< 2 Sama’ila 10 >

1 Ana nan sai sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa Hanun kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
And it came to pass after this, that the king of the children of Ammon died, and Hanun his son reigned in his stead.
2 Dawuda ya yi tunani a ransa ya ce, “Zan yi wa Hanun ɗan Nahash alheri kamar yadda mahaifinsa ya yi mini.” Saboda haka sai Dawuda ya aiki jakadu su yi masa ta’aziyyar mutuwar mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka isa ƙasar Ammonawa,
And David said, I will show kindness unto Hanun the son of Nahash, as his father showed kindness unto me. So David sent by his servants to comfort him concerning his father. And David’s servants came into the land of the children of Ammon.
3 sai manyan mutanen Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aiko da jakadu su kawo maka ta’aziyya? Ai, wayo ya yi don yă ga asirin birninmu, yă san ƙarfinmu, yă kuma ci mu da yaƙi.”
But the princes of the children of Ammon said unto Hanun their lord, Thinkest thou that David doth honor thy father, in that he hath sent comforters unto thee? hath not David sent his servants unto thee to search the city, and to spy it out, and to overthrow it?
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda ya aske rabin gemun kowannensu, ya yayyage rigunarsu daidai ɗuwawu, sa’an nan ya sallame su.
So Hanun took David’s servants, and shaved off the one half of their beards, and cut off their garments in the middle, even to their buttocks, and sent them away.
5 Sa’ad da aka gaya wa Dawuda game da wannan, sai ya aiki manzanni su taryi waɗannan mutanen da aka ci mutuncinsu, gama an wulaƙanta su ƙwarai. Sai sarki ya ce musu, “Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya sāke girma, sa’an nan ku dawo.”
When they told it unto David, he sent to meet them; for the men were greatly ashamed. And the king said, Tarry at Jericho until your beards be grown, and then return.
6 Da Ammonawa suka gane cewa Dawuda ya ji fushi da su sosai saboda abin da suka yi, sai suka yi hayar sojojin ƙasar Arameyawa dubu ashirin daga Bet Rehob da Aram-Zoba, suka kuma yi hayar sarkin Ma’aka tare da mutum dubu ɗaya, suka kuma yi hayar maza dubu goma sha biyu daga Tob.
And when the children of Ammon saw that they were become odious to David, the children of Ammon sent and hired the Syrians of Beth-rehob, and the Syrians of Zobah, twenty thousand footmen, and the king of Maacah with a thousand men, and the men of Tob twelve thousand men.
7 Da jin haka, Dawuda ya tura Yowab da dukan sojojin yaƙi.
And when David heard of it, he sent Joab, and all the host of the mighty men.
8 Ammonawa suka fita suka ja dāgār yaƙi a ƙofar shiga birninsu, yayinda Aram-Zoba, da na Rehob, da mutane Tob, da kuma na Ma’aka, suka ja tasu dāgār a karkara.
And the children of Ammon came out, and put the battle in array at the entrance of the gate: and the Syrians of Zobah and of Rehob, and the men of Tob and Maacah, were by themselves in the field.
9 Yowab ya ga cewa an ja masa dāgār yaƙi gaba da baya; saboda haka sai ya zaɓi waɗansu shahararrun sojoji cikin Isra’ila, ya sa su gabza da Arameyawa.
Now when Joab saw that the battle was set against him before and behind, he chose of all the choice men of Israel, and put them in array against the Syrians:
10 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin Abishai ɗan’uwansa, ya sa su gabza da Ammonawa.
and the rest of the people he committed into the hand of Abishai his brother; and he put them in array against the children of Ammon.
11 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ƙarfina, sai ku kawo mini gudummawa; amma in Ammonawa suka fi ƙarfinku, sai mu kawo muku gudummawa.
And he said, If the Syrians be too strong for me, then thou shalt help me; but if the children of Ammon be too strong for thee, then I will come and help thee.
12 Ku yi ƙarfin hali, mu kuma yi yaƙi da ƙarfin zuciya saboda mutanenmu da kuma birane Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da yake da kyau a idanunsa.”
Be of good courage, and let us play the man for our people, and for the cities of our God: and Jehovah do that which seemeth him good.
13 Sa’an nan Yowab da rundunar da take tare da shi suka ci gaba don su gabza da Arameyawa, Arameyawa kuwa suka gudu a gabansa.
So Joab and the people that were with him drew nigh unto the battle against the Syrians: and they fled before him.
14 Da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka ruga da gudu a gaban Abishai, suka shiga cikin birni. Sa’an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙin da ya yi da Ammonawa.
And when the children of Ammon saw that the Syrians were fled, they likewise fled before Abishai, and entered into the city. Then Joab returned from the children of Ammon, and came to Jerusalem.
15 Bayan Arameyawa suka ga Isra’ila ta ci su da yaƙi, sai suka sāke tattara kansu.
And when the Syrians saw that they were put to the worse before Israel, they gathered themselves together.
16 Hadadezer sarkin Zoba ya aika a kawo Arameyawan da suke ƙetaren Kogin Yuferites. Suka iso Helam a ƙarƙashin shugabancin Shobak, shugaban dukan sojojin Hadadezer.
And Hadarezer sent, and brought out the Syrians that were beyond the River: and they came to Helam, with Shobach the captain of the host of Hadarezer at their head.
17 Da aka gaya wa Dawuda wannan, sai ya tattara dukan Isra’ila, ya ƙetare Urdun, ya je Helam. Arameyawa suka ja dāgār yaƙinsu, suka kara da Dawuda.
And it was told David; and he gathered all Israel together, and passed over the Jordan, and came to Helam. And the Syrians set themselves in array against David, and fought with him.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, Dawuda kuwa ya kashe mahayan keken yaƙinsu ɗari bakwai, da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya bugi Shobak, shugaban ƙungiyar sojansu ya kuwa mutu a can.
And the Syrians fled before Israel; and David slew of the Syrians [the men of] seven hundred chariots, and forty thousand horsemen, and smote Shobach the captain of their host, so that he died there.
19 Sa’ad da dukan sarakuna waɗanda suke abokan tarayya na Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka yi sulhu da Isra’ilawa, suka kuma zama bayinsu. Wannan ya sa Arameyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudummawa.
And when all the kings that were servants to Hadarezer saw that they were put to the worse before Israel, they made peace with Israel, and served them. So the Syrians feared to help the children of Ammon any more.

< 2 Sama’ila 10 >