< 2 Sama’ila 12 >
1 Ubangiji ya aiki Natan wurin Dawuda. Da ya tafi wajensa, sai ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu a wani gari, ɗaya mai arziki, ɗayan kuma matalauci.
So then Yahweh sent Nathan the prophet unto David, —who therefore came unto him and said to him—Two men, there were in a certain city, the one, rich, and, the other, poor.
2 Mai arzikin yana da babban garken tumaki, da kuma shanu,
The, rich, man had flocks and herds exceeding many;
3 amma matalauci ba shi da kome sai’yar tunkiyar da ya sayo. Ya yi kiwonta, ta kuwa yi girma tare shi da yaransa. Takan ci tare da shi ta sha ruwa a kwaf nasa, har ma ta kwanta a ƙirjinsa. Ta ma zama kamar’ya a gare shi.
whereas the, poor, man had, nothing, —save one little lamb, which he had made his own, and sustained, and it had grown up with him and with his children, all together, —of his own morsel, used it to eat, and, out of his own cup, used it to drink, and, in his own bosom, used it to lie, and it was to him, as a daughter.
4 “To, sai ga wani baƙo ya zo wurin mai arzikin nan, amma mai arzikin ya ƙi yă kama tunkiyarsa, ko saniyarsa yă yanka don yă shirya wa baƙon da ya zo abinci. A maimako, sai ya je ya kama’yar tunkiyan nan ta matalaucin ya yanka ya shirya wa mutumin da ya zo masa.”
Now there came a traveller to the rich man, but he thought it a pity to take of his own flock, or his own herd, to make ready for the wayfarer who had come to him, —so he took the lamb of his poor neighbour, and made ready for the man who had come to him.
5 Dawuda ya husata ƙwarai da mutumin, ya ce wa Natan, “Muddin Ubangiji yana a raye, mutumin da ya yi wannan ya cancanci yă mutu!
Then was kindled the anger of David against the man, fiercely, —and he said unto Nathan, By the life of Yahweh, doomed to death, is the man that hath done this;
6 Dole yă biya diyyar tunkiyan nan sau huɗu, domin ya aikata haka ba tausayi.”
and, the lamb, shall he pay back sevenfold, —because he did this thing, and, for that he had no pity.
7 Sai Natan ya ce wa Dawuda, “Kai ne mutumin! Ga abin da Ubangiji, Allah ya ce, ‘Na naɗa ka sarki bisa Isra’ila, na kuma cece ka daga hannun Shawulu.
Then said Nathan unto David: Thou, art the man! Thus, saith Yahweh, God of Israel—I, anointed thee to be king over Israel, and, I, delivered thee out of the hand of Saul;
8 Na ba ka gidan maigidanka, da matan maigidanka duka. Na ba ka gidan Isra’ila da Yahuda. Da a ce dukan waɗannan sun kāsa maka, ai, da na ƙara maka.
and gave unto thee the household of thy lord, and the wives of thy lord, into thy bosom, and gave unto thee the house of Israel and Judah. And, if this had been too little, I could have further given thee more and more of such things.
9 Me ya sa ka rena maganar Ubangiji ta wurin yin mugunta haka a idonsa? Ka kashe Uriya mutumin Hitti da takobi, ka kuma ɗauki matarsa tă zama matarka. Ka kashe shi da takobin Ammonawa.
Wherefore, hast thou despised the word of Yahweh, by doing that which is wicked in mine eyes? Uriah the Hittite, hast thou smitten with the sword, and, his wife, hast thou taken to thyself to wife, yea, him, hast thou slain with the sword of the sons of Ammon!
10 To, fa, takobi ba zai taɓa rabu da gidanka ba, domin ka rena ni, ka kuma ƙwace matar Uriya mutumin Hitti ta zama matarka.’
Now, therefore, the sword shall not depart from thy house, unto age-abiding times, —because thou hast despised me, and taken the wife of Uriah the Hittite to be thy wife.
11 “Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Daga cikin iyalinka zan kawo masifa a kanka. A idanunka zan ɗauki matanka in ba wa wani da yake kusa da kai, zai kuwa kwana da su da rana tsaka.
Thus, saith Yahweh, —Behold me! raising up over thee calamity out of thine own household, and I will take thy wives, before thine eyes, and give unto thy neighbour, and he will lie with thy wives, in the eyes of this sun.
12 Ka aikata wannan a ɓoye, amma zan aikata wannan da rana tsaka, a gaban dukan Isra’ila.’”
For, thou, didst it, in secret, —but, I, will do this thing, before all Israel, and before the sun.
13 Sai Dawuda ya ce wa Natan, “Na yi wa Ubangiji zunubi.” Natan ya ce, “Ubangiji ya yafe maka zunubin. Ba za ka mutu ba.
And David said unto Nathan, I have sinned against Yahweh. Then said Nathan unto David, —Yahweh also, hath put away thy sin, thou shalt not die!
14 Amma saboda ka yi haka ka sa abokan gāba suka rena Ubangiji, yaron da aka haifa maka zai mutu.”
Nevertheless, because thou hast greatly blasphemed Yahweh, by this thing, the very son that is born to thee, shall, die.
15 Bayan Natan ya tafi gida, sai Ubangiji ya bugi yaron da matar Uriya ta haifa wa Dawuda, ya kuwa kamu da ciwo.
And Nathan departed unto his own house, —and Yahweh struck the child that the wife of Uriah had borne unto David, and it fell sick.
16 Dawuda ya roƙi Allah saboda yaron. Ya yi azumi, ya kuma shiga gidansa ya kwana kwance a ƙasa.
David therefore earnestly sought God in behalf of the boy, —and David kept a fast, and used to go in and pass the night, and lie upon the ground.
17 Dattawan iyalinsa suka tsaya kusa da shi don su ɗaga shi daga ƙasa, amma ya ƙi, bai kuwa ci wani abu tare da su ba.
And the elders of his house stood up over him, to raise him from the ground, —but he would not, neither would he eat food with them.
18 A rana ta bakwai sai yaron ya rasu. Barorin Dawuda suka ji tsoro su gaya masa cewa yaron ya mutu, gama sun yi tunani cewa, “Yayinda yaron yake da rai, mun yi magana da Dawuda bai ji mu ba. Yaya za mu gaya masa yaron ya mutu? Ai, zai yi wa kansa ɓarna.”
And it came to pass, on the seventh day, that the child died, —but the servants of David feared to tell him that the child was dead, for said they—Lo! while the child was living, we spake unto him, and he hearkened not unto our voice, how then can we say unto him, The child is dead, and so he do [himself] harm?
19 Dawuda ya gane bayinsa suna wa juna raɗan wani abu, sai ya gane yaron ya mutu. Sai ya ce, “Yaron ya rasu ko?” Suka ce, “I, ya rasu.”
But, when David saw that his servants were whispering among themselves, then understood David that the child was dead, —and David said unto his servants—Is the child, dead? And they answered—Dead!
20 Sa’an nan Dawuda ya tashi daga ƙasa. Bayan ya yi wanka, ya shafa mai, ya kuma canja rigunarsa, sa’an nan ya shiga gidan Ubangiji ya yi sujada. Sai ya tafi gidansa, ya nemi a ba shi abinci, aka ba shi, ya kuwa ci.
Then David arose from the ground, and bathed and anointed, and changed his apparel, and, entering into the house of Yahweh, bowed himself down, —then came he into his own house, and asked, and they set before him food, and he did eat.
21 Barorinsa suka ce masa, “Me ya sa kake yin haka? Yayinda yaron yake da rai, ka yi azumi, ka kuma yi kuka, amma yanzu da yaron ya mutu, ka tashi, ka kuma ci abinci!”
Then said his servants unto him, What is this thing that thou hast done? For the child’s sake, while living, thou didst fast and weep, but, as soon as the child was dead, thou didst arise and eat food.
22 Ya ce musu, “Yayinda yaron yake da rai, na yi azumi, na kuma yi kuka. Na yi tunani na ce, ‘Wa ya sani? Ko Ubangiji zai yi mini alheri yă bar yaron yă rayu.’
And he said, —While yet the child lived, I fasted, and wept, —for I said—Who knoweth whether Yahweh may not grant me favour, and the child live?
23 Amma yanzu da ya mutu, me zai sa in yi azumi? Zan iya dawo da shi ne? Ni zan je wajensa, ba shi zai dawo wurina ba.”
But, now, that he is dead, wherefore should I go on fasting? can I bring him back again? I am going unto him, but, he, will not come back unto me.
24 Sai Dawuda ya yi wa matarsa Batsheba ta’aziyya, ya kuma tafi wurinta ya kwana da ita. Ta kuma haifi ɗa, suka ba shi suna Solomon. Ubangiji ya ƙaunace shi;
And David consoled Bath-sheba his wife, and went in unto her, and lay with her, —and she bare a son, and called his name, Solomon, and Yahweh loved him.
25 kuma saboda Ubangiji ya ƙaunace shi, sai ya aika da saƙo ta wurin annabi Natan yă ba shi suna Yedidiya.
And he sent by the hand of Nathan the prophet, and called his name Jedidiah ["Beloved of Yah"], for Yahweh’s sake.
26 Ana cikin haka, sai Yowab ya yi yaƙi da Rabba na Ammonawa, ya kuma ƙwace babban birnin.
And Joab fought against Rabbah, of the sons of Ammon, —and captured the royal city.
27 Sa’an nan Yowab ya aika manzanni wurin Dawuda yana cewa, “Na yaƙi Rabba na kuma ƙwace hanyar samun ruwanta.
Then Joab sent messengers unto David, —and said—I have fought against Rabbah, I have also captured the city of the waters.
28 Yanzu fa ka tattara saura rundunoni ka fāɗa wa birnin ka ci shi. In ba haka ba zan karɓe birnin, a kuma kira shi da sunana.”
Now, therefore, gather thou together the rest of the people, and encamp against the city, and capture it, —lest, I, capture the city, and it be called by my name.
29 Saboda haka Dawuda ya tattara sauran rundunar sojojin suka tafi Rabba suka fāɗa masa suka kuma ci shi.
So David gathered together all the people, and went to Rabbah, —and fought against it, and captured it.
30 Ya ɗauke rawanin daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti, na zinariya, an kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, aka aza shi a kan Dawuda. Ya kuma kwashe ganima mai yawa daga garin.
Then took he the crown of Milcom from off his head, the weight thereof, being a talent of gold, with the precious stones, and it remained on the head of David, —the spoil of the city also, brought he forth in great abundance;
31 Ya fito da mutanen da suke a can, ya sa su su yi aiki da zarto, da diga, da kuma gatari, ya kuma sa su bugan bulok. Haka ya yi wa dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da dukan sojoji suka koma Urushalima.
the people also that were therein, brought he forth, and put them to the saw, and to threshing sledges of iron, and to axes of iron, and made them pass through the brickkiln, and thus used he to do unto all the cities of the sons of Ammon. And David and all the people returned unto Jerusalem.