< 2 Sama’ila 11 >

1 Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
Et il arriva, au retour de l’année, au temps où les rois entrent en campagne, que David envoya Joab, et ses serviteurs avec lui, et tout Israël; et ils détruisirent les fils d’Ammon et assiégèrent Rabba; mais David resta à Jérusalem.
2 Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
Et il arriva, au temps du soir, que David se leva de dessus son lit de repos et se promena sur le toit de la maison du roi, et, du toit, il vit une femme qui se lavait, et la femme était très belle à voir.
3 Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
Et David envoya et s’informa de cette femme, et on [lui] dit: N’est-ce pas là Bath-Shéba, fille d’Éliam, femme d’Urie, le Héthien?
4 Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
Et David envoya des messagers, et la prit; et elle vint vers lui, et il coucha avec elle (et elle se purifia de son impureté); et elle s’en retourna dans sa maison.
5 Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
Et la femme conçut; et elle envoya, et informa David et dit: Je suis enceinte.
6 Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
Et David envoya vers Joab, [disant]: Envoie-moi Urie, le Héthien. Et Joab envoya Urie à David.
7 Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
Et Urie vint vers lui; et David s’enquit de l’état de Joab, et de l’état du peuple, et de l’état de la guerre.
8 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
Et David dit à Urie: Descends dans ta maison, et lave tes pieds. Et Urie sortit de la maison du roi, et on envoya après lui un présent de la part du roi.
9 Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
Et Urie se coucha à l’entrée de la maison du roi avec tous les serviteurs de son seigneur, et ne descendit pas dans sa maison.
10 Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
Et on le rapporta à David, disant: Urie n’est pas descendu dans sa maison. Et David dit à Urie: Ne viens-tu pas de voyage? Pourquoi n’es-tu pas descendu dans ta maison?
11 Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
Et Urie dit à David: L’arche, et Israël, et Juda, habitent sous des tentes; et mon seigneur Joab et les serviteurs de mon seigneur campent dans les champs, et moi, j’entrerais dans ma maison pour manger et boire, et pour coucher avec ma femme? Tu es vivant, et ton âme est vivante, si je fais une telle chose!
12 Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
Et David dit à Urie: Demeure ici encore aujourd’hui, et demain je te renverrai. Et Urie demeura à Jérusalem ce jour-là et le lendemain.
13 Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
Et David l’appela, et il mangea et but devant lui, et [David] l’enivra; et il sortit le soir pour se coucher sur son lit avec les serviteurs de son seigneur, et il ne descendit pas dans sa maison.
14 Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
Et il arriva, le matin, que David écrivit une lettre à Joab, et l’envoya par la main d’Urie.
15 A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
Et il écrivit dans la lettre, disant: Placez Urie sur la première ligne au fort de la bataille, et retirez-vous d’auprès de lui, afin qu’il soit frappé et qu’il meure.
16 Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
Et il arriva que, comme Joab surveillait la ville, il plaça Urie à l’endroit où il savait qu’étaient de vaillants hommes.
17 Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
Et les hommes de la ville sortirent et se battirent contre Joab; et il en tomba quelques-uns d’entre le peuple, d’entre les serviteurs de David, et Urie, le Héthien, mourut aussi.
18 Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
Et Joab envoya, et rapporta à David tous les faits du combat.
19 Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
Et il commanda au messager, disant: Quand tu auras achevé de dire au roi tous les faits du combat,
20 wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
s’il arrive que la fureur du roi monte, et qu’il te dise: Pourquoi vous êtes-vous approchés de la ville pour combattre? Ne savez-vous pas qu’on tire de dessus la muraille?
21 Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
Qui frappa Abimélec, fils de Jerubbésheth? N’est-ce pas une femme qui jeta sur lui, de dessus la muraille, une meule tournante, et il en mourut à Thébets? Pourquoi vous êtes-vous approchés de la muraille? – alors tu diras: Ton serviteur Urie, le Héthien, est mort aussi.
22 Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
Et le messager s’en alla; et étant arrivé, il rapporta à David tout ce pour quoi Joab l’avait envoyé.
23 Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
Et le messager dit à David: Les hommes ont eu l’avantage sur nous; ils sont sortis contre nous dans la campagne, et nous les avons chargés jusqu’à l’entrée de la porte;
24 Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
et les archers ont tiré sur tes serviteurs de dessus la muraille, et des serviteurs du roi sont morts, et ton serviteur Urie, le Héthien, est mort aussi.
25 Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
Et David dit au messager: Tu diras ainsi à Joab: Que cela ne soit pas mauvais à tes yeux, car l’épée dévore tantôt ici, tantôt là; renforce le combat contre la ville, et détruis-la. Et toi, encourage-le.
26 Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
Et la femme d’Urie apprit qu’Urie, son mari, était mort, et elle se lamenta sur son mari.
27 Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.
Et quand le deuil fut passé, David envoya, et la recueillit dans sa maison, et elle devint sa femme, et lui enfanta un fils. Mais la chose que David avait faite fut mauvaise aux yeux de l’Éternel.

< 2 Sama’ila 11 >