< 2 Sama’ila 10 >

1 Ana nan sai sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa Hanun kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Après cela, le roi des enfants d'Ammon mourut, et Hanun, son fils, régna à sa place.
2 Dawuda ya yi tunani a ransa ya ce, “Zan yi wa Hanun ɗan Nahash alheri kamar yadda mahaifinsa ya yi mini.” Saboda haka sai Dawuda ya aiki jakadu su yi masa ta’aziyyar mutuwar mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka isa ƙasar Ammonawa,
Et David dit: J'userai de bonté envers Hanun, fils de Nachash, comme son père a usé de bonté envers moi. David envoya donc ses serviteurs pour le consoler au sujet de son père; et les serviteurs de David vinrent au pays des enfants d'Ammon.
3 sai manyan mutanen Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aiko da jakadu su kawo maka ta’aziyya? Ai, wayo ya yi don yă ga asirin birninmu, yă san ƙarfinmu, yă kuma ci mu da yaƙi.”
Mais les chefs d'entre les enfants d'Ammon dirent à Hanun, leur seigneur: Penses-tu que ce soit pour honorer ton père que David t'envoie des consolateurs? N'est-ce pas pour reconnaître exactement la ville, pour l'épier, et la détruire, que David envoie ses serviteurs vers toi?
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda ya aske rabin gemun kowannensu, ya yayyage rigunarsu daidai ɗuwawu, sa’an nan ya sallame su.
Hanun prit donc les serviteurs de David, et leur fit raser la moitié de la barbe, et couper la moitié de leurs habits jusqu'aux hanches; puis il les renvoya.
5 Sa’ad da aka gaya wa Dawuda game da wannan, sai ya aiki manzanni su taryi waɗannan mutanen da aka ci mutuncinsu, gama an wulaƙanta su ƙwarai. Sai sarki ya ce musu, “Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya sāke girma, sa’an nan ku dawo.”
Et cela fut rapporté à David, qui envoya au-devant d'eux; car ces hommes étaient dans une grande confusion. Et le roi leur fit dire: Tenez-vous à Jérico jusqu'à ce que votre barbe ait repoussé, et alors vous reviendrez.
6 Da Ammonawa suka gane cewa Dawuda ya ji fushi da su sosai saboda abin da suka yi, sai suka yi hayar sojojin ƙasar Arameyawa dubu ashirin daga Bet Rehob da Aram-Zoba, suka kuma yi hayar sarkin Ma’aka tare da mutum dubu ɗaya, suka kuma yi hayar maza dubu goma sha biyu daga Tob.
Or les enfants d'Ammon, voyant qu'ils s'étaient mis en mauvaise odeur auprès de David, envoyèrent lever à leur solde vingt mille hommes de pied chez les Syriens de Beth-Réhob et chez les Syriens de Tsoba, et mille hommes chez le roi de Maaca, et douze mille hommes chez les gens de Tob.
7 Da jin haka, Dawuda ya tura Yowab da dukan sojojin yaƙi.
David, l'ayant appris, envoya Joab et toute l'armée, les plus vaillants hommes.
8 Ammonawa suka fita suka ja dāgār yaƙi a ƙofar shiga birninsu, yayinda Aram-Zoba, da na Rehob, da mutane Tob, da kuma na Ma’aka, suka ja tasu dāgār a karkara.
Alors les enfants d'Ammon sortirent, et se rangèrent en bataille à l'entrée de la porte; et les Syriens de Tsoba, et de Réhob, et ceux de Tob et de Maaca, étaient à part dans la campagne.
9 Yowab ya ga cewa an ja masa dāgār yaƙi gaba da baya; saboda haka sai ya zaɓi waɗansu shahararrun sojoji cikin Isra’ila, ya sa su gabza da Arameyawa.
Et Joab, voyant que leur armée était tournée contre lui devant et derrière, choisit d'entre tous ceux d'Israël des hommes d'élite, et les rangea contre les Syriens.
10 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin Abishai ɗan’uwansa, ya sa su gabza da Ammonawa.
Et il donna la conduite du reste du peuple à Abishaï, son frère, qui les rangea contre les enfants d'Ammon.
11 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ƙarfina, sai ku kawo mini gudummawa; amma in Ammonawa suka fi ƙarfinku, sai mu kawo muku gudummawa.
Et il lui dit: Si les Syriens sont plus forts que moi, tu me viendras en aide; et si les enfants d'Ammon sont plus forts que toi, j'irai te délivrer.
12 Ku yi ƙarfin hali, mu kuma yi yaƙi da ƙarfin zuciya saboda mutanenmu da kuma birane Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da yake da kyau a idanunsa.”
Sois vaillant, et combattons vaillamment pour notre peuple et pour les villes de notre Dieu; et que l'Éternel fasse ce qui lui semblera bon.
13 Sa’an nan Yowab da rundunar da take tare da shi suka ci gaba don su gabza da Arameyawa, Arameyawa kuwa suka gudu a gabansa.
Alors Joab et le peuple qui était avec lui, s'approchèrent pour livrer bataille aux Syriens, et ils s'enfuirent devant lui.
14 Da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka ruga da gudu a gaban Abishai, suka shiga cikin birni. Sa’an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙin da ya yi da Ammonawa.
Et les enfants d'Ammon, voyant que les Syriens avaient pris la fuite, s'enfuirent aussi devant Abishaï, et rentrèrent dans la ville. Et Joab s'en retourna de la poursuite des enfants d'Ammon, et vint à Jérusalem.
15 Bayan Arameyawa suka ga Isra’ila ta ci su da yaƙi, sai suka sāke tattara kansu.
Mais les Syriens, voyant qu'ils avaient été battus par ceux d'Israël, se rallièrent.
16 Hadadezer sarkin Zoba ya aika a kawo Arameyawan da suke ƙetaren Kogin Yuferites. Suka iso Helam a ƙarƙashin shugabancin Shobak, shugaban dukan sojojin Hadadezer.
Et Hadarézer envoya, et fit venir les Syriens d'au delà du fleuve, et ils vinrent à Hélam; et Shobac, chef de l'armée de Hadarézer, les conduisait.
17 Da aka gaya wa Dawuda wannan, sai ya tattara dukan Isra’ila, ya ƙetare Urdun, ya je Helam. Arameyawa suka ja dāgār yaƙinsu, suka kara da Dawuda.
Cela fut rapporté à David, qui assembla tout Israël, passa le Jourdain, et vint à Hélam. Et les Syriens se rangèrent en bataille contre David, et combattirent contre lui.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, Dawuda kuwa ya kashe mahayan keken yaƙinsu ɗari bakwai, da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya bugi Shobak, shugaban ƙungiyar sojansu ya kuwa mutu a can.
Mais les Syriens s'enfuirent devant Israël; et David défit sept cents chars des Syriens et quarante mille cavaliers. Il frappa aussi Shobac, chef de leur armée, qui mourut là.
19 Sa’ad da dukan sarakuna waɗanda suke abokan tarayya na Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka yi sulhu da Isra’ilawa, suka kuma zama bayinsu. Wannan ya sa Arameyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudummawa.
Et quand tous les rois, soumis à Hadarézer, virent qu'ils avaient été battus par Israël, ils firent la paix avec les Israélites, et leur furent assujettis; et les Syriens craignirent de donner encore du secours aux enfants d'Ammon.

< 2 Sama’ila 10 >