< 2 Sama’ila 13 >

1 Ana nan sai Amnon ɗan Dawuda ya fara son Tamar, kyakkyawar’yar’uwar Absalom ɗan Dawuda.
و بعد از این، واقع شد که ابشالوم بن داود را خواهری نیکو صورت مسمی به تامار بود، و امنون، پسر داود، او را دوست می‌داشت.۱
2 Amnon ya matsu ƙwarai har abin ya sa shi ciwo saboda ƙanuwarsa Tamar. Ya gane zai zama da wuya yă sadu da Tamar ita kaɗai, gama ba ta taɓa kwana da namiji ba.
و امنون به‌سبب خواهر خود تامارچنان گرفتار شد که بیمار گشت، زیرا که او باکره بود و به نظر امنون دشوار آمد که با وی کاری کند.۲
3 To, Amnon yana da wani aboki mai suna Yonadab, ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda. Yonadab dai mai wayo ne ƙwarai.
و امنون رفیقی داشت که مسمی به یوناداب بن شمعی، برادر داود، بود، و یوناداب مردی بسیارزیرک بود.۳
4 Ya tambayi Amnon ya ce, “Don me kowace safiya fuskarka a ɓace take? Kai ba yaron sarki ba ne? Faɗa mini, me ke faruwa?” Amnon ya ce masa, “Ina son Tamar ƙanuwar wan nawa Absalom ne.”
و او وی را گفت: «ای پسر پادشاه چرا روز به روز چنین لاغر می‌شوی و مرا خبرنمی دهی؟» امنون وی را گفت که «من تامار، خواهر برادر خود، ابشالوم را دوست می‌دارم.»۴
5 Yonadab ya ce, “Je gado ka kwanta kamar ba ka da lafiya. Sa’ad da mahaifinka ya zo ganinka, sai ka ce masa, ‘Ina so ƙanuwata Tamar tă kawo mini wani abu in ci. Bari tă shirya abincin a gabana don in ganta, in kuma ci daga hannunta.’”
و یوناداب وی را گفت: «بر بستر خود خوابیده، تمارض نما و چون پدرت برای عیادت تو بیاید، وی را بگو: تمنا این که خواهر من تامار بیاید و مراخوراک بخوراند و خوراک را در نظر من حاضرسازد تا ببینم و از دست وی بخورم.»۵
6 Sai Amnon ya kwanta sai ka ce yana ciwo. Da sarki ya zo don ganinsa, sai Amnon ya ce, “Zan so ƙanuwata Tamar tă zo tă shirya mini abinci a gabana, don in ci daga hannunta.”
پس امنون خوابید و تمارض نمود و چون پادشاه به عیادتش آمد، امنون به پادشاه گفت: «تمنا اینکه خواهرم تامار بیاید و دو قرص طعام پیش من بپزد تا ازدست او بخورم.»۶
7 Dawuda kuwa ya aika wa Tamar a fada, ya ce, “Ki je gidan Amnon ɗan’uwanki, ki yi masa abinci.”
و داود نزد تامار به خانه‌اش فرستاده، گفت: «الان به خانه برادرت امنون برو و برایش طعام بساز.»۷
8 Saboda haka Tamar ta tafi gidan ɗan’uwanta Amnon, wanda yake kwance. Ta ɗauki fulawa, ta kwaɓa, ta yi burodi a gabansa ta toya shi.
و تامار به خانه برادر خود، امنون، رفت. واو خوابیده بود. و آرد گرفته، خمیر کرد، و پیش اوقرصها ساخته، آنها را پخت.۸
9 Sa’an nan ta juye a kasko ta ba shi burodin, amma ya ƙi ci. Amnon ya ce, “A sa kowa yă fita daga nan.” Saboda haka kowa ya fita ya bar shi.
و تابه را گرفته، آنها را پیش او ریخت. اما از خوردن ابا نمود وگفت: «همه کس را از نزد من بیرون کنید.» وهمگان از نزد او بیرون رفتند.۹
10 Sa’an nan Amnon ya ce wa Tamar, “Kawo abincin a nan a cikin ɗakin kwanciyata, don in ci daga hannunki.” Tamar kuwa ta ɗauki burodin da ta toya, ta kawo wa ɗan’uwanta Amnon a ciki ɗakin kwanciyarsa.
و امنون به تامارگفت: «خوراک را به اطاق بیاور تا از دست توبخورم.» و تامار قرصها را که ساخته بود، گرفته، نزد برادر خود، امنون، به اطاق آورد.۱۰
11 Amma da ta kai masa don yă ci, sai ya cafke ta ya ce, “Zo in kwana da ke,’yar’uwata.”
و چون پیش او گذاشت تا بخورد، او وی را گرفته، به اوگفت: «ای خواهرم بیا با من بخواب.»۱۱
12 Ta ce, “Kada ka yi wannan ɗan’uwana! Kada ka tilasta ni. Bai kamata a yi irin wannan abu a Isra’ila ba! Kada ka yi wannan mugun abu.
او وی راگفت: «نی‌ای برادرم، مرا ذلیل نساز زیرا که چنین کار در اسرائیل کرده نشود، این قباحت را به عمل میاور.۱۲
13 Ni fa, ina zan sa kaina saboda kunya? Kai kuma za ka zama kamar wani mugun wawa a Isra’ila. Ina roƙonka ka yi wa sarki magana; ba zai hana ni aurenka ba.”
اما من کجا ننگ خود را ببرم و اما تو مثل یکی از سفها در اسرائیل خواهی شد، پس حال تمنا اینکه به پادشاه بگویی، زیرا که مرا از تو دریغ نخواهد نمود.»۱۳
14 Amma Amnon ya ƙi yă saurare ta, da yake ya fi ta ƙarfi, sai ya yi mata fyaɗe.
لیکن او نخواست سخن وی رابشنود، و بر او زورآور شده، او را مجبور ساخت و با او خوابید.۱۴
15 Bayan ya yi lalata da ita sai Amnon ya ƙi ta da mummunan ƙiyayya. Zahiri ya ƙi ta fiye da ya ƙaunace ta. Sai Amnon ya ce mata, “Tashi, ki fita!”
آنگاه امنون با شدت بر وی بغض نمود، وبغضی که با او ورزید از محبتی که با وی می داشت، زیاده بود، پس امنون وی را گفت: «برخیز و برو.»۱۵
16 Ta ce, “A’a! Korina zai fi muni da abin da ka riga ka yi mini.” Amma ya ƙi yă saurare ta.
او وی را گفت: «چنین مکن. زیرا این ظلم عظیم که در بیرون کردن من می‌کنی، بدتر است از آن دیگری که با من کردی.» لیکن اونخواست که وی را بشنود.۱۶
17 Sai ya kira bawansa ya ce, “Fitar da matan nan daga nan, ka rufe ƙofa.”
پس خادمی را که اورا خدمت می‌کرد خوانده، گفت: «این دختر را ازنزد من بیرون کن و در را از عقبش ببند.»۱۷
18 Saboda haka bawansa ya fitar da ita, ya kuma sa aka rufe ƙofa. Tana sanye da doguwar riga mai kayan ado masu tsada, gama wannan ne irin kayan da budurwai’ya’yan sarki mata suke sawa.
و اوجامه رنگارنگ دربر داشت زیرا که دختران باکره پادشاه به این‌گونه لباس، ملبس می‌شدند. وخادمش او را بیرون کرده، در را از عقبش بست.۱۸
19 Sai Tamar ta zuba toka a kanta, ta kuma yayyage doguwar riga mai kayan adon da take sanye da shi. Ta sa hannunta a kai, ta tafi tana kuka da ƙarfi.
و تامار خاکستر بر سر خود ریخته، و جامه رنگارنگ که در برش بود، دریده، و دست خود رابر سر گذارده، روانه شد. و چون می‌رفت، فریادمی نمود.۱۹
20 Absalom ɗan’uwanta ya ce mata, “Amnon, ɗan’uwanki ya ɓata ki ko? To, ki yi shiru’yar’uwata; ai, ɗan’uwanki ne. Kada wannan abu yă dame ki.” Tamar kuwa ta zauna a gidan ɗan’uwanta Absalom, zaman kaɗaici.
و برادرش، ابشالوم، وی را گفت: «که آیابرادرت، امنون، با تو بوده است؟ پس‌ای خواهرم اکنون خاموش باش. او برادر توست و از این کارمتفکر مباش.» پس تامار در خانه برادر خود، ابشالوم، در پریشان حالی ماند.۲۰
21 Da Sarki Dawuda ya ji dukan abin da ya faru, sai ya husata ƙwarai.
و چون داودپادشاه تمامی این وقایع را شنید، بسیار غضبناک شد.۲۱
22 Absalom kuwa bai yi wa Amnon wata magana ta alheri ko ta mugunta ba; ya ƙi jinin Amnon domin ya ci mutuncin ƙanuwarsa Tamar.
و ابشالوم به امنون سخنی نیک یا بدنگفت، زیرا که ابشالوم امنون را بغض می‌داشت، به علت اینکه خواهرش تامار را ذلیل ساخته بود.۲۲
23 Bayan shekaru biyu, sa’ad da masu askin tumakin Absalom suna Ba’al-Hazor, kusa da iyakar Efraim, sai ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza a can.
و بعد از دو سال تمام، واقع شد که ابشالوم در بعل حاصور که نزد افرایم است، پشم برندگان داشت. و ابشالوم تمامی پسران پادشاه را دعوت نمود.۲۳
24 Sai Absalom ya je wurin sarki ya ce, “Bawanka ya sa masu askin tumaki sun zo. Ko sarki da fadawansa za su zo tare da ni?”
و ابشالوم نزد پادشاه آمده، گفت: «اینک حال، بنده تو، پشم برندگان دارد. تمنا اینکه پادشاه با خادمان خود همراه بنده ات بیایند.»۲۴
25 Sarki ya ce, “A’a ɗana, bai kamata dukanmu mu tafi ba; don kada nauyi yă yi maka yawa.” Absalom dai ya dāge, duk da haka sarki ya ƙi yă je, sai dai ya albarkace shi.
پادشاه به ابشالوم گفت: «نی‌ای پسرم، همه ما نخواهیم آمد مبادا برای تو بار سنگین باشیم.» وهر‌چند او را الحاح نمود لیکن نخواست که بیایدو او را برکت داد.۲۵
26 Sa’an nan Absalom ya ce, to, “In ba za ka ba, ina roƙonka bari Amnon ɗan’uwana yă zo tare da mu.” Sarki ya ce masa, “Don me zai tafi tare da kai?”
و ابشالوم گفت: «پس تمنااینکه برادرم، امنون، با ما بیاید.» پادشاه او را گفت: «چرا با تو بیاید؟»۲۶
27 Amma Absalom ya nace don sarki yă yarda, saboda haka sarki ya bar Amnon da sauran’ya’yan sarki maza su tafi tare da shi.
اما چون ابشالوم او را الحاح نمود، امنون و تمامی پسران پادشاه را با او روانه کرد.۲۷
28 Absalom ya umarci mutanensa ya ce, “Ku saurara! Sa’ad da Amnon ya bugu sosai da giya na kuma ce muku, ‘Ku bugi Amnon,’ sai ku kashe shi. Kada ku ji tsoro. Ashe, ba ni ne na ba ku wannan umarni ba? Ku yi ƙarfin hali, ku kuma yi jaruntaka.”
و ابشالوم خادمان خود را امر فرموده، گفت: «ملاحظه کنید که چون دل امنون از شراب خوش شود، و به شما بگویم که امنون را بزنید. آنگاه او را بکشید، و مترسید، آیا من شما را امرنفرمودم. پس دلیر و شجاع باشید.»۲۸
29 Saboda haka mutanen Absalom suka yi wa Amnon abin da Absalom ya umarta. Sai dukan sauran’ya’yan sarki maza suka hau dawakansu suka gudu.
و خادمان ابشالوم با امنون به طوری که ابشالوم امر فرموده بود، به عمل آوردند، و جمیع پسران پادشاه برخاسته، هر کس به قاطر خود سوار شده، گریختند.۲۹
30 Yayinda suke kan hanyarsu, sai labari ya kai kunnen Dawuda cewa, “Absalom ya kashe dukan’ya’yan sarki maza; ko ɗayansu Absalom bai rage ba.”
و چون ایشان در راه می‌بودند، خبر به داودرسانیده، گفتند که «ابشالوم همه پسران پادشاه راکشته و یکی از ایشان باقی نمانده است.»۳۰
31 Sai sarki ya tashi, ya yage tufafinsa, ya kuma kwanta a ƙasa; dukan bayinsa kuwa suka tsaya da rigunansu yagaggu.
پس پادشاه برخاسته، جامه خود را درید و به روی زمین دراز شد و جمیع بندگانش با جامه دریده دراطرافش ایستاده بودند.۳۱
32 Amma Yonadab, ɗan Shimeya ɗan’uwan Dawuda ya ce, “Kada ranka yă daɗe yă yi tunani cewa an kashe dukan’ya’yan sarki maza; Amnon ne kaɗai ya mutu. Wannan ce niyyar Absalom tun lokacin da Amnon ya yi wa Tamar’yar’uwansa fyaɗe.
اما یوناداب بن شمعی برادر داود متوجه شده، گفت: «آقایم گمان نبرد که جمیع جوانان، یعنی پسران پادشاه کشته شده‌اند، زیرا که امنون تنها مرده است چونکه این، نزدابشالوم مقرر شده بود از روزی که خواهرش تاماررا ذلیل ساخته بود.۳۲
33 Kada mai girma sarki yă damu da jita-jitan nan cewa an kashe dukan’ya’yan sarki maza. Amnon ne kaɗai ya mutu.”
و الان آقایم، پادشاه از این امر متفکر نشود، و خیال نکند که تمامی پسران پادشاه مرده‌اند زیرا که امنون تنها مرده است.»۳۳
34 Ana cikin haka, sai Absalom ya gudu. To, mutumin da yake tsaro a wannan lokaci ya ɗaga kai sai ya ga mutane da yawa a hanya, yamma da shi, suna gangarowa daga gefen tudu. Sai mai tsaron ya je ya gaya wa sarki cewa, “Na ga mutane ta wajen Horonayim, a gefen tudu.”
و ابشالوم گریخت، و جوانی که دیده بانی می‌کرد، چشمان خود را بلند کرده، نگاه کرد و اینک خلق بسیاری از پهلوی کوه که در عقبش بود، می‌آمدند.۳۴
35 Yonadab ya ce wa Sarki, “Duba, ga’ya’yan sarki maza sun zo; ya faru kamar dai yadda bawanka ya faɗa.”
و یوناداب به پادشاه گفت: «اینک پسران پادشاه می‌آیند، پس به طوری که بنده ات گفت، چنان شد.»۳۵
36 Yana gama magana, sai ga’ya’yan sarki maza suka shigo suna kuka da ƙarfi. Sarki ma da dukan bayinsa suka yi kuka mai zafi.
و چون از سخن‌گفتن فارغ شد، اینک پسران پادشاه رسیدند و آوازخود را بلند کرده، گریستند، و پادشاه نیز و جمیع خادمانش به آواز بسیار بلند گریه کردند.۳۶
37 Absalom ya gudu ya tafi wurin Talmai ɗan Ammihud, sarkin Geshur. Amma Sarki Dawuda ya yi ta makokin ɗansa kowace rana.
و ابشالوم فرار کرده، نزد تلمای ابن عمیهود، پادشاه جشور رفت، و داود برای پسرخود هر روز نوحه گری می‌نمود.۳۷
38 Bayan Absalom ya gudu sai ya je wurin Geshur, ya zauna a can shekara uku.
و ابشالوم فرار کرده، به جشور رفت و سه سال در آنجا ماند.۳۸
39 Sai zuciyar sarki Dawuda ya komo kan Absalom, gama an yi masa ta’aziyya game da mutuwar Amnon.
و داود آرزو می‌داشت که نزد ابشالوم بیرون رود، زیرا درباره امنون تسلی یافته بود، چونکه مرده بود.۳۹

< 2 Sama’ila 13 >