< 2 Sama’ila 10 >

1 Ana nan sai sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa Hanun kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Og det skete derefter, at Ammons Børns Konge døde, og Hanon, hans Søn, blev Konge i hans Sted.
2 Dawuda ya yi tunani a ransa ya ce, “Zan yi wa Hanun ɗan Nahash alheri kamar yadda mahaifinsa ya yi mini.” Saboda haka sai Dawuda ya aiki jakadu su yi masa ta’aziyyar mutuwar mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka isa ƙasar Ammonawa,
Da sagde David: Jeg vil gøre Miskundhed imod Hanon, Nahas's Søn, ligesom hans Fader gjorde Miskundhed imod mig; og David sendte hen for at trøste ham ved sine Tjenere over hans Fader, og Davids Tjenere kom til Ammons Børns Land.
3 sai manyan mutanen Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aiko da jakadu su kawo maka ta’aziyya? Ai, wayo ya yi don yă ga asirin birninmu, yă san ƙarfinmu, yă kuma ci mu da yaƙi.”
Da sagde Ammons Børns Fyrster til Hanon, deres Herre: Synes det for dine Øjne, at David ærer din Fader, ved at han sender dig Trøstere? mon David ikke har sendt sine Tjenere til dig for at udforske Staden og for at bespejde den og omstyrte den?
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda ya aske rabin gemun kowannensu, ya yayyage rigunarsu daidai ɗuwawu, sa’an nan ya sallame su.
Da tog Hanon Davids Tjenere og lod rage Halvdelen af deres Skæg og afskar Halvdelen af deres Klæder indtil Sædet og lod dem fare.
5 Sa’ad da aka gaya wa Dawuda game da wannan, sai ya aiki manzanni su taryi waɗannan mutanen da aka ci mutuncinsu, gama an wulaƙanta su ƙwarai. Sai sarki ya ce musu, “Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya sāke girma, sa’an nan ku dawo.”
Der de gave David det til Kende, da sendte han dem et Bud i Møde; thi Mændene vare saare forhaanede; og Kongen lod sige: Bliver i Jeriko, indtil eders Skæg vokser, og kommer da tilbage.
6 Da Ammonawa suka gane cewa Dawuda ya ji fushi da su sosai saboda abin da suka yi, sai suka yi hayar sojojin ƙasar Arameyawa dubu ashirin daga Bet Rehob da Aram-Zoba, suka kuma yi hayar sarkin Ma’aka tare da mutum dubu ɗaya, suka kuma yi hayar maza dubu goma sha biyu daga Tob.
Der Ammons Børn saa, at de havde gjort sig forhadte for David, da sendte Ammons Børn hen og lejede Syrerne af Rekobs Hus og Syrerne af Zoba, tyve Tusinde Mand Fodfolk, og tusinde Mand af Kongen af Maaka og Mændene af Tob, tolv Tusinde Mand.
7 Da jin haka, Dawuda ya tura Yowab da dukan sojojin yaƙi.
Der David hørte det, da udsendte han Joab og de vældiges ganske Hær.
8 Ammonawa suka fita suka ja dāgār yaƙi a ƙofar shiga birninsu, yayinda Aram-Zoba, da na Rehob, da mutane Tob, da kuma na Ma’aka, suka ja tasu dāgār a karkara.
Og Ammons Børn droge ud og opstillede deres Slagorden ved Indgangen til Porten; men Syrerne af Zoba og Rekob og Mændene af Tob og Maaka stode for sig alene paa Marken.
9 Yowab ya ga cewa an ja masa dāgār yaƙi gaba da baya; saboda haka sai ya zaɓi waɗansu shahararrun sojoji cikin Isra’ila, ya sa su gabza da Arameyawa.
Der Joab saa, at Krigen truede ham for og bagfra, da udvalgte han nogle af alle de udvalgte i Israel og opstillede sig imod Syrerne.
10 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin Abishai ɗan’uwansa, ya sa su gabza da Ammonawa.
Og det øvrige Folk gav han under sin Broder Abisajs Haand, og denne opstillede sig imod Ammons Børn.
11 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ƙarfina, sai ku kawo mini gudummawa; amma in Ammonawa suka fi ƙarfinku, sai mu kawo muku gudummawa.
Og han sagde: Dersom Syrerne blive mig for stærke, da skal du være mig til Hjælp; men dersom Ammons Børn blive dig for stærke, da vil jeg komme til at hjælpe dig.
12 Ku yi ƙarfin hali, mu kuma yi yaƙi da ƙarfin zuciya saboda mutanenmu da kuma birane Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da yake da kyau a idanunsa.”
Vær frimodig, og lader os være frimodige for vort Folk og for vor Guds Stæder; men Herren gøre, hvad som er godt for hans Øjne.
13 Sa’an nan Yowab da rundunar da take tare da shi suka ci gaba don su gabza da Arameyawa, Arameyawa kuwa suka gudu a gabansa.
Da drog Joab frem og det Folk, som var hos ham, til Kamp imod Syrerne, og de flyede for hans Ansigt.
14 Da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka ruga da gudu a gaban Abishai, suka shiga cikin birni. Sa’an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙin da ya yi da Ammonawa.
Der Ammons Børn saa, at Syrerne flyede, flyede de og for Abisajs Ansigt og kom i Staden. Saa vendte Joab tilbage fra Ammons Børn og kom til Jerusalem.
15 Bayan Arameyawa suka ga Isra’ila ta ci su da yaƙi, sai suka sāke tattara kansu.
Og der Syrerne saa, at de vare slagne for Israels Ansigt, da samledes de til Hobe.
16 Hadadezer sarkin Zoba ya aika a kawo Arameyawan da suke ƙetaren Kogin Yuferites. Suka iso Helam a ƙarƙashin shugabancin Shobak, shugaban dukan sojojin Hadadezer.
Og Hadad-Eser sendte hen og førte Syrerne, som vare paa hin Side Floden, frem, og de kom til Helam; og Sobak, som var Hadad-Esers Stridshøvedsmand, var i Spidsen for dem.
17 Da aka gaya wa Dawuda wannan, sai ya tattara dukan Isra’ila, ya ƙetare Urdun, ya je Helam. Arameyawa suka ja dāgār yaƙinsu, suka kara da Dawuda.
Der det blev David tilkendegivet, da samlede han al Israel og drog over Jordanen og kom til Helam, og Syrerne opstillede sig imod David og strede med ham.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, Dawuda kuwa ya kashe mahayan keken yaƙinsu ɗari bakwai, da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya bugi Shobak, shugaban ƙungiyar sojansu ya kuwa mutu a can.
Men Syrerne flyede for Israels Ansigt, og David ødelagde blandt Syrerne syv Hundrede Vogne og fyrretyve Tusinde Ryttere, tillige slog han og Sobak, hans Stridshøvedsmand, saa at denne døde der.
19 Sa’ad da dukan sarakuna waɗanda suke abokan tarayya na Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka yi sulhu da Isra’ilawa, suka kuma zama bayinsu. Wannan ya sa Arameyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudummawa.
Der alle de Konger, som vare Hadad-Esers Tjenere, saa, at de vare slagne for Israels Ansigt, da gjorde de Fred med Israel og tjente dem; og Syrerne frygtede for at hjælpe Ammons Børn ydermere.

< 2 Sama’ila 10 >