< 2 Sama’ila 12 >
1 Ubangiji ya aiki Natan wurin Dawuda. Da ya tafi wajensa, sai ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu a wani gari, ɗaya mai arziki, ɗayan kuma matalauci.
Gospod je k Davidu poslal Natána. Ta je prišel k njemu in mu rekel: »Bila sta dva moža v enem mestu; eden bogat, drugi pa reven.
2 Mai arzikin yana da babban garken tumaki, da kuma shanu,
Bogat človek je imel silno mnogo tropov in čred,
3 amma matalauci ba shi da kome sai’yar tunkiyar da ya sayo. Ya yi kiwonta, ta kuwa yi girma tare shi da yaransa. Takan ci tare da shi ta sha ruwa a kwaf nasa, har ma ta kwanta a ƙirjinsa. Ta ma zama kamar’ya a gare shi.
toda reven človek ni imel ničesar, razen ene majhne ovčje jagnjice, ki jo je kupil in jo preživljal. Ta je zrasla skupaj z njim in z njegovimi otroki; jedla je od njegove lastne hrane, pila iz njegove lastne čaše, ležala v njegovem naročju in mu je bila kakor hči.
4 “To, sai ga wani baƙo ya zo wurin mai arzikin nan, amma mai arzikin ya ƙi yă kama tunkiyarsa, ko saniyarsa yă yanka don yă shirya wa baƙon da ya zo abinci. A maimako, sai ya je ya kama’yar tunkiyan nan ta matalaucin ya yanka ya shirya wa mutumin da ya zo masa.”
K bogatašu pa je prišel popotnik in žal mu je bilo vzeti od svojega lastnega tropa in od svoje lastne črede, da pripravi za popotnika, ki je prišel k njemu, temveč je vzel reveževo jagnje in to pripravil za človeka, ki je prišel k njemu.«
5 Dawuda ya husata ƙwarai da mutumin, ya ce wa Natan, “Muddin Ubangiji yana a raye, mutumin da ya yi wannan ya cancanci yă mutu!
Davidova jeza je bila silno vžgana zoper tega moža in Natánu je rekel: » Kakor Gospod živi, mož, ki je storil to stvar, bo zagotovo umrl
6 Dole yă biya diyyar tunkiyan nan sau huɗu, domin ya aikata haka ba tausayi.”
in četverno bo povrnil jagnje, ker je storil to stvar in ker ni imel usmiljenja.«
7 Sai Natan ya ce wa Dawuda, “Kai ne mutumin! Ga abin da Ubangiji, Allah ya ce, ‘Na naɗa ka sarki bisa Isra’ila, na kuma cece ka daga hannun Shawulu.
Natán je rekel Davidu: »Ti si ta človek. Tako govori Gospod, Izraelov Bog: ›Mazilil sem te [za] kralja nad Izraelom in te osvobodil iz Savlove roke.
8 Na ba ka gidan maigidanka, da matan maigidanka duka. Na ba ka gidan Isra’ila da Yahuda. Da a ce dukan waɗannan sun kāsa maka, ai, da na ƙara maka.
Dal sem ti hišo tvojega gospodarja in v tvoje naročje žene tvojega gospodarja in dal sem ti Izraelovo in Judovo hišo. Če bi bilo to premalo, bi ti dodal še več takšnih in takšnih stvari.
9 Me ya sa ka rena maganar Ubangiji ta wurin yin mugunta haka a idonsa? Ka kashe Uriya mutumin Hitti da takobi, ka kuma ɗauki matarsa tă zama matarka. Ka kashe shi da takobin Ammonawa.
Zakaj si preziral Gospodovo zapoved, da si storil zlo v njegovem pogledu? Hetejca Urijája si ubil z mečem in njegovo ženo vzel, da postane tvoja žena, njega pa si umoril z mečem Amónovih otrok.
10 To, fa, takobi ba zai taɓa rabu da gidanka ba, domin ka rena ni, ka kuma ƙwace matar Uriya mutumin Hitti ta zama matarka.’
Zdaj torej meč ne bo nikoli odšel od tvoje hiše, ker si me preziral in si vzel ženo Hetejca Urijája, da bi bila tvoja žena.‹
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Daga cikin iyalinka zan kawo masifa a kanka. A idanunka zan ɗauki matanka in ba wa wani da yake kusa da kai, zai kuwa kwana da su da rana tsaka.
Tako govori Gospod: ›Glej, zoper tebe bom vzdignil zlo iz tvoje lastne hiše in pred tvojimi očmi bom vzel tvoje žene in jih dal tvojemu bližnjemu in ta bo ležal s tvojimi ženami v pogledu tega sonca.
12 Ka aikata wannan a ɓoye, amma zan aikata wannan da rana tsaka, a gaban dukan Isra’ila.’”
Kajti ti si to delal naskrivaj, toda jaz bom to stvar storil pred vsem Izraelom in pred soncem.‹«
13 Sai Dawuda ya ce wa Natan, “Na yi wa Ubangiji zunubi.” Natan ya ce, “Ubangiji ya yafe maka zunubin. Ba za ka mutu ba.
David je rekel Natánu: »Grešil sem zoper Gospoda.« Natán je rekel Davidu: » Gospod je tudi odstranil tvoj greh; ne boš umrl.
14 Amma saboda ka yi haka ka sa abokan gāba suka rena Ubangiji, yaron da aka haifa maka zai mutu.”
Vendar ker si s tem dejanjem dal Gospodovim sovražnikom veliko priložnost, da izrekajo bogokletje, bo tudi otrok, ki ti je rojen, zagotovo umrl.«
15 Bayan Natan ya tafi gida, sai Ubangiji ya bugi yaron da matar Uriya ta haifa wa Dawuda, ya kuwa kamu da ciwo.
In Natán je odšel od njegove hiše. Gospod pa je udaril otroka, ki ga je Urijájeva žena rodila Davidu in ta je bil zelo bolan.
16 Dawuda ya roƙi Allah saboda yaron. Ya yi azumi, ya kuma shiga gidansa ya kwana kwance a ƙasa.
David je zato rotil Boga za otroka in David se je postil in vstopil ter vso noč ležal na zemlji.
17 Dattawan iyalinsa suka tsaya kusa da shi don su ɗaga shi daga ƙasa, amma ya ƙi, bai kuwa ci wani abu tare da su ba.
Starešine njegove hiše so vstali in odšli k njemu, da ga vzdignejo z zemlje, toda ni hotel niti ni z njimi jedel kruha.
18 A rana ta bakwai sai yaron ya rasu. Barorin Dawuda suka ji tsoro su gaya masa cewa yaron ya mutu, gama sun yi tunani cewa, “Yayinda yaron yake da rai, mun yi magana da Dawuda bai ji mu ba. Yaya za mu gaya masa yaron ya mutu? Ai, zai yi wa kansa ɓarna.”
Pripetilo se je na sedmi dan, da je otrok umrl. Davidovi služabniki pa so se mu bali povedati, da je bil otrok mrtev, kajti rekli so: »Glej, medtem ko je bil otrok še živ, smo mu govorili, pa ni hotel poslušati našega glasu. Kako bo torej žalostil samega sebe, če mu povemo, da je otrok mrtev?«
19 Dawuda ya gane bayinsa suna wa juna raɗan wani abu, sai ya gane yaron ya mutu. Sai ya ce, “Yaron ya rasu ko?” Suka ce, “I, ya rasu.”
Toda ko je David videl, da so njegovi služabniki šepetali, je David zaznal, da je bil otrok mrtev. Zato je David rekel svojim služabnikom: »Je otrok mrtev?« Rekli so: »Mrtev je.«
20 Sa’an nan Dawuda ya tashi daga ƙasa. Bayan ya yi wanka, ya shafa mai, ya kuma canja rigunarsa, sa’an nan ya shiga gidan Ubangiji ya yi sujada. Sai ya tafi gidansa, ya nemi a ba shi abinci, aka ba shi, ya kuwa ci.
Potem se je David vzdignil z zemlje, se umil, mazilil, zamenjal svojo obleko, prišel v Gospodovo hišo in oboževal. Potem je prišel v svojo lastno hišo; in ko je zahteval, so predenj postavili kruh in je jedel.
21 Barorinsa suka ce masa, “Me ya sa kake yin haka? Yayinda yaron yake da rai, ka yi azumi, ka kuma yi kuka, amma yanzu da yaron ya mutu, ka tashi, ka kuma ci abinci!”
Potem so mu njegovi služabniki rekli: »Kakšna stvar je ta, ki si jo storil? Postil si se in jokal zaradi otroka, medtem ko je bil živ, toda ko je bil otrok mrtev, si vstal in jedel kruh.«
22 Ya ce musu, “Yayinda yaron yake da rai, na yi azumi, na kuma yi kuka. Na yi tunani na ce, ‘Wa ya sani? Ko Ubangiji zai yi mini alheri yă bar yaron yă rayu.’
Rekel je: »Medtem ko je bil otrok še živ, sem se postil in jokal, kajti rekel sem: ›Kdo lahko pove, ali mi bo Bog milostljiv, da bo otrok lahko živel?‹
23 Amma yanzu da ya mutu, me zai sa in yi azumi? Zan iya dawo da shi ne? Ni zan je wajensa, ba shi zai dawo wurina ba.”
Toda sedaj je mrtev, zakaj bi se torej postil? Ali ga lahko ponovno privedem nazaj? Jaz bom šel k njemu, toda on se ne bo vrnil k meni.«
24 Sai Dawuda ya yi wa matarsa Batsheba ta’aziyya, ya kuma tafi wurinta ya kwana da ita. Ta kuma haifi ɗa, suka ba shi suna Solomon. Ubangiji ya ƙaunace shi;
David je potolažil svojo ženo Batšébo in šel noter k njej in ležal z njo in rodila je sina in njegovo ime je imenoval Salomon. In Gospod ga je ljubil.
25 kuma saboda Ubangiji ya ƙaunace shi, sai ya aika da saƙo ta wurin annabi Natan yă ba shi suna Yedidiya.
In poslal je po roki preroka Natána in ta je njegovo ime imenoval Jedidjá, zaradi Gospoda.
26 Ana cikin haka, sai Yowab ya yi yaƙi da Rabba na Ammonawa, ya kuma ƙwace babban birnin.
Joáb se je boril zoper Rabo Amónovih sinov in zavzel kraljevo mesto.
27 Sa’an nan Yowab ya aika manzanni wurin Dawuda yana cewa, “Na yaƙi Rabba na kuma ƙwace hanyar samun ruwanta.
Joáb je poslal poslance k Davidu in rekel: »Boril sem se zoper Rabo in zavzel mesto vodá.
28 Yanzu fa ka tattara saura rundunoni ka fāɗa wa birnin ka ci shi. In ba haka ba zan karɓe birnin, a kuma kira shi da sunana.”
Zdaj torej zberi skupaj preostanek ljudstva in se utabôri zoper mesto in ga zavzemi, da ne bi jaz zavzel mesta in bi se ta imenoval po mojem imenu.«
29 Saboda haka Dawuda ya tattara sauran rundunar sojojin suka tafi Rabba suka fāɗa masa suka kuma ci shi.
In David je vse ljudstvo zbral skupaj in odšel v Rabo in se bojeval zoper njo ter jo zavzel.
30 Ya ɗauke rawanin daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti, na zinariya, an kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, aka aza shi a kan Dawuda. Ya kuma kwashe ganima mai yawa daga garin.
Vzel je krono njihovega kralja iz njegove glave, katere teža je bila talent zlata z dragocenimi kamni in ta je bila postavljena na Davidovo glavo. In iz mesta je prinesel plena v velikem obilju.
31 Ya fito da mutanen da suke a can, ya sa su su yi aiki da zarto, da diga, da kuma gatari, ya kuma sa su bugan bulok. Haka ya yi wa dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da dukan sojoji suka koma Urushalima.
Privedel je ljudstvo, ki je bilo tam in jih postavil pod žage, pod brane iz železa, pod sekire iz železa in jih primoral, da gredo skozi opekarsko peč. Tako je storil vsem mestom Amónovih otrok. Tako se je David in vse ljudstvo vrnilo v Jeruzalem.