< 2 Sama’ila 11 >

1 Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
Året efter, ved den tid da kongene pleier å dra ut i krig, sendte David Joab avsted med sine tjenere og hele Israel, og de herjet Ammons barns land og kringsatte Rabba. Men David blev i Jerusalem.
2 Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
Så hendte det en aften at David stod op fra sitt leie og gikk omkring på kongehusets tak; da fikk han fra taket se en kvinne som badet sig; og kvinnen var meget fager av utseende.
3 Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
David sendte bud og spurte sig for om kvinnen, og de sa: Det er jo Batseba, datter av Eliam og hetitten Urias hustru.
4 Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
Da sendte David bud og lot henne hente; hun kom til ham, og han lå hos henne like efterat hun hadde renset sig fra sin urenhet; så gikk hun hjem igjen.
5 Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
Kvinnen blev fruktsommelig; og hun sendte bud om det til David og lot si: Jeg er fruktsommelig.
6 Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
Da sendte David det bud til Joab: Send hetitten Uria til mig! Og Joab sendte Uria til David.
7 Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
Da Uria kom til ham, spurte David ham om det stod vel til med Joab og med krigsfolkene, og hvorledes det gikk med krigen.
8 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
Så sa David til Uria: Gå ned til ditt hus og tvett dine føtter! Og da Uria gikk ut av kongens hus, blev det sendt en rett mat efter ham fra kongens bord.
9 Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
Men Uria la sig ved inngangen til kongens hus sammen med alle sin herres tjenere og gikk ikke ned til sitt hus.
10 Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
Da det blev meldt David at Uria ikke var gått ned til sitt hus, sa David til ham: Kommer du ikke fra reisen? Hvorfor er du da ikke gått ned til ditt hus?
11 Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
Da svarte Uria: Arken og Israel og Juda bor i løvhytter, og min herre Joab og min herres tjenere ligger i leir på åpen mark, og jeg skulde gå inn i mitt hus og ete og drikke og ligge hos min hustru! Så sant du lever, så sant din sjel lever: Det gjør jeg ikke!
12 Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
Da sa David til Uria: Bli her også idag, så vil jeg imorgen la dig fare. Og Uria blev i Jerusalem den dag og dagen efter.
13 Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
Og David bad ham til sig, og han åt og drakk hos ham, og han drakk ham drukken; og om aftenen gikk han ut og la sig på sitt leie sammen med sin herres tjenere; men til sitt hus gikk han ikke ned.
14 Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
Morgenen efter skrev David et brev til Joab og sendte det med Uria.
15 A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
Og i brevet skrev han således: Sett Uria lengst frem, der hvor striden er hårdest, og dra eder tilbake fra ham, så han blir slått og dør!
16 Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
Mens nu Joab lå og voktet på byen, satte han Uria på et sted hvor han visste at der var djerve menn.
17 Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
Og da mennene i byen drog ut og stred mot Joab, falt nogen av krigsfolket - av Davids menn - og hetitten Uria døde også.
18 Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
Da sendte Joab bud til David med tidende om alt som hadde hendt i krigen.
19 Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
Og han bød sendebudet: Når du har talt ut til kongen om alt det som har hendt i krigen,
20 wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
og det skulde hende at kongens vrede optendes, og han sier til dig: Hvorfor gikk I så nær inn til byen under striden? Visste I ikke at de vilde skyte ned fra muren?
21 Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
Hvem var det som drepte Abimelek, Jerubbesets sønn? Var det ikke en kvinne som kastet en kvernsten ned på ham fra muren i Tebes, så han døde? Hvorfor gikk I så nær inn til muren? - så skal du si: Også din tjener hetitten Uria er død.
22 Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
Så tok sendebudet avsted og kom og meldte David alt det Joab hadde pålagt ham.
23 Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
Og budet sa til David: Mennene fikk overtaket over oss og drog ut på marken mot oss; men så trengte vi dem tilbake like til byporten.
24 Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
Da skjøt bueskytterne fra muren ned på dine tjenere, og det falt nogen av kongens tjenere; også din tjener hetitten Uria døde.
25 Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
Da sa David til budet: Så skal du si til Joab: Ta dig ikke nær av dette! For sverdet fortærer snart en, snart en annen; hold kraftig ved med å stride mot byen og riv den ned! Og sett du mot i ham!
26 Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
Da Urias hustru hørte at Uria, hennes mann var død, sørget hun over sin ektefelle.
27 Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.
Men da sørgetiden var til ende, sendte David bud og hentet henne til sitt hus, og hun blev hans hustru og fødte ham en sønn. Men det som David hadde gjort, var ondt i Herrens øine.

< 2 Sama’ila 11 >