< 2 Sama’ila 13 >

1 Ana nan sai Amnon ɗan Dawuda ya fara son Tamar, kyakkyawar’yar’uwar Absalom ɗan Dawuda.
И бысть по сих, и у Авессалома сына Давидова бе сестра добра взором зело, имя же ей Фамарь, и возлюби ю Амнон сын Давидов:
2 Amnon ya matsu ƙwarai har abin ya sa shi ciwo saboda ƙanuwarsa Tamar. Ya gane zai zama da wuya yă sadu da Tamar ita kaɗai, gama ba ta taɓa kwana da namiji ba.
и скорбяше Амнон, яко и разболетися (ему) сестры своея ради Фамары, зане дева бяше сия, и не удобно бе пред очима Амнонима что сотворити ей.
3 To, Amnon yana da wani aboki mai suna Yonadab, ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda. Yonadab dai mai wayo ne ƙwarai.
И бе Амнону друг, имя же ему Ионадав, сын Самаа брата Давидова, и Ионадав муж мудр зело.
4 Ya tambayi Amnon ya ce, “Don me kowace safiya fuskarka a ɓace take? Kai ba yaron sarki ba ne? Faɗa mini, me ke faruwa?” Amnon ya ce masa, “Ina son Tamar ƙanuwar wan nawa Absalom ne.”
И рече ему (Ионадав): что ти, яко ты тако болиши, сыне царев, утро утро? И не возвещаеши ми? И рече ему Амнон: Фамару сестру Авессалома брата моего аз люблю.
5 Yonadab ya ce, “Je gado ka kwanta kamar ba ka da lafiya. Sa’ad da mahaifinka ya zo ganinka, sai ka ce masa, ‘Ina so ƙanuwata Tamar tă kawo mini wani abu in ci. Bari tă shirya abincin a gabana don in ganta, in kuma ci daga hannunta.’”
И рече ему Ионадав: лязи на постели твоей и разболися, и внидет отец твой видети тя, и речеши к нему: да приидет ныне Фамарь сестра моя, и да ми даст ясти, и да сотворит пред очима моима снедь, да увижду и вкушу от рук ея.
6 Sai Amnon ya kwanta sai ka ce yana ciwo. Da sarki ya zo don ganinsa, sai Amnon ya ce, “Zan so ƙanuwata Tamar tă zo tă shirya mini abinci a gabana, don in ci daga hannunta.”
И ляже Амнон и разболеся: и вниде царь видети его. И рече Амнон к царю: да приидет ныне Фамарь сестра моя ко мне и да испечет два пряжма пред очима моима, и имам ясти от руку ея.
7 Dawuda kuwa ya aika wa Tamar a fada, ya ce, “Ki je gidan Amnon ɗan’uwanki, ki yi masa abinci.”
И посла Давид к Фамаре в дом, глаголя: иди ныне в дом Амнона брата твоего и сотвори ему снедь.
8 Saboda haka Tamar ta tafi gidan ɗan’uwanta Amnon, wanda yake kwance. Ta ɗauki fulawa, ta kwaɓa, ta yi burodi a gabansa ta toya shi.
И иде Фамарь в дом Амнона брата своего, и той лежаше. И взя тесто, и смеси, и устрои пред очима его, и испече пряжма:
9 Sa’an nan ta juye a kasko ta ba shi burodin, amma ya ƙi ci. Amnon ya ce, “A sa kowa yă fita daga nan.” Saboda haka kowa ya fita ya bar shi.
и взя сковраду и изложи пред него, и не восхоте ясти. И рече Амнон: изжените вся мужы от мене. И изгнаша вся мужы от него.
10 Sa’an nan Amnon ya ce wa Tamar, “Kawo abincin a nan a cikin ɗakin kwanciyata, don in ci daga hannunki.” Tamar kuwa ta ɗauki burodin da ta toya, ta kawo wa ɗan’uwanta Amnon a ciki ɗakin kwanciyarsa.
И рече Амнон к Фамаре: внеси ми снедь во внутреннюю храмину, и ям от руку твоею. И взя Фамарь пряжма, яже испече, и внесе Амнону брату своему во внутреннюю храмину,
11 Amma da ta kai masa don yă ci, sai ya cafke ta ya ce, “Zo in kwana da ke,’yar’uwata.”
и представи ему да яст. И ят ю, и рече ей: гряди, лязи со мною, сестро моя.
12 Ta ce, “Kada ka yi wannan ɗan’uwana! Kada ka tilasta ni. Bai kamata a yi irin wannan abu a Isra’ila ba! Kada ka yi wannan mugun abu.
И рече ему: ни, брате мой, не обругай мене, понеже не сотворится тако во Израили, не сотвори безумия сего:
13 Ni fa, ina zan sa kaina saboda kunya? Kai kuma za ka zama kamar wani mugun wawa a Isra’ila. Ina roƙonka ka yi wa sarki magana; ba zai hana ni aurenka ba.”
и аз камо скрыю безчестие мое? И ты будеши яко един от безумных во Израили: и ныне глаголи к царю, да не отлучит мене от тебе.
14 Amma Amnon ya ƙi yă saurare ta, da yake ya fi ta ƙarfi, sai ya yi mata fyaɗe.
И не восхоте Амнон послушати гласа ея, и преодоле ей, и смири ю, и преспа с нею.
15 Bayan ya yi lalata da ita sai Amnon ya ƙi ta da mummunan ƙiyayya. Zahiri ya ƙi ta fiye da ya ƙaunace ta. Sai Amnon ya ce mata, “Tashi, ki fita!”
И возненавиде ю Амнон ненавистию великою зело, яко велиим ненавидением возненавиде ю паче любве, еюже любляше ю, и рече ей Амнон: востани и отиди.
16 Ta ce, “A’a! Korina zai fi muni da abin da ka riga ka yi mini.” Amma ya ƙi yă saurare ta.
И рече ему Фамарь: (ни, брате, ) яко злоба болши есть последняя паче первыя, юже сотворил еси со мною, еже отслати мене. И не восхоте Амнон слышати гласа ея.
17 Sai ya kira bawansa ya ce, “Fitar da matan nan daga nan, ka rufe ƙofa.”
И призва отрока своего, приставника дому своего, и рече ему: отсли ныне сию от мене вон, и заключи двери вслед ея.
18 Saboda haka bawansa ya fitar da ita, ya kuma sa aka rufe ƙofa. Tana sanye da doguwar riga mai kayan ado masu tsada, gama wannan ne irin kayan da budurwai’ya’yan sarki mata suke sawa.
И бе риза на ней испещрена, понеже тако облачахуся дщери царевы, сущыя девицы, во одежды своя. И изведе ю вон слуга его и затвори двери вслед ея.
19 Sai Tamar ta zuba toka a kanta, ta kuma yayyage doguwar riga mai kayan adon da take sanye da shi. Ta sa hannunta a kai, ta tafi tana kuka da ƙarfi.
И взя Фамарь пепел, и насыпа на главу свою, и одежду испещренную растерза на себе, и возложи руце свои на главу свою, и идущи идяше и вопияше.
20 Absalom ɗan’uwanta ya ce mata, “Amnon, ɗan’uwanki ya ɓata ki ko? To, ki yi shiru’yar’uwata; ai, ɗan’uwanki ne. Kada wannan abu yă dame ki.” Tamar kuwa ta zauna a gidan ɗan’uwanta Absalom, zaman kaɗaici.
И рече к ней Авессалом брат ея: еда Амнон брат твой бысть с тобою? И ныне, сестро моя, умолчи, яко брат твой есть: не полагай на сердцы твоем еже глаголати слово сие. И седе Фамарь вдовствующи в дому Авессалома брата своего.
21 Da Sarki Dawuda ya ji dukan abin da ya faru, sai ya husata ƙwarai.
И слыша царь Давид вся словеса сия, и разгневася зело, и не опечали духа Амнона сына своего, понеже любляше его, яко первенец бе ему.
22 Absalom kuwa bai yi wa Amnon wata magana ta alheri ko ta mugunta ba; ya ƙi jinin Amnon domin ya ci mutuncin ƙanuwarsa Tamar.
И не глагола Авессалом со Амноном ни о добре, ни о зле, понеже возненавиде Авессалом Амнона того ради, понеже Фамару сестру его обругал.
23 Bayan shekaru biyu, sa’ad da masu askin tumakin Absalom suna Ba’al-Hazor, kusa da iyakar Efraim, sai ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza a can.
И бысть по двух летех дний, и беша стригуще (овцы) Авессаломовы (раби) в Веласоре близ Ефрема: и призва Авессалом вся сыны царевы.
24 Sai Absalom ya je wurin sarki ya ce, “Bawanka ya sa masu askin tumaki sun zo. Ko sarki da fadawansa za su zo tare da ni?”
И прииде Авессалом ко царю и рече: се, ныне стригут рабу твоему, да идет убо царь и отроцы его с рабом твоим.
25 Sarki ya ce, “A’a ɗana, bai kamata dukanmu mu tafi ba; don kada nauyi yă yi maka yawa.” Absalom dai ya dāge, duk da haka sarki ya ƙi yă je, sai dai ya albarkace shi.
И рече царь ко Авессалому: ни, сыне мой, да не пойдем вси мы, и да не отяготим тя. И нуждаше его: и не восхоте (царь) ити, и благослови его.
26 Sa’an nan Absalom ya ce, to, “In ba za ka ba, ina roƙonka bari Amnon ɗan’uwana yă zo tare da mu.” Sarki ya ce masa, “Don me zai tafi tare da kai?”
И рече Авессалом к нему: аще же ни, поне да идет с нами Амнон брат мой. И рече ему царь: почто идет с тобою Амнон?
27 Amma Absalom ya nace don sarki yă yarda, saboda haka sarki ya bar Amnon da sauran’ya’yan sarki maza su tafi tare da shi.
И принуди его Авессалом, и отпусти с ним Амнона и вся сыны царевы. И сотвори Авессалом пир, якоже творит пир царь.
28 Absalom ya umarci mutanensa ya ce, “Ku saurara! Sa’ad da Amnon ya bugu sosai da giya na kuma ce muku, ‘Ku bugi Amnon,’ sai ku kashe shi. Kada ku ji tsoro. Ashe, ba ni ne na ba ku wannan umarni ba? Ku yi ƙarfin hali, ku kuma yi jaruntaka.”
И заповеда Авессалом отроком своим, глаголя: видите егда возблажает сердце Амноне от вина, и реку вам: поразите Амнона, и умертвите его: не убойтеся, яко не аз ли есмь повелеваяй вам? Мужайтеся и будите в сыны силы.
29 Saboda haka mutanen Absalom suka yi wa Amnon abin da Absalom ya umarta. Sai dukan sauran’ya’yan sarki maza suka hau dawakansu suka gudu.
И сотвориша отроцы Авессаломли Амнону, якоже заповеда им Авессалом. И восташа вси сынове царевы, и вседе кийждо на мска своего, и бежаша.
30 Yayinda suke kan hanyarsu, sai labari ya kai kunnen Dawuda cewa, “Absalom ya kashe dukan’ya’yan sarki maza; ko ɗayansu Absalom bai rage ba.”
И бысть, сущым им на пути, и слух дойде до Давида, глаголя: изби Авессалом вся сыны царевы, и не избысть от них ни един.
31 Sai sarki ya tashi, ya yage tufafinsa, ya kuma kwanta a ƙasa; dukan bayinsa kuwa suka tsaya da rigunansu yagaggu.
И воста царь, и растерза ризы своя, и ляже на земли, и вси отроцы его предстоящии ему растерзаша ризы своя.
32 Amma Yonadab, ɗan Shimeya ɗan’uwan Dawuda ya ce, “Kada ranka yă daɗe yă yi tunani cewa an kashe dukan’ya’yan sarki maza; Amnon ne kaɗai ya mutu. Wannan ce niyyar Absalom tun lokacin da Amnon ya yi wa Tamar’yar’uwansa fyaɗe.
И рече Ионадав, сын Самаа брата Давидова, и рече: да не речет господин мой царь, яко вся отроки сыны царевы уби, но Амнон есть един убиен, яко той из уст Авессалому не исхождаше, отнележе обруга сестру его Фамару:
33 Kada mai girma sarki yă damu da jita-jitan nan cewa an kashe dukan’ya’yan sarki maza. Amnon ne kaɗai ya mutu.”
и ныне да не полагает господин мой царь словесе на сердцы своем, глаголя: вси сынове царевы умроша: яко Амнон един умре.
34 Ana cikin haka, sai Absalom ya gudu. To, mutumin da yake tsaro a wannan lokaci ya ɗaga kai sai ya ga mutane da yawa a hanya, yamma da shi, suna gangarowa daga gefen tudu. Sai mai tsaron ya je ya gaya wa sarki cewa, “Na ga mutane ta wajen Horonayim, a gefen tudu.”
И побеже Авессалом. И воздвиже отрок страж очеса своя и виде: и се, людие мнози идуще путем вслед его со страны гор в низхождение. И прииде страж и возвести царю и рече: мужы видех от пути Оронска со страны горы.
35 Yonadab ya ce wa Sarki, “Duba, ga’ya’yan sarki maza sun zo; ya faru kamar dai yadda bawanka ya faɗa.”
И рече Ионадав ко царю: се, сынове царевы приходят: по словеси раба твоего, тако бысть.
36 Yana gama magana, sai ga’ya’yan sarki maza suka shigo suna kuka da ƙarfi. Sarki ma da dukan bayinsa suka yi kuka mai zafi.
И бысть егда сконча глаголя, и се, сынове царевы приидоша и воздвигоша глас свой и плакаша: и сам царь и вси отроцы его плакаша плачем великим зело.
37 Absalom ya gudu ya tafi wurin Talmai ɗan Ammihud, sarkin Geshur. Amma Sarki Dawuda ya yi ta makokin ɗansa kowace rana.
И Авессалом убеже, и прииде ко Фолму сыну Емиуда, царю Гедсурску, в землю Хамаахадску. И плакаше Давид царь о сыне своем вся дни.
38 Bayan Absalom ya gudu sai ya je wurin Geshur, ya zauna a can shekara uku.
И Авессалом убеже, и иде в Гедсур, и бе тамо три лета.
39 Sai zuciyar sarki Dawuda ya komo kan Absalom, gama an yi masa ta’aziyya game da mutuwar Amnon.
И остави царь Давид изыти вслед Авессалома, яко утешися о Амноне, яко умре.

< 2 Sama’ila 13 >