu. Suka yi faɗa da juna a fili, kuma ba wanda yake can don yă raba su. Ɗayan ya bugi ɗayan, ya kashe shi.
Et ta servante avait deux fils, et ils eurent entre eux deux une rixe dans les champs, et il ne se trouva personne pour les séparer, et l'un porta un coup à l'autre et le tua.
7 To, ga duk iyali sun hau kan baiwarka, suna cewa, ‘Ki ba mu ɗayan da ya kashe ɗan’uwansa mu kashe don ran ɗan’uwansa da ya kashe; sa’an nan za mu hallaka magājin shi ma.’ Za su kashe garwashin wuta mai ci da nake da shi kaɗai, su bar mijina ba suna, ba jika, a duniya.”
Et voilà qu'il y eut une levée de toute la parenté contre ta servante, et ils dirent: Livre le fratricide afin que nous lui donnions la mort pour l'âme de son frère qu'il a égorgé! et ils veulent aussi détruire l'héritier, et ainsi éteindre le tison qui me reste pour ne laisser à mon mari ni nom ni lignée sur la face de la terre.
8 Sarki ya ce wa macen, “Koma gida, zan ba da umarni a madadinki.”
Et le Roi dit à la femme: Va dans ta maison! et moi, j'aviserai à ton égard.
9 Amma macen da ta fito daga Tekowa ta ce, “Ranka yă daɗe, sarki! Bari alhakin shari’arka yă kasance a kaina da gidan mahaifina, kai sarki da gidan mulkinka, ba ku da laifi a ciki.”
Et la femme Thékôïte dit au Roi: C'est à moi, ô Roi, mon Seigneur, qu'on s'en prendra de la dérogation, et à la maison de mon père et le Roi et son trône ne seront pas responsables!
10 Sai sarki ya ce, “In wani ya yi miki magana, ki kawo shi wurina, ba zai kuwa ƙara damunki ba.”
Et le Roi dit: Si quelqu'un te menace, amène-le-moi! il ne s'avisera plus de s'attaquer à toi!
11 Sai ta ce, “To, bari sarki yă rantse da Ubangiji Allahnsa don yă hana mai ramako yin ƙarin hallakawar da aka yi, domin kada a hallaka ɗana.” Sai ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, babu gashi guda na ɗanki da zai fāɗi ƙasa.”
Et elle dit: Oh! que le Roi, mon Seigneur, se souvienne de l'Éternel, ton Dieu, pour empêcher le vengeur du sang de multiplier les victimes et de faire périr le fils que j'ai! Et il dit: Par la vie de l'Éternel! non, si des cheveux de ton fils un seul tombe en terre.
12 Sai matar ta ce, “Bari baiwarka ta ƙara yin magana sau ɗayan nan wa ranka yă daɗe.” Ya ce, “Ki faɗa.”
Et la femme dit: Permets que ta servante dise un mot à mon Seigneur, le Roi! Et il dit: Parle!
13 Matar ta ce, “To, don me ka yi wa mutanen Allah irin wannan abu? Sa’ad da sarki ya ce haka, ashe, ba ka hukunta kanka ke nan ba, tun da yake sarki bai yarda ɗansa yă komo gida ba?
Et la femme dit: Pourquoi est-ce là ta manière de penser quand il s'agit du peuple de Dieu, puisque en se prononçant ainsi le Roi est comme coupable de ne pas accorder le retour de son banni?
14 Kamar ruwan da ya zuba a ƙasa, wanda ba a iya kwasa, haka dole mu mutu. Amma Allah ba ya ɗaukan rai; a maimako, yakan ƙirƙiro hanyoyi domin mutumin da aka kora kada yă kasance yasasshe daga gare shi.
Car il nous faut mourir tous, et nous devenons comme une eau épanchée sur la terre et qui ne se recueille plus; et Dieu ne se presse pas d'ôter une vie, mais Sa pensée constante est de ne pas repousser loin de Lui celui qui s'est banni.
15 “Yanzu ga shi na zo don in faɗa wannan wa ranka yă daɗe sarki, don mutane sun tsorata ni. Baiwarka ta yi tunani ta ce, ‘Zan yi magana wa sarki; wataƙila yă yi abin da baiwarsa ta roƙa.
Or, si je suis venue tenir ce langage au Roi, mon Seigneur, c'est que le peuple m'avait alarmée! et ta servante s'est dit: Je veux parler au Roi; peut-être donnera-t-il effet à la parole de sa servante.
16 Wataƙila sarki zai yarda yă ceci baiwarsa daga hannun mutumin nan da yake ƙoƙari yă hallaka ni da ɗana daga gādon da Allah ya ba mu.’
Oui, le Roi prêtera l'oreille pour sauver sa servante des mains de l'homme qui veut éliminer moi et mon fils à la fois de l'héritage de Dieu.
17 “Yanzu kuwa baiwarka tana cewa, ‘Bari magana ranka yă daɗe sarki yă ba ni hutu, gama ranka yă daɗe sarki yana kama da mala’ikan Allah cikin rarrabe nagarta da mugunta. Bari Ubangiji Allahnka yă kasance tare da kai.’”
Et ta servante se disait: Puisse le langage du Roi, mon Seigneur, servir à me tranquilliser! car pareil à un ange de Dieu, le Roi, mon Seigneur, saura entendre le bien et le mal: et que l'Éternel, ton Dieu, t'assiste!
18 Sai sarki ya ce wa matar, “Kada ki ɓoye mini kome daga abin da zan tambaye ki.” Matar ta ce, “Bari ranka yă daɗe sarki yă yi tambaya.”
Et le Roi répondit et dit à la femme: Ne me cache rien de ce que je vais te demander! Et la femme dit: Que mon Seigneur le Roi daigne parler!
19 Sarki ya ce, “Anya, babu hannun Yowab a cikin dukan wannan?” Matar ta ce, “Muddin kana a raye, ranka yă daɗe sarki, ba wanda zai juya dama ko hagu daga wani abin da ranka yă daɗe sarki ya faɗa. I, bawanka Yowab ne ya umarce ni in yi wannan, shi ne kuma ya sa kalmomin nan a bakin baiwarka.
Et le Roi dit: La main de Joab n'est-elle pas ta complice en tout ceci? Et la femme répondit et dit: Par ta vie, ô Roi, mon Seigneur! Ce n'est ni à droite ni à gauche qu'a frappé aucune des paroles du Roi, mon Seigneur! oui, c'est ton serviteur Joab qui m'a donné ses ordres, et a mis toutes ces paroles dans la bouche de ta servante.
20 Bawanka Yowab ne ya yi haka don yă daidaita al’amura. Ranka yă daɗe yana da hikima iri ta mala’ikan Allah, ya san dukan kome da yake faruwa a ƙasar.”
C'est pour donner à l'affaire une autre tournure que Joab s'y est pris de cette façon. Mais mon Seigneur a la sagesse d'un ange de Dieu pour savoir tout ce qui a lieu sur la terre.
21 Sarki ya ce wa Yowab, “To, da kyau, zan yi haka. Je ka, ka dawo da saurayin nan Absalom.”
Et le Roi dit à Joab: Eh bien! voici, je donne effet à cette parole: va donc, ramène le jeune homme, Absalom.
22 Yowab ya rusuna har ƙasa don bangirma, ya kuma yi wa sarki kyakkyawar fata. Yowab ya ce, “Yau, bawanka ya sani ya sami tagomashi a gare ka, ranka yă daɗe sarki, gama sarki ya ji roƙon bawansa.”
Alors Joab se jeta la face contre terre et se prosterna et bénit le Roi, et Joab. dit: Aujourd'hui ton serviteur sent qu'il a trouvé grâce à tes yeux, ô Roi, mon Seigneur, puisque le Roi met à effet la parole de son serviteur.
23 Sa’an nan Yowab ya tafi Geshur ya dawo da Absalom Urushalima.
Et Joab partit et se rendit à Gesur et il ramena Absalom à Jérusalem.
24 Amma sarki ya ce, “Yă tafi gidansa; kada yă zo yă gan ni.” Saboda haka Absalom ya tafi gidansa, bai kuwa je ganin sarki ba.
Mais le Roi dit: Qu'il se retire dans sa maison et ne se montre pas devant moi. Ainsi Absalom se retira dans sa maison et ne parut point devant le Roi.
25 A cikin dukan Isra’ila babu wanda ake yabon kyansa kamar Absalom. Tun daga kansa har zuwa tafin ƙafansa babu tabo a jikinsa.
Et dans tout Israël il n'y avait pas un homme qui eût la beauté d'Absalom; elle était fort célèbre; de la plante des pieds au sommet de la tête il était sans défaut.
26 A duk sa’ad da ya aske gashin kansa (yakan aske kansa lokaci-lokaci sa’ad da ya yi masa nauyi) yakan auna shi, nauyin gashin kuwa yakan kai wajen shekel ɗari biyu a ma’aunin da ake awo.
Et lorsqu'il se tondait la tête, — or toutes les années il se la tondait, car sa chevelure lui pesait, c'est pourquoi il la coupait; — le poids des cheveux de sa tête était de deux cents sicles, poids de Roi.
27 Aka haifa wa Absalom’ya’ya uku maza da’ya mace guda. Sunanta Tamar, ta kuwa zama kyakkyawan mace ƙwarai.
Et il était né à Absalom trois fils et une fille, nommée Thamar, et celle-ci était une femme belle de figure.
28 Absalom ya zauna a Urushalima shekara biyu amma ba tare da ganin fuskar sarki ba.
Et Absalom demeura ainsi deux ans à Jérusalem, mais sans paraître en la présence du Roi.
29 Sai Absalom ya aika a kira masa Yowab don yă aike shi wurin sarki, amma Yowab ya ƙi zuwa. Saboda haka ya sāke aika sau na biyu, amma ya ƙi yă zo.
Et Absalom manda Joab pour le députer auprès du Roi; mais il ne voulut pas venir; et il lui fit faire un second message, mais il ne voulut pas venir.
30 Sai ya ce wa bayinsa, “Duba, gonar Yowab tana gab da tawa, kuma yana da sha’ir a can. Ku je ku sa mata wuta.” Sai bayin Absalom suka sa wa gonar wuta.
Alors il dit à ses serviteurs: Voyez le champ de Joab à côté du mien, et il y a de l'orge; allez et mettez-y le feu. Et les serviteurs d'Absalom mirent le feu au champ.
31 Sa’an nan Yowab ya tafi gidan Absalom ya ce masa, “Me ya sa bayinka suka sa wa gonata wuta?”
Là-dessus Joab se leva et vint trouver Absalom chez lui et lui dit: Pourquoi tes serviteurs ont-ils mis le feu à mon champ?
32 Absalom ya ce wa Yowab, “Kai, na aika, ‘Ka zo nan don in aike ka wurin sarki ka tambaya, “Me ya sa na dawo daga Geshur? Ai, ya fi mini a ce ina can har yanzu!”’ Yanzu kuwa, ina so in ga sarki, kuma idan na yi wani laifi, to, yă kashe ni.”
Et Absalom dit à Joab: Voilà que je t'ai fait faire un message en ces termes: Viens ici et je te députerai auprès du Roi pour lui dire: Pourquoi suis-je revenu de Gesur? Mieux vaudrait pour moi d'y être encore; maintenant je veux voir le visage du Roi; si un crime est à ma charge, qu'il me fasse mourir!
33 Saboda haka Yowab ya tafi wurin sarki ya gaya masa wannan. Sai sarki ya aika aka zo da Absalom, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa a gaban sarki. Sarki kuwa ya sumbaci Absalom.
Alors Joab se présenta chez le Roi et lui fit rapport. Et il rappela Absalom, lequel vint chez le Roi et se prosterna devant le Roi face contre terre; et le Roi donna le baiser à Absalom.

< 2 Sama’ila 14 >