< 2 Sama’ila 12 >
1 Ubangiji ya aiki Natan wurin Dawuda. Da ya tafi wajensa, sai ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu a wani gari, ɗaya mai arziki, ɗayan kuma matalauci.
Yahvé envoya Nathan auprès de David. Il vint le trouver et lui dit: « Il y avait dans une ville deux hommes, l'un riche et l'autre pauvre.
2 Mai arzikin yana da babban garken tumaki, da kuma shanu,
Le riche avait beaucoup de troupeaux,
3 amma matalauci ba shi da kome sai’yar tunkiyar da ya sayo. Ya yi kiwonta, ta kuwa yi girma tare shi da yaransa. Takan ci tare da shi ta sha ruwa a kwaf nasa, har ma ta kwanta a ƙirjinsa. Ta ma zama kamar’ya a gare shi.
mais le pauvre n'avait rien, sauf une petite brebis qu'il avait achetée et élevée. Elle grandissait avec lui et avec ses enfants. Elle mangeait de sa nourriture, buvait dans sa coupe, se couchait dans son sein et était pour lui comme une fille.
4 “To, sai ga wani baƙo ya zo wurin mai arzikin nan, amma mai arzikin ya ƙi yă kama tunkiyarsa, ko saniyarsa yă yanka don yă shirya wa baƙon da ya zo abinci. A maimako, sai ya je ya kama’yar tunkiyan nan ta matalaucin ya yanka ya shirya wa mutumin da ya zo masa.”
Un voyageur vint chez le riche, et il ne voulut pas prendre de son propre troupeau et de son propre bétail pour le préparer pour le voyageur qui était venu chez lui, mais il prit l'agneau du pauvre et le prépara pour l'homme qui était venu chez lui. »
5 Dawuda ya husata ƙwarai da mutumin, ya ce wa Natan, “Muddin Ubangiji yana a raye, mutumin da ya yi wannan ya cancanci yă mutu!
La colère de David s'enflamma contre cet homme, et il dit à Nathan: « L'Éternel est vivant, l'homme qui a fait cela mérite la mort!
6 Dole yă biya diyyar tunkiyan nan sau huɗu, domin ya aikata haka ba tausayi.”
Il doit rendre l'agneau au quadruple, parce qu'il a fait cette chose et parce qu'il n'a pas eu de pitié! ».
7 Sai Natan ya ce wa Dawuda, “Kai ne mutumin! Ga abin da Ubangiji, Allah ya ce, ‘Na naɗa ka sarki bisa Isra’ila, na kuma cece ka daga hannun Shawulu.
Nathan dit à David: « Tu es l'homme de la situation! Voici ce que dit Yahvé, le Dieu d'Israël: « Je t'ai oint comme roi d'Israël et je t'ai délivré de la main de Saül.
8 Na ba ka gidan maigidanka, da matan maigidanka duka. Na ba ka gidan Isra’ila da Yahuda. Da a ce dukan waɗannan sun kāsa maka, ai, da na ƙara maka.
Je t'ai donné la maison de ton maître et les femmes de ton maître dans ton sein, et je t'ai donné la maison d'Israël et de Juda; et si cela eût été trop peu, je t'en aurais ajouté beaucoup d'autres.
9 Me ya sa ka rena maganar Ubangiji ta wurin yin mugunta haka a idonsa? Ka kashe Uriya mutumin Hitti da takobi, ka kuma ɗauki matarsa tă zama matarka. Ka kashe shi da takobin Ammonawa.
Pourquoi avez-vous méprisé la parole de l'Éternel, pour faire ce qui est mal à ses yeux? Vous avez frappé par l'épée Urie, le Hittite, vous avez pris sa femme pour en faire votre épouse, et vous l'avez tué par l'épée des fils d'Ammon.
10 To, fa, takobi ba zai taɓa rabu da gidanka ba, domin ka rena ni, ka kuma ƙwace matar Uriya mutumin Hitti ta zama matarka.’
Maintenant, l'épée ne s'éloignera jamais de ta maison, parce que tu m'as méprisé et que tu as pris pour femme la femme d'Urie, le Héthien ».
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Daga cikin iyalinka zan kawo masifa a kanka. A idanunka zan ɗauki matanka in ba wa wani da yake kusa da kai, zai kuwa kwana da su da rana tsaka.
« Voici ce que dit Yahvé: 'Voici, je vais susciter le mal contre toi à partir de ta propre maison; je prendrai tes femmes sous tes yeux et les donnerai à ton prochain, et il couchera avec tes femmes sous les yeux de ce soleil.
12 Ka aikata wannan a ɓoye, amma zan aikata wannan da rana tsaka, a gaban dukan Isra’ila.’”
Car vous avez fait cela secrètement, mais moi, je ferai cela devant tout Israël et devant le soleil.'"
13 Sai Dawuda ya ce wa Natan, “Na yi wa Ubangiji zunubi.” Natan ya ce, “Ubangiji ya yafe maka zunubin. Ba za ka mutu ba.
David dit à Nathan: « J'ai péché contre Yahvé. » Nathan dit à David: « Yahvé a aussi effacé ton péché. Tu ne mourras pas.
14 Amma saboda ka yi haka ka sa abokan gāba suka rena Ubangiji, yaron da aka haifa maka zai mutu.”
Mais, parce que tu as donné aux ennemis de Yahvé l'occasion de blasphémer, l'enfant qui te naîtra mourra. »
15 Bayan Natan ya tafi gida, sai Ubangiji ya bugi yaron da matar Uriya ta haifa wa Dawuda, ya kuwa kamu da ciwo.
Puis Nathan s'en alla dans sa maison. Yahvé frappa l'enfant que la femme d'Urie avait enfanté à David, et celui-ci fut très malade.
16 Dawuda ya roƙi Allah saboda yaron. Ya yi azumi, ya kuma shiga gidansa ya kwana kwance a ƙasa.
David supplia donc Dieu de lui accorder cet enfant; il jeûna, entra et passa la nuit à terre.
17 Dattawan iyalinsa suka tsaya kusa da shi don su ɗaga shi daga ƙasa, amma ya ƙi, bai kuwa ci wani abu tare da su ba.
Les anciens de sa maison se levèrent à côté de lui, pour le relever de terre; mais il ne voulut pas, et il ne mangea pas de pain avec eux.
18 A rana ta bakwai sai yaron ya rasu. Barorin Dawuda suka ji tsoro su gaya masa cewa yaron ya mutu, gama sun yi tunani cewa, “Yayinda yaron yake da rai, mun yi magana da Dawuda bai ji mu ba. Yaya za mu gaya masa yaron ya mutu? Ai, zai yi wa kansa ɓarna.”
Le septième jour, l'enfant mourut. Les serviteurs de David eurent peur de lui annoncer que l'enfant était mort, car ils disaient: « Voici, lorsque l'enfant était encore vivant, nous lui avons parlé et il n'a pas écouté notre voix. Comment se fera-t-il donc du mal si nous lui disons que l'enfant est mort? ».
19 Dawuda ya gane bayinsa suna wa juna raɗan wani abu, sai ya gane yaron ya mutu. Sai ya ce, “Yaron ya rasu ko?” Suka ce, “I, ya rasu.”
Mais lorsque David vit que ses serviteurs chuchotaient ensemble, il comprit que l'enfant était mort; et David dit à ses serviteurs: « L'enfant est-il mort? » Ils ont dit: « Il est mort. »
20 Sa’an nan Dawuda ya tashi daga ƙasa. Bayan ya yi wanka, ya shafa mai, ya kuma canja rigunarsa, sa’an nan ya shiga gidan Ubangiji ya yi sujada. Sai ya tafi gidansa, ya nemi a ba shi abinci, aka ba shi, ya kuwa ci.
Alors David se leva de terre, se lava, s'oignit et changea de vêtements, puis il entra dans la maison de Yahvé et se prosterna. Puis il rentra dans sa maison; et quand il demanda, on mit du pain devant lui et il mangea.
21 Barorinsa suka ce masa, “Me ya sa kake yin haka? Yayinda yaron yake da rai, ka yi azumi, ka kuma yi kuka, amma yanzu da yaron ya mutu, ka tashi, ka kuma ci abinci!”
Alors ses serviteurs lui dirent: « Qu'est-ce que tu as fait? Tu as jeûné et pleuré l'enfant pendant qu'il était vivant, mais quand l'enfant est mort, tu t'es levé et tu as mangé du pain. »
22 Ya ce musu, “Yayinda yaron yake da rai, na yi azumi, na kuma yi kuka. Na yi tunani na ce, ‘Wa ya sani? Ko Ubangiji zai yi mini alheri yă bar yaron yă rayu.’
Il dit: « Lorsque l'enfant vivait encore, j'ai jeûné et pleuré, car je disais: « Qui sait si Yahvé ne me fera pas grâce, afin que l'enfant vive? »
23 Amma yanzu da ya mutu, me zai sa in yi azumi? Zan iya dawo da shi ne? Ni zan je wajensa, ba shi zai dawo wurina ba.”
Mais maintenant, il est mort. Pourquoi devrais-je jeûner? Puis-je le ramener à la vie? J'irai vers lui, mais il ne reviendra pas vers moi. »
24 Sai Dawuda ya yi wa matarsa Batsheba ta’aziyya, ya kuma tafi wurinta ya kwana da ita. Ta kuma haifi ɗa, suka ba shi suna Solomon. Ubangiji ya ƙaunace shi;
David consola sa femme Bethsabée, alla vers elle, et coucha avec elle. Elle enfanta un fils, et il lui donna le nom de Salomon. L'Éternel l'aima.
25 kuma saboda Ubangiji ya ƙaunace shi, sai ya aika da saƙo ta wurin annabi Natan yă ba shi suna Yedidiya.
Il envoya par la main de Nathan le prophète, qui lui donna le nom de Jedidia, à cause de l'Éternel.
26 Ana cikin haka, sai Yowab ya yi yaƙi da Rabba na Ammonawa, ya kuma ƙwace babban birnin.
Joab fit la guerre à Rabba, des enfants d'Ammon, et prit la ville royale.
27 Sa’an nan Yowab ya aika manzanni wurin Dawuda yana cewa, “Na yaƙi Rabba na kuma ƙwace hanyar samun ruwanta.
Joab envoya des messagers à David, et dit: « J'ai combattu contre Rabba. Oui, j'ai pris la ville des eaux.
28 Yanzu fa ka tattara saura rundunoni ka fāɗa wa birnin ka ci shi. In ba haka ba zan karɓe birnin, a kuma kira shi da sunana.”
Maintenant, rassemble le reste du peuple, campe contre la ville et prends-la, de peur que je ne prenne la ville et qu'on l'appelle de mon nom. »
29 Saboda haka Dawuda ya tattara sauran rundunar sojojin suka tafi Rabba suka fāɗa masa suka kuma ci shi.
David rassembla tout le peuple, alla à Rabba, l'attaqua et la prit.
30 Ya ɗauke rawanin daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti, na zinariya, an kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, aka aza shi a kan Dawuda. Ya kuma kwashe ganima mai yawa daga garin.
Il enleva de sa tête la couronne de leur roi, dont le poids était d'un talent d'or, et dans laquelle il y avait des pierres précieuses, et il la mit sur la tête de David. Il fit sortir de la ville une grande quantité de butin.
31 Ya fito da mutanen da suke a can, ya sa su su yi aiki da zarto, da diga, da kuma gatari, ya kuma sa su bugan bulok. Haka ya yi wa dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da dukan sojoji suka koma Urushalima.
Il fit sortir les gens qui s'y trouvaient et les fit travailler sous des scies, sous des pioches de fer, sous des haches de fer, et les fit passer au four à briques; il fit ainsi dans toutes les villes des enfants d'Ammon. Puis David et tout le peuple retournèrent à Jérusalem.