< 2 Sama’ila 14 >

1 Yowab, ɗan Zeruhiya ya gane cewa zuriyar sarki ta koma ga Absalom.
Da nu Joab, Zerujas Søn, mærkede, at Kongens Hjerte hang ved Absalom,
2 Saboda haka Yowab ya aiki wani zuwa Tekowa, ya sa a zo da wata mace mai hikima. Ya ce mata, “Ki yi kamar kina makoki. Ki sa rigar makoki, kada kuwa ki shafa mai. Ki yi kamar macen da ta yi kwanaki da yawa, tana makokin matattu.
sendte han Bud til Tekoa efter en klog Kvinde og sagde til hende: »Lad, som om du har Sorg, ifør dig Sørgeklæder, lad være at salve dig med Olie, men bær dig ad som en Kvinde, der alt i lang Tid har sørget over en afdød;
3 Sa’an nan ki je wurin sarki, ki ce masa haka.” Sai Yowab ya faɗa mata duk abin da za tă faɗa.
gaa saa til Kongen og sig saaledes til ham« — og Joab lagde hende Ordene i Munden.
4 Da macen da ta fito daga Tekowa ta je wajen sarki, sai ta rusuna har ƙasa don bangirma, sai ta ce, “Ka taimake ni, ya sarki!”
Kvinden fra Tekoa gik saa til Kongen, faldt til Jorden paa sit Ansigt, bøjede sig og sagde: »Hjælp Konge!«
5 Sarki ya ce mata, “Mece ce matsalarki?” Sai ta ce, “Tabbatacce, ni gwauruwa ce; mijina ya mutu.
Kongen spurgte hende: »Hvad fattes dig?« Og hun sagde: »Jo, jeg er Enke, min Mand er død.
6 Baiwarka tana da’ya’ya maza biyu. Suka yi faɗa da juna a fili, kuma ba wanda yake can don yă raba su. Ɗayan ya bugi ɗayan, ya kashe shi.
Din Trælkvinde havde to Sønner; de kom i Klammeri ude paa Marken, og der var ingen til at bilægge deres Tvist; saa slog den ene den anden ihjel.
7 To, ga duk iyali sun hau kan baiwarka, suna cewa, ‘Ki ba mu ɗayan da ya kashe ɗan’uwansa mu kashe don ran ɗan’uwansa da ya kashe; sa’an nan za mu hallaka magājin shi ma.’ Za su kashe garwashin wuta mai ci da nake da shi kaɗai, su bar mijina ba suna, ba jika, a duniya.”
Men nu træder hele Slægten op imod din Trælkvinde og siger: Udlever Brodermorderen, for at vi kan slaa ham ihjel og hævne Broderen, som han dræbte! Saaledes siger de for at faa Arvingen ryddet af Vejen og slukke den sidste Glød, jeg har tilbage, saa at min Mand ikke faar Eftermæle eller Efterkommere paa Jorden!«
8 Sarki ya ce wa macen, “Koma gida, zan ba da umarni a madadinki.”
Da sagde Kongen til Kvinden: »Gaa kun hjem, jeg skal jævne Sagen for dig!«
9 Amma macen da ta fito daga Tekowa ta ce, “Ranka yă daɗe, sarki! Bari alhakin shari’arka yă kasance a kaina da gidan mahaifina, kai sarki da gidan mulkinka, ba ku da laifi a ciki.”
Men Kvinden fra Tekoa sagde til Kongen: »Lad Skylden komme over mig og mit Fædrenehus, Herre Konge, men Kongen og hans Trone skal være skyldfri!«
10 Sai sarki ya ce, “In wani ya yi miki magana, ki kawo shi wurina, ba zai kuwa ƙara damunki ba.”
Kongen sagde da: »Enhver, som vil dig noget, skal du bringe til mig, saa skal han ikke mere volde dig Men!«
11 Sai ta ce, “To, bari sarki yă rantse da Ubangiji Allahnsa don yă hana mai ramako yin ƙarin hallakawar da aka yi, domin kada a hallaka ɗana.” Sai ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, babu gashi guda na ɗanki da zai fāɗi ƙasa.”
Men Kvinden sagde: »Vilde dog Kongen nævne HERREN din Guds Navn, for at Blodhævneren ikke skal volde endnu mere Ulykke og min Søn blive ryddet af Vejen!« Da sagde han: »Saa sandt HERREN lever, der skal ikke krummes et Haar paa din Søns Hoved!«
12 Sai matar ta ce, “Bari baiwarka ta ƙara yin magana sau ɗayan nan wa ranka yă daɗe.” Ya ce, “Ki faɗa.”
Da sagde Kvinden: »Maa din Trælkvinde sige min Herre Kongen et Ord?« Han svarede: »Tal!«
13 Matar ta ce, “To, don me ka yi wa mutanen Allah irin wannan abu? Sa’ad da sarki ya ce haka, ashe, ba ka hukunta kanka ke nan ba, tun da yake sarki bai yarda ɗansa yă komo gida ba?
Og Kvinden sagde: »Hvor kan du da tænke paa at gøre det samme ved Guds Folk — naar Kongen taler saaledes, dømmer han jo sig selv — og det gør Kongen, naar han ikke vil lade sin forstødte Søn vende tilbage.
14 Kamar ruwan da ya zuba a ƙasa, wanda ba a iya kwasa, haka dole mu mutu. Amma Allah ba ya ɗaukan rai; a maimako, yakan ƙirƙiro hanyoyi domin mutumin da aka kora kada yă kasance yasasshe daga gare shi.
Thi vi skal visselig alle dø, vi er som Vandet, der ikke kan samles op igen, naar det hældes ud paa Jorden; men Gud vil ikke tage det Menneskes Liv, der omgaas med den Tanke, at en forstødt ikke skal være forstødt for stedse.
15 “Yanzu ga shi na zo don in faɗa wannan wa ranka yă daɗe sarki, don mutane sun tsorata ni. Baiwarka ta yi tunani ta ce, ‘Zan yi magana wa sarki; wataƙila yă yi abin da baiwarsa ta roƙa.
Naar jeg nu er kommet for at tale om denne Sag til min Herre Kongen, saa er det, fordi de Folk har gjort mig bange; din Trælkvinde tænkte: Jeg vil tale til Kongen, maaske opfylder Kongen sin Trælkvindes Bøn;
16 Wataƙila sarki zai yarda yă ceci baiwarsa daga hannun mutumin nan da yake ƙoƙari yă hallaka ni da ɗana daga gādon da Allah ya ba mu.’
thi Kongen vil bønhøre mig og fri sin Trælkvinde af den Mands Haand, som tragter efter at udrydde mig tillige med min Søn af Guds Arvelod.
17 “Yanzu kuwa baiwarka tana cewa, ‘Bari magana ranka yă daɗe sarki yă ba ni hutu, gama ranka yă daɗe sarki yana kama da mala’ikan Allah cikin rarrabe nagarta da mugunta. Bari Ubangiji Allahnka yă kasance tare da kai.’”
Og din Trælkvinde tænkte: Min Herre Kongens Ord vil være mig en Lindring; thi min Herre Kongen er som en Guds Engel til at skønne over godt og ondt! HERREN din Gud være med dig!«
18 Sai sarki ya ce wa matar, “Kada ki ɓoye mini kome daga abin da zan tambaye ki.” Matar ta ce, “Bari ranka yă daɗe sarki yă yi tambaya.”
Da sagde Kongen til Kvinden: »Svar mig paa det Spørgsmaal, jeg nu stiller dig, dølg ikke noget!« Kvinden sagde: »Min Herre Kongen tale!«
19 Sarki ya ce, “Anya, babu hannun Yowab a cikin dukan wannan?” Matar ta ce, “Muddin kana a raye, ranka yă daɗe sarki, ba wanda zai juya dama ko hagu daga wani abin da ranka yă daɗe sarki ya faɗa. I, bawanka Yowab ne ya umarce ni in yi wannan, shi ne kuma ya sa kalmomin nan a bakin baiwarka.
Da sagde Kongen: »Har Joab en Finger med i alt dette?« Og Kvinden svarede: »Saa sandt du lever, Herre Konge, det er umuligt at slippe uden om, hvad min Herre Kongen siger. Ja, det var din Træl Joab, som paalagde mig dette og lagde din Trælkvinde alle disse Ord i Munden.
20 Bawanka Yowab ne ya yi haka don yă daidaita al’amura. Ranka yă daɗe yana da hikima iri ta mala’ikan Allah, ya san dukan kome da yake faruwa a ƙasar.”
For at give Sagen et andet Udseende har din Træl Joab gjort saaledes. Men min Herre er viis som en Guds Engel, saa han ved alle Ting paa Jorden!«
21 Sarki ya ce wa Yowab, “To, da kyau, zan yi haka. Je ka, ka dawo da saurayin nan Absalom.”
Derpaa sagde Kongen til Joab: »Vel, jeg vil gøre det! Gaa hen og bring den unge Mand, Absalom, tilbage!«
22 Yowab ya rusuna har ƙasa don bangirma, ya kuma yi wa sarki kyakkyawar fata. Yowab ya ce, “Yau, bawanka ya sani ya sami tagomashi a gare ka, ranka yă daɗe sarki, gama sarki ya ji roƙon bawansa.”
Da faldt Joab paa sit Ansigt til Jorden og bøjede sig og velsignede Kongen og sagde: »Nu ved din Træl, at jeg har fundet Naade for dine Øjne, Herre Konge, siden Kongen har opfyldt sin Træls Bøn!«
23 Sa’an nan Yowab ya tafi Geshur ya dawo da Absalom Urushalima.
Derpaa begav Joab sig til Gesjur og hentede Absalom tilbage til Jerusalem.
24 Amma sarki ya ce, “Yă tafi gidansa; kada yă zo yă gan ni.” Saboda haka Absalom ya tafi gidansa, bai kuwa je ganin sarki ba.
Men Kongen sagde: »Lad ham gaa hjem til sit Hus; for mit Aasyn bliver han ikke stedet!« Da gik Absalom hjem til sit Hus, og for Kongens Aasyn blev han ikke stedet.
25 A cikin dukan Isra’ila babu wanda ake yabon kyansa kamar Absalom. Tun daga kansa har zuwa tafin ƙafansa babu tabo a jikinsa.
Men ingen Mand i hele Israel blev beundret saa højt for sin Skønhed som Absalom; fra Fodsaal til Isse var der ikke en Lyde ved ham.
26 A duk sa’ad da ya aske gashin kansa (yakan aske kansa lokaci-lokaci sa’ad da ya yi masa nauyi) yakan auna shi, nauyin gashin kuwa yakan kai wajen shekel ɗari biyu a ma’aunin da ake awo.
Og naar han lod sit Haar klippe — han lod det klippe, hver Gang der var gaaet et Aar, fordi det blev ham for tungt, derfor maatte han lade det klippe — vejede det 200 Sekel efter kongelig Vægt.
27 Aka haifa wa Absalom’ya’ya uku maza da’ya mace guda. Sunanta Tamar, ta kuwa zama kyakkyawan mace ƙwarai.
Der fødtes Absalom tre Sønner og een Datter ved Navn Tamar; hun var en smuk Kvinde.
28 Absalom ya zauna a Urushalima shekara biyu amma ba tare da ganin fuskar sarki ba.
Absalom boede nu to Aar i Jerusalem uden at blive stedet for Kongen.
29 Sai Absalom ya aika a kira masa Yowab don yă aike shi wurin sarki, amma Yowab ya ƙi zuwa. Saboda haka ya sāke aika sau na biyu, amma ya ƙi yă zo.
Da sendte Absalom Bud efter Joab for at faa ham til at gaa til Kongen; men han vilde ikke komme. Han sendte Bud een Gang til, men han vilde ikke komme.
30 Sai ya ce wa bayinsa, “Duba, gonar Yowab tana gab da tawa, kuma yana da sha’ir a can. Ku je ku sa mata wuta.” Sai bayin Absalom suka sa wa gonar wuta.
Da sagde han til sine Folk »Se den Bygmark, Joab har der ved Siden af min! Gaa hen og stik Ild paa den!« Og Absaloms Folk stak Ild paa Marken.
31 Sa’an nan Yowab ya tafi gidan Absalom ya ce masa, “Me ya sa bayinka suka sa wa gonata wuta?”
Da begav Joab sig ind til Absalom og sagde til ham: »Hvorfor har dine Folk stukket Ild paa min Mark?«
32 Absalom ya ce wa Yowab, “Kai, na aika, ‘Ka zo nan don in aike ka wurin sarki ka tambaya, “Me ya sa na dawo daga Geshur? Ai, ya fi mini a ce ina can har yanzu!”’ Yanzu kuwa, ina so in ga sarki, kuma idan na yi wani laifi, to, yă kashe ni.”
Absalom svarede Joab: »Se, jeg sendte Bud efter dig og bad dig komme herhen, for at jeg kunde sende dig til Kongen og sige: Hvorfor kom jeg tilbage fra Gesjur? Det havde været bedre for mig, om jeg var blevet der! Men nu vil jeg stedes for Kongen; er der Skyld hos mig saa lad ham dræbe mig!«
33 Saboda haka Yowab ya tafi wurin sarki ya gaya masa wannan. Sai sarki ya aika aka zo da Absalom, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa a gaban sarki. Sarki kuwa ya sumbaci Absalom.
Joab gik da til Kongen og overbragte ham disse Ord. Saa lod han Absalom kalde, og han kom ind til Kongen; og han bøjede sig for ham og faldt paa sit Ansigt til Jorden for Kongen. Saa kyssede Kongen Absalom.

< 2 Sama’ila 14 >