< 2 Sama’ila 12 >
1 Ubangiji ya aiki Natan wurin Dawuda. Da ya tafi wajensa, sai ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu a wani gari, ɗaya mai arziki, ɗayan kuma matalauci.
Le Seigneur donc envoya Nathan vers David; et lorsque Nathan fut venu vers lui, il lui dit: Deux hommes étaient dans une ville, l’un riche et l’autre pauvre.
2 Mai arzikin yana da babban garken tumaki, da kuma shanu,
Le riche avait des brebis et des bœufs en très grand nombre;
3 amma matalauci ba shi da kome sai’yar tunkiyar da ya sayo. Ya yi kiwonta, ta kuwa yi girma tare shi da yaransa. Takan ci tare da shi ta sha ruwa a kwaf nasa, har ma ta kwanta a ƙirjinsa. Ta ma zama kamar’ya a gare shi.
Mais le pauvre n’avait absolument rien, hors une brebis très petite, qu’il avait achetée et nourrie, et qui avait grandi chez lui en même temps que ses enfants, mangeant de son pain, buvant de sa coupe, et dormant sur son sein, et elle était pour lui comme une fille.
4 “To, sai ga wani baƙo ya zo wurin mai arzikin nan, amma mai arzikin ya ƙi yă kama tunkiyarsa, ko saniyarsa yă yanka don yă shirya wa baƙon da ya zo abinci. A maimako, sai ya je ya kama’yar tunkiyan nan ta matalaucin ya yanka ya shirya wa mutumin da ya zo masa.”
Mais un étranger étant venu chez le riche, et s’abstenant de prendre de ses brebis et de ses bœufs, pour faire un festin à cet étranger, qui était venu chez lui, il enleva la brebis de l’homme pauvre, et apprêta un mets à l’homme qui était venu chez lui.
5 Dawuda ya husata ƙwarai da mutumin, ya ce wa Natan, “Muddin Ubangiji yana a raye, mutumin da ya yi wannan ya cancanci yă mutu!
Or, fortement irrité d’indignation contre cet homme, David dit: Le Seigneur vit! c’est un fils de mort, l’homme qui a fait cela.
6 Dole yă biya diyyar tunkiyan nan sau huɗu, domin ya aikata haka ba tausayi.”
Il rendra la brebis au quadruple, parce qu’il a fait cette action, et qu’il n’a pas épargné la pauvreté.
7 Sai Natan ya ce wa Dawuda, “Kai ne mutumin! Ga abin da Ubangiji, Allah ya ce, ‘Na naɗa ka sarki bisa Isra’ila, na kuma cece ka daga hannun Shawulu.
Alors Nathan dit à David: C’est vous qui êtes cet homme. Voici ce que dit le Seigneur Dieu d’Israël: C’est moi qui t’ai oint roi sur Israël, et moi qui t’ai délivré de la main de Saül;
8 Na ba ka gidan maigidanka, da matan maigidanka duka. Na ba ka gidan Isra’ila da Yahuda. Da a ce dukan waɗannan sun kāsa maka, ai, da na ƙara maka.
Et je t’ai donné la maison de ton seigneur et les femmes de ton seigneur sur ton sein; je t’ai donné aussi la maison d’Israël et de Juda; et si ce sont là de petites choses, je t’en aurais ajouté de beaucoup plus grandes.
9 Me ya sa ka rena maganar Ubangiji ta wurin yin mugunta haka a idonsa? Ka kashe Uriya mutumin Hitti da takobi, ka kuma ɗauki matarsa tă zama matarka. Ka kashe shi da takobin Ammonawa.
Pourquoi donc as-tu méprisé la parole du Seigneur pour faire le mal en ma présence? Tu as frappé du glaive Urie, l’Héthéen, tu as pris sa femme pour en faire ta femme, et tu l’as tué par le glaive des enfants d’Ammon.
10 To, fa, takobi ba zai taɓa rabu da gidanka ba, domin ka rena ni, ka kuma ƙwace matar Uriya mutumin Hitti ta zama matarka.’
Pour cette raison le glaive ne s’éloignera jamais de ta maison, parce que tu m’as méprisé, et que tu as enlevé la femme d’Urie, l’Héthéen, afin qu’elle fût ta femme.
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Daga cikin iyalinka zan kawo masifa a kanka. A idanunka zan ɗauki matanka in ba wa wani da yake kusa da kai, zai kuwa kwana da su da rana tsaka.
C’est pourquoi voici ce que dit le Seigneur: Voilà que moi je susciterai sur toi du mal de ta propre maison; et j’enlèverai tes femmes à tes yeux, et je les donnerai à ton prochain, et il dormira avec tes femmes aux yeux de ce soleil.
12 Ka aikata wannan a ɓoye, amma zan aikata wannan da rana tsaka, a gaban dukan Isra’ila.’”
Car toi tu as agi secrètement; mais moi, j’accomplirai cette parole en la présence de tout Israël, et en la présence du soleil.
13 Sai Dawuda ya ce wa Natan, “Na yi wa Ubangiji zunubi.” Natan ya ce, “Ubangiji ya yafe maka zunubin. Ba za ka mutu ba.
Et David dit à Nathan: J’ai péché contre le Seigneur. Et Nathan répondit à David: Le Seigneur aussi a transféré votre péché; vous ne mourrez point.
14 Amma saboda ka yi haka ka sa abokan gāba suka rena Ubangiji, yaron da aka haifa maka zai mutu.”
Cependant, parce que vous avez fait blasphémer les ennemis du Seigneur, à cause de cette action, le fils qui vous est né mourra de mort.
15 Bayan Natan ya tafi gida, sai Ubangiji ya bugi yaron da matar Uriya ta haifa wa Dawuda, ya kuwa kamu da ciwo.
Ensuite Nathan retourna en sa maison. Le Seigneur frappa aussi le petit enfant qu’avait enfanté la femme d’Urie à David, et il fut désespéré.
16 Dawuda ya roƙi Allah saboda yaron. Ya yi azumi, ya kuma shiga gidansa ya kwana kwance a ƙasa.
Et David pria le Seigneur pour le petit enfant, et David jeûna entièrement, et, étant entré à part, il demeura couché sur la terre.
17 Dattawan iyalinsa suka tsaya kusa da shi don su ɗaga shi daga ƙasa, amma ya ƙi, bai kuwa ci wani abu tare da su ba.
Mais vinrent les anciens de sa maison pour le forcer à se lever de terre; David ne voulut point, et il ne prit pas avec eux de nourriture.
18 A rana ta bakwai sai yaron ya rasu. Barorin Dawuda suka ji tsoro su gaya masa cewa yaron ya mutu, gama sun yi tunani cewa, “Yayinda yaron yake da rai, mun yi magana da Dawuda bai ji mu ba. Yaya za mu gaya masa yaron ya mutu? Ai, zai yi wa kansa ɓarna.”
Or, il arriva au septième jour que l’enfant mourut; et les serviteurs de David craignirent de lui annoncer que le petit enfant était mort; car ils dirent: Voilà que lorsque le petit enfant vivait encore, nous lui parlions, et il n’écoutait pas notre voix; combien plus s’affligera-t-il, si nous lui disons: Il est mort, le petit enfant?
19 Dawuda ya gane bayinsa suna wa juna raɗan wani abu, sai ya gane yaron ya mutu. Sai ya ce, “Yaron ya rasu ko?” Suka ce, “I, ya rasu.”
Lors donc que David eut vu ses serviteurs parlant tout bas, il comprit que le jeune enfant était mort; et il dit à ses serviteurs: Est-ce qu’il est mort, l’enfant? Ceux-ci lui répondirent: Il est mort.
20 Sa’an nan Dawuda ya tashi daga ƙasa. Bayan ya yi wanka, ya shafa mai, ya kuma canja rigunarsa, sa’an nan ya shiga gidan Ubangiji ya yi sujada. Sai ya tafi gidansa, ya nemi a ba shi abinci, aka ba shi, ya kuwa ci.
David donc se leva de terre, se lava et s’oignit; puis lorsqu’il eut changé de vêtement, il entra dans la maison du Seigneur et il adora; et il vint en sa maison, et il demanda qu’on lui servît du pain, et il mangea.
21 Barorinsa suka ce masa, “Me ya sa kake yin haka? Yayinda yaron yake da rai, ka yi azumi, ka kuma yi kuka, amma yanzu da yaron ya mutu, ka tashi, ka kuma ci abinci!”
Alors ses serviteurs lui demandèrent: Qu’est-ce que vous avez fait? à cause de l’enfant, vous avez jeûné et vous pleuriez, lorsqu’il vivait encore, mais, l’enfant mort, vous vous êtes levé, et vous avez mangé du pain.
22 Ya ce musu, “Yayinda yaron yake da rai, na yi azumi, na kuma yi kuka. Na yi tunani na ce, ‘Wa ya sani? Ko Ubangiji zai yi mini alheri yă bar yaron yă rayu.’
David répondit: À cause de l’enfant, pendant qu’il vivait encore, j’ai jeûné et j’ai pleuré; car je disais: Qui sait si le Seigneur ne me le donnera point, et si l’enfant ne vivra point?
23 Amma yanzu da ya mutu, me zai sa in yi azumi? Zan iya dawo da shi ne? Ni zan je wajensa, ba shi zai dawo wurina ba.”
Mais maintenant qu’il est mort, pourquoi jeûnerais-je? Est-ce que je pourrai encore le faire revenir? Moi j’irai plutôt à lui; mais lui ne reviendra pas à moi.
24 Sai Dawuda ya yi wa matarsa Batsheba ta’aziyya, ya kuma tafi wurinta ya kwana da ita. Ta kuma haifi ɗa, suka ba shi suna Solomon. Ubangiji ya ƙaunace shi;
Et David consola Bethsabée sa femme, il s’approcha d’elle et dormit avec elle; et elle engendra un fils, et il l’appela du nom de Salomon, et le Seigneur l’aima;
25 kuma saboda Ubangiji ya ƙaunace shi, sai ya aika da saƙo ta wurin annabi Natan yă ba shi suna Yedidiya.
Et il envoya par l’entremise de Nathan, le prophète, et il l’appela du nom d’Aimable au Seigneur, parce que le Seigneur l’aima.
26 Ana cikin haka, sai Yowab ya yi yaƙi da Rabba na Ammonawa, ya kuma ƙwace babban birnin.
Or, Joab combattait contre Rabbath des enfants d’Ammon, et il attaquait vivement la ville royale.
27 Sa’an nan Yowab ya aika manzanni wurin Dawuda yana cewa, “Na yaƙi Rabba na kuma ƙwace hanyar samun ruwanta.
Et Joab envoya des messagers à David, disant: J’ai combattu contre Rabbath, et la ville des eaux doit être prise.
28 Yanzu fa ka tattara saura rundunoni ka fāɗa wa birnin ka ci shi. In ba haka ba zan karɓe birnin, a kuma kira shi da sunana.”
Maintenant donc, assemblez le reste du peuple, assiégez la ville et prenez-la, de peur que, lorsque la ville aura été détruite par moi, la victoire ne soit attribuée à mon nom.
29 Saboda haka Dawuda ya tattara sauran rundunar sojojin suka tafi Rabba suka fāɗa masa suka kuma ci shi.
C’est pourquoi David assembla tout le peuple, et partit contre Rabbath, et après qu’il eut combattu, il la prit.
30 Ya ɗauke rawanin daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti, na zinariya, an kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, aka aza shi a kan Dawuda. Ya kuma kwashe ganima mai yawa daga garin.
Et il ôta le diadème du roi de sa tête, pesant un talent d’or, et ayant des pierreries très précieuses; et il fut mis sur la tête de David. Mais il emporta aussi le très grand butin de la ville;
31 Ya fito da mutanen da suke a can, ya sa su su yi aiki da zarto, da diga, da kuma gatari, ya kuma sa su bugan bulok. Haka ya yi wa dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da dukan sojoji suka koma Urushalima.
Et amenant ses habitants, il les scia, fit passer sur eux les chariots armés de fer, les partagea avec des couteaux, et les fit passer dans le moule des briques; ainsi fit-il à toutes les villes des enfants d’Ammon. Ensuite David revint et toute l’armée à Jérusalem.