< 2 Sama’ila 10 >

1 Ana nan sai sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa Hanun kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Now after these things, it happened that the king of the sons of Ammon died, and his son Hanun reigned after him.
2 Dawuda ya yi tunani a ransa ya ce, “Zan yi wa Hanun ɗan Nahash alheri kamar yadda mahaifinsa ya yi mini.” Saboda haka sai Dawuda ya aiki jakadu su yi masa ta’aziyyar mutuwar mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka isa ƙasar Ammonawa,
And David said, “I will show mercy to Hanun, the son of Nahash, just as his father showed mercy to me.” Therefore, David sent consolation to him, by his servants, over the passing of his father. But when the servants of David had arrived in the land of the sons of Ammon,
3 sai manyan mutanen Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aiko da jakadu su kawo maka ta’aziyya? Ai, wayo ya yi don yă ga asirin birninmu, yă san ƙarfinmu, yă kuma ci mu da yaƙi.”
the leaders of the sons of Ammon said to Hanun, their lord: “Do you think it was because of the honor of your father that David sent consolers to you? And did not David send his servants to you, so that he might investigate and explore the city, and so that he might overthrow it?”
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda ya aske rabin gemun kowannensu, ya yayyage rigunarsu daidai ɗuwawu, sa’an nan ya sallame su.
And so, Hanun took the servants of David, and he shaved off one half part of their beards, and he cut their garments at the middle, as far as the buttocks, and he sent them away.
5 Sa’ad da aka gaya wa Dawuda game da wannan, sai ya aiki manzanni su taryi waɗannan mutanen da aka ci mutuncinsu, gama an wulaƙanta su ƙwarai. Sai sarki ya ce musu, “Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya sāke girma, sa’an nan ku dawo.”
And when this had been reported to David, he sent to meet them. And the men were greatly disturbed by shame. And David commanded them, “Remain in Jericho, until your beards grow, and then return.”
6 Da Ammonawa suka gane cewa Dawuda ya ji fushi da su sosai saboda abin da suka yi, sai suka yi hayar sojojin ƙasar Arameyawa dubu ashirin daga Bet Rehob da Aram-Zoba, suka kuma yi hayar sarkin Ma’aka tare da mutum dubu ɗaya, suka kuma yi hayar maza dubu goma sha biyu daga Tob.
Now the sons of Ammon, seeing that they had done an injury to David, sent for, and paid wages to, the Syrians of Rehob, and the Syrians of Zobah, twenty thousand foot soldiers, and from the king of Maacah, one thousand men, and from Tob, twelve thousand men.
7 Da jin haka, Dawuda ya tura Yowab da dukan sojojin yaƙi.
And when David had heard this, he sent Joab and the entire army of warriors.
8 Ammonawa suka fita suka ja dāgār yaƙi a ƙofar shiga birninsu, yayinda Aram-Zoba, da na Rehob, da mutane Tob, da kuma na Ma’aka, suka ja tasu dāgār a karkara.
Then the sons of Ammon went forth, and they positioned their battle line before the very entrance of the gates. But the Syrians of Zobah, and of Rehob, and of Tob, and of Maacah, were by themselves in the field.
9 Yowab ya ga cewa an ja masa dāgār yaƙi gaba da baya; saboda haka sai ya zaɓi waɗansu shahararrun sojoji cikin Isra’ila, ya sa su gabza da Arameyawa.
And so, seeing that the battle had been prepared against him, both facing him and behind, Joab chose some from all of the elect men of Israel, and he set up a battle line opposite the Syrians.
10 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin Abishai ɗan’uwansa, ya sa su gabza da Ammonawa.
But the remaining part of the people he delivered to his brother Abishai, who formed a battle line against the sons of Ammon.
11 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ƙarfina, sai ku kawo mini gudummawa; amma in Ammonawa suka fi ƙarfinku, sai mu kawo muku gudummawa.
And Joab said: “If the Syrians prevail against me, then you shall assist me. But if the sons of Ammon prevail against you, then I will assist you.
12 Ku yi ƙarfin hali, mu kuma yi yaƙi da ƙarfin zuciya saboda mutanenmu da kuma birane Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da yake da kyau a idanunsa.”
Be valiant men. And let us fight on behalf of our people and the city of our God. Then the Lord will do what is good in his own sight.”
13 Sa’an nan Yowab da rundunar da take tare da shi suka ci gaba don su gabza da Arameyawa, Arameyawa kuwa suka gudu a gabansa.
And so, Joab, and the people who were with him, undertook the conflict against the Syrians, who immediately fled before their face.
14 Da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka ruga da gudu a gaban Abishai, suka shiga cikin birni. Sa’an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙin da ya yi da Ammonawa.
Then, seeing that the Syrians had fled, the sons of Ammon themselves also fled from the face of Abishai, and they entered into the city. And Joab returned from the sons of Ammon, and he went to Jerusalem.
15 Bayan Arameyawa suka ga Isra’ila ta ci su da yaƙi, sai suka sāke tattara kansu.
And so, the Syrians, seeing that they had fallen before Israel, gathered themselves together.
16 Hadadezer sarkin Zoba ya aika a kawo Arameyawan da suke ƙetaren Kogin Yuferites. Suka iso Helam a ƙarƙashin shugabancin Shobak, shugaban dukan sojojin Hadadezer.
And Hadadezer sent and brought the Syrians who were beyond the river, and he led in their army. And Shobach, the ruler of the military of Hadadezer, was their leader.
17 Da aka gaya wa Dawuda wannan, sai ya tattara dukan Isra’ila, ya ƙetare Urdun, ya je Helam. Arameyawa suka ja dāgār yaƙinsu, suka kara da Dawuda.
And when this had been reported to David, he drew together all of Israel. And he crossed over the Jordan, and he went to Helam. And the Syrians formed a battle line opposite David, and they fought against him.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, Dawuda kuwa ya kashe mahayan keken yaƙinsu ɗari bakwai, da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya bugi Shobak, shugaban ƙungiyar sojansu ya kuwa mutu a can.
And the Syrians fled before the face of Israel. And David killed, among the Syrians, the men of seven hundred chariots, and forty thousand horsemen. And he struck down Shobach, the leader of the military, who immediately died.
19 Sa’ad da dukan sarakuna waɗanda suke abokan tarayya na Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka yi sulhu da Isra’ilawa, suka kuma zama bayinsu. Wannan ya sa Arameyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudummawa.
Then all the kings who were in the reinforcements of Hadadezer, seeing themselves to be defeated by Israel, were very afraid and they fled: fifty-eight thousand men before Israel. And they made peace with Israel, and they served them. And the Syrians were afraid to offer assistance to the sons of Ammon anymore.

< 2 Sama’ila 10 >