< 2 Sama’ila 13 >
1 Ana nan sai Amnon ɗan Dawuda ya fara son Tamar, kyakkyawar’yar’uwar Absalom ɗan Dawuda.
And it came to pass after this, that Amnon the son of David loved the sister of Absalom the son of David, who was very beautiful, and her name was Thamar.
2 Amnon ya matsu ƙwarai har abin ya sa shi ciwo saboda ƙanuwarsa Tamar. Ya gane zai zama da wuya yă sadu da Tamar ita kaɗai, gama ba ta taɓa kwana da namiji ba.
And he was exceedingly fond of her, so that he fell sick for the love of her: for as she was a virgin, he thought it hard to do any thing dishonestly with her.
3 To, Amnon yana da wani aboki mai suna Yonadab, ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda. Yonadab dai mai wayo ne ƙwarai.
Now Amnon had a friend, named Jonadab the son of Semmaa the brother of David, a very wise man:
4 Ya tambayi Amnon ya ce, “Don me kowace safiya fuskarka a ɓace take? Kai ba yaron sarki ba ne? Faɗa mini, me ke faruwa?” Amnon ya ce masa, “Ina son Tamar ƙanuwar wan nawa Absalom ne.”
And he said to him: Why dost thou grow so lean from day to day, O son of the king? why dost thou not tell me the reason of it? And Amnon said to him: I am in love with Thamar the sister of my brother Absalom.
5 Yonadab ya ce, “Je gado ka kwanta kamar ba ka da lafiya. Sa’ad da mahaifinka ya zo ganinka, sai ka ce masa, ‘Ina so ƙanuwata Tamar tă kawo mini wani abu in ci. Bari tă shirya abincin a gabana don in ganta, in kuma ci daga hannunta.’”
And Jonadab said to him: Lie down upon thy bed, and feign thyself sick: and when thy father shall come to visit thee, say to him: Let my sister Thamar, I pray thee, come to me, to give me to eat, and to make me a mess, that I may eat it at her hand.
6 Sai Amnon ya kwanta sai ka ce yana ciwo. Da sarki ya zo don ganinsa, sai Amnon ya ce, “Zan so ƙanuwata Tamar tă zo tă shirya mini abinci a gabana, don in ci daga hannunta.”
So Amnon lay down, and made as if he were sick: and when the king came to visit him, Amnon said to the king: I pray thee let my sister Thamar come, and make in my sight two little messes, that I may eat at her hand.
7 Dawuda kuwa ya aika wa Tamar a fada, ya ce, “Ki je gidan Amnon ɗan’uwanki, ki yi masa abinci.”
Then David sent home to Thamar, saying: Come to the house of thy brother Amnon, and make him a mess.
8 Saboda haka Tamar ta tafi gidan ɗan’uwanta Amnon, wanda yake kwance. Ta ɗauki fulawa, ta kwaɓa, ta yi burodi a gabansa ta toya shi.
And Thamar came to the house of Amnon her brother: but he was laid down: and she took meal and tempered it: and dissolving it in his sight she made little messes.
9 Sa’an nan ta juye a kasko ta ba shi burodin, amma ya ƙi ci. Amnon ya ce, “A sa kowa yă fita daga nan.” Saboda haka kowa ya fita ya bar shi.
And taking what she had boiled, she poured it out, and set it before him, but he would not eat: and Amnon said: Put out all persons from me. And when they had put all persons out,
10 Sa’an nan Amnon ya ce wa Tamar, “Kawo abincin a nan a cikin ɗakin kwanciyata, don in ci daga hannunki.” Tamar kuwa ta ɗauki burodin da ta toya, ta kawo wa ɗan’uwanta Amnon a ciki ɗakin kwanciyarsa.
Amnon said to Thamar: Bring the mess into the chamber, that I may eat at thy hand. And Thamar took the little messes which she had made, and brought them in to her brother Amnon in the chamber.
11 Amma da ta kai masa don yă ci, sai ya cafke ta ya ce, “Zo in kwana da ke,’yar’uwata.”
And when she had presented him the meat, he took hold of her, and said: Come lie with me, my sister.
12 Ta ce, “Kada ka yi wannan ɗan’uwana! Kada ka tilasta ni. Bai kamata a yi irin wannan abu a Isra’ila ba! Kada ka yi wannan mugun abu.
She answered him: Do not so, my brother, do not force me: for no such thing must be done in Israel. Do not thou this folly.
13 Ni fa, ina zan sa kaina saboda kunya? Kai kuma za ka zama kamar wani mugun wawa a Isra’ila. Ina roƙonka ka yi wa sarki magana; ba zai hana ni aurenka ba.”
For I shall not be able to bear my shame, and thou shalt be as one of the fools in Israel: but rather speak to the king, and he will not deny me to thee.
14 Amma Amnon ya ƙi yă saurare ta, da yake ya fi ta ƙarfi, sai ya yi mata fyaɗe.
But he would not hearken to her prayers, but being stronger overpowered her and lay with her.
15 Bayan ya yi lalata da ita sai Amnon ya ƙi ta da mummunan ƙiyayya. Zahiri ya ƙi ta fiye da ya ƙaunace ta. Sai Amnon ya ce mata, “Tashi, ki fita!”
Then Amnon hated her with an exceeding great hatred: so that the hatred wherewith he hated her was greater than the love with which he had loved her before, And Amnon said to her: Arise, and get thee gone.
16 Ta ce, “A’a! Korina zai fi muni da abin da ka riga ka yi mini.” Amma ya ƙi yă saurare ta.
She answered him: This evil which now thou dost against me, in driving me away, is greater than that which thou didst before. And he would not hearken to her:
17 Sai ya kira bawansa ya ce, “Fitar da matan nan daga nan, ka rufe ƙofa.”
But calling the servants that ministered to him, he said: Thrust this woman out from me: and shut the door after her.
18 Saboda haka bawansa ya fitar da ita, ya kuma sa aka rufe ƙofa. Tana sanye da doguwar riga mai kayan ado masu tsada, gama wannan ne irin kayan da budurwai’ya’yan sarki mata suke sawa.
And she was clothed with along robe: for the king’s daughters that were virgins, used such kind of garments. Then his servant thrust her out: and shut the door after her.
19 Sai Tamar ta zuba toka a kanta, ta kuma yayyage doguwar riga mai kayan adon da take sanye da shi. Ta sa hannunta a kai, ta tafi tana kuka da ƙarfi.
And she put ashes on her head, and rent her long robe and laid her hands upon her head, and went on crying.
20 Absalom ɗan’uwanta ya ce mata, “Amnon, ɗan’uwanki ya ɓata ki ko? To, ki yi shiru’yar’uwata; ai, ɗan’uwanki ne. Kada wannan abu yă dame ki.” Tamar kuwa ta zauna a gidan ɗan’uwanta Absalom, zaman kaɗaici.
And Absalom her brother said to her: Hath thy brother Amnon lain with thee? but now, sister, hold thy peace, he is thy brother: and afflict not thy heart for this thing. So Thamar remained pining away in the house of Absalom her brother.
21 Da Sarki Dawuda ya ji dukan abin da ya faru, sai ya husata ƙwarai.
And when king David heard of these things he was exceedingly grieved: and he would not afflict the spirit of his son Amnon, for he loved him, because he was his firstborn.
22 Absalom kuwa bai yi wa Amnon wata magana ta alheri ko ta mugunta ba; ya ƙi jinin Amnon domin ya ci mutuncin ƙanuwarsa Tamar.
But Absalom spoke not to Amnon neither good nor evil: for Absalom hated Amnon because he had ravished his sister Thamar.
23 Bayan shekaru biyu, sa’ad da masu askin tumakin Absalom suna Ba’al-Hazor, kusa da iyakar Efraim, sai ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza a can.
And it came to pass after two years, that the sheep of Absalom were shorn in Baalhasor, which is near Ephraim: and Absalom invited all the king’s sons:
24 Sai Absalom ya je wurin sarki ya ce, “Bawanka ya sa masu askin tumaki sun zo. Ko sarki da fadawansa za su zo tare da ni?”
And he came to the king, and said to him: Behold thy servant’s sheep are shorn. Let the king, I pray, with his servants come to his servant.
25 Sarki ya ce, “A’a ɗana, bai kamata dukanmu mu tafi ba; don kada nauyi yă yi maka yawa.” Absalom dai ya dāge, duk da haka sarki ya ƙi yă je, sai dai ya albarkace shi.
And the king said to Absalom: Nay, my son, do not ask that we should all come, and be chargeable to thee. And when he pressed him, and he would not go, he blessed him.
26 Sa’an nan Absalom ya ce, to, “In ba za ka ba, ina roƙonka bari Amnon ɗan’uwana yă zo tare da mu.” Sarki ya ce masa, “Don me zai tafi tare da kai?”
And Absalom said: If thou wilt not come, at least let my brother Amnon, I beseech thee, come with us. And the king said to him: It is not necessary that he should go with thee.
27 Amma Absalom ya nace don sarki yă yarda, saboda haka sarki ya bar Amnon da sauran’ya’yan sarki maza su tafi tare da shi.
But Absalom pressed him, so that he let Amnon and all the king’s sons go with him. And Absalom made a feast as it were the feast of a king.
28 Absalom ya umarci mutanensa ya ce, “Ku saurara! Sa’ad da Amnon ya bugu sosai da giya na kuma ce muku, ‘Ku bugi Amnon,’ sai ku kashe shi. Kada ku ji tsoro. Ashe, ba ni ne na ba ku wannan umarni ba? Ku yi ƙarfin hali, ku kuma yi jaruntaka.”
And Absalom had commanded his servants, saying: Take notice when Amnon shall be drunk with wine, and when I shall say to you: Strike him, and kill him, fear not: for it is I that command you: take courage, and be valiant men.
29 Saboda haka mutanen Absalom suka yi wa Amnon abin da Absalom ya umarta. Sai dukan sauran’ya’yan sarki maza suka hau dawakansu suka gudu.
And the servants of Absalom did to Amnon as Absalom had commanded them. And all the king’s sons arose and got up every man upon his mule, and fled.
30 Yayinda suke kan hanyarsu, sai labari ya kai kunnen Dawuda cewa, “Absalom ya kashe dukan’ya’yan sarki maza; ko ɗayansu Absalom bai rage ba.”
And while they were yet in the way, a rumour came to David, saying: Absalom hath slain all the king’s sons, and there is not one of them left.
31 Sai sarki ya tashi, ya yage tufafinsa, ya kuma kwanta a ƙasa; dukan bayinsa kuwa suka tsaya da rigunansu yagaggu.
Then the king rose up, and rent his garments: and fell upon the ground, and all his servants, that stood about him, rent their garments.
32 Amma Yonadab, ɗan Shimeya ɗan’uwan Dawuda ya ce, “Kada ranka yă daɗe yă yi tunani cewa an kashe dukan’ya’yan sarki maza; Amnon ne kaɗai ya mutu. Wannan ce niyyar Absalom tun lokacin da Amnon ya yi wa Tamar’yar’uwansa fyaɗe.
But Jonadab the son of Semmaa David’s brother answering, said: Let not my lord the king think that all the king’s sons are slain: Amnon only is dead, for he was appointed by the mouth of Absalom from the day that he ravished his sister Thamar.
33 Kada mai girma sarki yă damu da jita-jitan nan cewa an kashe dukan’ya’yan sarki maza. Amnon ne kaɗai ya mutu.”
Now therefore let not my lord the king take this thing into his heart, saying: All the king’s sons are slain: for Amnon only is dead.
34 Ana cikin haka, sai Absalom ya gudu. To, mutumin da yake tsaro a wannan lokaci ya ɗaga kai sai ya ga mutane da yawa a hanya, yamma da shi, suna gangarowa daga gefen tudu. Sai mai tsaron ya je ya gaya wa sarki cewa, “Na ga mutane ta wajen Horonayim, a gefen tudu.”
But Absalom fled away: and the young man that kept the watch, lifted up his eyes and looked, and behold there came much people by a by-way on the side of the mountain.
35 Yonadab ya ce wa Sarki, “Duba, ga’ya’yan sarki maza sun zo; ya faru kamar dai yadda bawanka ya faɗa.”
And Jonadab said to the king: Behold the king’s sons are come: as thy servant said, so it is.
36 Yana gama magana, sai ga’ya’yan sarki maza suka shigo suna kuka da ƙarfi. Sarki ma da dukan bayinsa suka yi kuka mai zafi.
And when he made an end of speaking, the king’s sons also appeared: and coming in they lifted up their voice, and wept: and the king also and all his servants wept very much.
37 Absalom ya gudu ya tafi wurin Talmai ɗan Ammihud, sarkin Geshur. Amma Sarki Dawuda ya yi ta makokin ɗansa kowace rana.
But Absalom fled, and went to Tholomai the son of Ammiud the king of Gessur. And David mourned for his son every day.
38 Bayan Absalom ya gudu sai ya je wurin Geshur, ya zauna a can shekara uku.
And Absalom after he was fled, and come into Gessur, was there three years.
39 Sai zuciyar sarki Dawuda ya komo kan Absalom, gama an yi masa ta’aziyya game da mutuwar Amnon.
And king David ceased to pursue after Absalom, because he was comforted concerning the death of Amnon.