< 2 Sama’ila 11 >

1 Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
A kad proðe godina, u vrijeme kad carevi idu na vojsku, posla David Joava i sluge svoje s njim, i svega Izrailja, te potirahu sinove Amonove, i opkoliše Ravu; a David osta u Jerusalimu.
2 Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
I pred veèe usta David s postelje svoje, i hodajuæi po krovu carskoga dvora ugleda s krova ženu gdje se mije, a žena bijaše vrlo lijepa na oèi.
3 Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
I David posla da propitaju za ženu i rekoše: nije li to Vitsaveja kæi Elijamova žena Urije Hetejina?
4 Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
I David posla poslanike da je dovedu; i kad doðe k njemu, on leže s njom, a ona se bješe oèistila od neèistote svoje; poslije se vrati svojoj kuæi.
5 Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
I zatrudnje žena, te posla i javi Davidu govoreæi: trudna sam.
6 Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
Tada David posla k Joavu i poruèi: pošlji mi Uriju Hetejina. I posla Joav Uriju k Davidu.
7 Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
I kad Urija doðe k njemu, zapita ga David kako je Joav i kako je narod i kako ide rat.
8 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
Potom reèe David Uriji: idi kuæi svojoj, i operi noge svoje. I Urija izide iz careva dvora, a za njim iznesoše jelo carsko.
9 Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
Ali Urija leže na vratima dvora careva sa svijem slugama gospodara svojega, i ne otide kuæi svojoj.
10 Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
I javiše Davidu govoreæi: Urija nije otišao kuæi svojoj. A David reèe Uriji: nijesi li došao s puta? zašto ne ideš kuæi svojoj?
11 Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
A Urija reèe Davidu: kovèeg i Izrailj i Juda stoje po šatorima, i Joav gospodar moj i sluge gospodara mojega stoje u polju, pa kako bih ja ušao u kuæu svoju da jedem i pijem i spavam sa ženom svojom? Tako ti bio živ i tako bila živa duša tvoja, neæu to uèiniti.
12 Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
Tada reèe David Uriji: ostani ovdje još danas, pa æu te sjutra otpustiti. Tako osta Urija u Jerusalimu onaj dan i sjutradan.
13 Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
I pozva ga David da jede i pije s njim, te ga opije. A uveèe otide, te leže na postelju svoju sa slugama gospodara svojega, a kuæi svojoj ne otide.
14 Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
A ujutru napisa David knjigu Joavu, i posla po Uriji.
15 A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
A u knjizi pisa i reèe: namjestite Uriju gdje je najžešæi boj, pa se uzmaknite od njega da bi ga ubili da pogine.
16 Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
I Joav opkolivši grad namjesti Uriju na mjesto gdje je znao da su najhrabriji ljudi.
17 Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
I izidoše ljudi iz grada i pobiše se s Judom. I pogibe iz naroda nekoliko sluga Davidovijeh; pogibe i Urija Hetejin.
18 Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
Tada Joav posla k Davidu, i javi mu sve što bi u boju.
19 Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
I zapovjedi glasniku govoreæi: kad pripovjediš caru sve što je bilo u boju,
20 wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
Ako se razgnjevi car i reèe ti: zašto ste išli tako blizu grada da se bijete? zar nijeste znali kako se strijelja s grada?
21 Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
Ko je ubio Avimeleha sina Jeruvesetova? nije li žena bacila na nj komad žrvnja sa zida, te pogibe u Tevesu? zašto ste išli blizu zida? tada reci: poginuo je i sluga tvoj Urija Hetejin.
22 Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
I otide glasnik, i došavši javi Davidu sve za što ga je poslao Joav.
23 Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
I reèe glasnik Davidu: bijahu jaèi od nas, i izidoše u polje na nas, ali ih uzbismo do vrata gradskih.
24 Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
A strijelci stadoše strijeljati na sluge tvoje sa zida, i pogibe nekoliko sluga carevijeh, tako i sluga tvoj Urija Hetejin pogibe.
25 Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
Tada reèe David glasniku: ovako reci Joavu: ne budi zlovoljan za to; jer maè proždire sad ovoga sad onoga; udri još jaèe na grad i raskopaj ga. Tako ga ohrabri.
26 Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
A žena Urijina èuvši da je poginuo muž njezin Urija, plaka za mužem svojim.
27 Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.
A kad proðe žalost, posla David i uze je u kuæu svoju, i ona mu posta žena, i rodi mu sina. Ali ne bješe po volji Gospodu što uèini David.

< 2 Sama’ila 11 >