< 2 Sama’ila 11 >

1 Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
It happened, at the return of the year, at the time when kings go out, that David sent Joab, and his servants with him, and all Israel; and they destroyed the people of Ammon, and besieged Rabbah. But David stayed at Jerusalem.
2 Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
Now it happened one evening that David got up from his bed and walked on the roof of the king's palace; and he saw a woman bathing, and the woman was very beautiful.
3 Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
And David sent and inquired about the woman. And one said, "Isn't this Bathsheba, the daughter of Eliam, the wife of Uriah the Hethite?"
4 Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
So David sent messengers to get her, and she came in to him, and he lay with her. (For she had been purifying herself from her uncleanness.) And she returned to her house.
5 Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
The woman conceived; and she sent and told David, and said, "I'm pregnant."
6 Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
Then David sent to Joab and said, "Send me Uriah the Hethite." So Joab sent Uriah to him.
7 Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
And Uriah came to him, and David asked about the prosperity of Joab, and of the prosperity of the people, and of the prosperity of the war. And he said, "Its well."
8 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
And David said to Uriah, "Go down to your house, and wash your feet." So Uriah went out from the presence of the king, and a gift from the king was sent after him.
9 Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
But Uriah slept at the king's door with his master's servants, and did not go down to his house.
10 Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
And it was reported to David, saying, "Uriah did not go down to his house." So David said to Uriah, "Haven't you come from a journey? Why did you not go down to your house?"
11 Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
And Uriah said to David, "The ark and Israel and Judah are staying in tents; and my lord Joab and the servants of my lord are camped in the open field. Then how can I go to my house to eat and to drink and to lie with my wife? As the LORD lives, and as you live, I will not do this thing."
12 Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
Then David said to Uriah, "Stay here today also, and tomorrow I will let you depart." So Uriah stayed in Jerusalem that day.
13 Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
And the next day David summoned him, and he ate and drank in his presence, and he became drunk. But in the evening he went out and lay on a bed with his master's servants, and did not go down to his house.
14 Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
It happened in the morning, that David wrote a letter to Joab, and sent it by the hand of Uriah.
15 A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
He wrote in the letter, saying, "Send Uriah to the forefront of the hottest battle, and retreat from him, that he may be struck down and die."
16 Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
It happened, when Joab kept watch on the city, that he assigned Uriah to the place where he knew that valiant men were.
17 Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
The men of the city went out, and fought with Joab. Some of the people fell, even of the servants of David; and Uriah the Hethite died also.
18 Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
Then Joab sent and told David all the things concerning the war;
19 Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
and he commanded the messenger, saying, "When you have finished telling all the things concerning the war to the king,
20 wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
if it happens that he becomes angry,
21 Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
then you are to say, 'Your servant Uriah the Hethite is dead also.'"
22 Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
So the messenger of Joab went to the king in Jerusalem and reported to David everything that Joab had told him.
23 Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
The messenger said to David, "The men overpowered us, and came out to us into the field, and when we drove them back to the entrance of the gate,
24 Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
then the arrows came down heavily on your servants from the wall, and some eighteen men of the king's servants died." And the messenger finished the words to the king about the report of the battle. Then David was very angry with Joab, and said to the messenger, "Why did you go so close to the city to fight? Didn't you know you would be struck from the wall? Who struck Abimelech the son of Jerubbaal? Didn't a woman cast an upper millstone on him from the wall so that he died at Thebez? Why did you go so near to the wall?" [Then he said to the king, ] "Also your servant Uriah the Hethite is dead."
25 Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
Then David said to the messenger, "Thus you shall tell Joab, 'Do not let this thing displease you, for the sword devours one as well as another. Make your battle stronger against the city, and overthrow it.' And encourage him."
26 Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
When the wife of Uriah heard that Uriah her husband was dead, she made lamentation for her husband.
27 Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.
When the mourning was past, David sent and took her home to his house, and she became his wife, and bore him a son. But the thing that David had done displeased the LORD.

< 2 Sama’ila 11 >