< 2 Sama’ila 10 >

1 Ana nan sai sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa Hanun kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
此後,阿孟子民的君王死了,他的兒子哈農繼位為王。
2 Dawuda ya yi tunani a ransa ya ce, “Zan yi wa Hanun ɗan Nahash alheri kamar yadda mahaifinsa ya yi mini.” Saboda haka sai Dawuda ya aiki jakadu su yi masa ta’aziyyar mutuwar mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka isa ƙasar Ammonawa,
達味心想:「我要善待納哈士的兒子哈農,像他父親善待我一樣。」於是達味派自己的臣僕去慰問他,追悼他的父親。當達味的臣僕來到阿孟子民國內時,
3 sai manyan mutanen Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aiko da jakadu su kawo maka ta’aziyya? Ai, wayo ya yi don yă ga asirin birninmu, yă san ƙarfinmu, yă kuma ci mu da yaƙi.”
阿孟子民的公卿,對他們的主上哈農說:「達味派人來慰問你,你想他是為尊敬你的父親嗎﹖達味派臣僕到你這裏來,豈不是來調查、探聽、破壞城池嗎﹖」
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda ya aske rabin gemun kowannensu, ya yayyage rigunarsu daidai ɗuwawu, sa’an nan ya sallame su.
哈農遂拿住達味的臣僕,將他們的鬍鬚剃去一半,又將他們下半截衣服割去,直到臀部;然後放他們走了。
5 Sa’ad da aka gaya wa Dawuda game da wannan, sai ya aiki manzanni su taryi waɗannan mutanen da aka ci mutuncinsu, gama an wulaƙanta su ƙwarai. Sai sarki ya ce musu, “Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya sāke girma, sa’an nan ku dawo.”
有人把這事告訴了達味,王遂打發人去迎接他們,因為這些人很覺羞恥;王便吩咐他們說:「你們暫且留在耶里哥,等鬍鬚長起後再回來。」
6 Da Ammonawa suka gane cewa Dawuda ya ji fushi da su sosai saboda abin da suka yi, sai suka yi hayar sojojin ƙasar Arameyawa dubu ashirin daga Bet Rehob da Aram-Zoba, suka kuma yi hayar sarkin Ma’aka tare da mutum dubu ɗaya, suka kuma yi hayar maza dubu goma sha biyu daga Tob.
阿孟子民見自己在達味跟前惹下仇恨,便遣人去,向貝特勒曷布和祚巴的阿蘭人僱了兩萬步兵,向瑪阿加君王僱了一千人,向托布人僱了一萬二千人。
7 Da jin haka, Dawuda ya tura Yowab da dukan sojojin yaƙi.
達味聽說這事,便派出約阿布和全隊士兵和勇士。
8 Ammonawa suka fita suka ja dāgār yaƙi a ƙofar shiga birninsu, yayinda Aram-Zoba, da na Rehob, da mutane Tob, da kuma na Ma’aka, suka ja tasu dāgār a karkara.
阿孟子民出來,在城門前擺了陣,祚巴和勒曷布的阿蘭人和托布人與瑪阿加人,分別在田野間擺了陣。
9 Yowab ya ga cewa an ja masa dāgār yaƙi gaba da baya; saboda haka sai ya zaɓi waɗansu shahararrun sojoji cikin Isra’ila, ya sa su gabza da Arameyawa.
約阿布見自己前後受敵,就由以色列勁旅中,選一隊精兵擺陣進攻阿蘭人,
10 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin Abishai ɗan’uwansa, ya sa su gabza da Ammonawa.
將其餘的軍隊,交給自己的兄弟阿彼瑟指揮,叫他列陣進攻阿孟子民,
11 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ƙarfina, sai ku kawo mini gudummawa; amma in Ammonawa suka fi ƙarfinku, sai mu kawo muku gudummawa.
並對他說:「若我打不下阿蘭人,你就來援助我;若你打不下阿孟子民,我就來援助你。
12 Ku yi ƙarfin hali, mu kuma yi yaƙi da ƙarfin zuciya saboda mutanenmu da kuma birane Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da yake da kyau a idanunsa.”
要勇敢奮鬥,為了我們的民族,為了我們天主的城池,我們應奮鬥! 願上主成就他認為好的事! 」
13 Sa’an nan Yowab da rundunar da take tare da shi suka ci gaba don su gabza da Arameyawa, Arameyawa kuwa suka gudu a gabansa.
然後約阿布和跟隨他的軍隊,向前進攻阿蘭人,阿蘭人就在他們前逃走了。
14 Da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka ruga da gudu a gaban Abishai, suka shiga cikin birni. Sa’an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙin da ya yi da Ammonawa.
阿孟子民見阿蘭人逃走,他們也在阿彼瑟前逃走,退入城中。約阿布便不再進攻阿孟子民,回了耶路撒冷。
15 Bayan Arameyawa suka ga Isra’ila ta ci su da yaƙi, sai suka sāke tattara kansu.
阿蘭人見自己為以色列打敗,便再聯合起來。
16 Hadadezer sarkin Zoba ya aika a kawo Arameyawan da suke ƙetaren Kogin Yuferites. Suka iso Helam a ƙarƙashin shugabancin Shobak, shugaban dukan sojojin Hadadezer.
哈達德則爾派人去,將大河那邊的阿蘭人也調來,都到了赫藍,由哈達德則爾的元帥芍巴客率領。
17 Da aka gaya wa Dawuda wannan, sai ya tattara dukan Isra’ila, ya ƙetare Urdun, ya je Helam. Arameyawa suka ja dāgār yaƙinsu, suka kara da Dawuda.
達味一得了情報,就調集所有的以色列人,渡過約但河,來到赫藍。阿蘭人遂列陣進攻達味,與他交戰。
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, Dawuda kuwa ya kashe mahayan keken yaƙinsu ɗari bakwai, da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya bugi Shobak, shugaban ƙungiyar sojansu ya kuwa mutu a can.
阿蘭人在以色列面前潰退。達味擊殺了阿蘭人的七百匹拉車的馬,和四萬馬兵;又攻擊了他們的元帥芍巴客,他便死在那裏。
19 Sa’ad da dukan sarakuna waɗanda suke abokan tarayya na Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka yi sulhu da Isra’ilawa, suka kuma zama bayinsu. Wannan ya sa Arameyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudummawa.
所有臣屬哈達德則爾的王子,一見自己敗於以色列,便與以色列講和,臣服於他們;從此阿蘭人再不敢援助阿孟子民了。

< 2 Sama’ila 10 >