< 2 Sama’ila 1 >

1 Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
Saul'un ölümünden sonra Amalekliler'e karşı kazandığı zaferden dönen Davut Ziklak'ta iki gün kaldı.
2 A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
Üçüncü gün, Saul'un ordugahından giysileri yırtılmış, başı toz toprak içinde bir adam geldi. Adam Davut'a yaklaşınca önünde yere kapandı.
3 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
Davut, “Nereden geliyorsun?” diye sordu. Adam, “İsrail ordugahından kaçıp kurtuldum” dedi.
4 Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
Davut, “Ne oldu? Bana anlat” dedi. Adam askerlerin savaş alanından kaçtığını, birçoğunun düşüp öldüğünü, Saul'la oğlu Yonatan'ın da ölüler arasında olduğunu anlattı.
5 Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
Davut, kendisine haberi veren genç adama, “Saul'la oğlu Yonatan'ın öldüğünü nereden biliyorsun?” diye sordu.
6 Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
Genç adam şöyle yanıtladı: “Bir rastlantı sonucu Gilboa Dağı'ndaydım. Saul mızrağına dayanmıştı. Atlılarla savaş arabaları ona doğru yaklaşıyordu.
7 Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
Saul arkasına dönüp beni görünce seslendi. Ben de, ‘Buyrun, buradayım’ dedim.
8 “Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
“Saul, ‘Sen kimsin?’ diye sordu. “‘Ben bir Amalekli'yim’ diye yanıtladım.
9 “Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
“Saul, ‘Ne olur üstüme var ve beni öldür!’ dedi, ‘Çünkü çektiğim acılardan kurtulmak istiyorum.’
10 “Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
Bu yüzden varıp onu öldürdüm. Çünkü yere düştükten sonra yaşayamayacağını biliyordum. Başındaki taçla kolundaki bileziği aldım ve onları buraya, efendime getirdim.”
11 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
Bunun üzerine Davut'la yanındakiler giysilerini yırttılar.
12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
Kılıçtan geçirilen Saul, oğlu Yonatan ve RAB'bin halkı olan İsrailliler için akşama dek yas tutup ağladılar, oruç tuttular.
13 Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
Davut, kendisine haber getiren genç adama, “Nerelisin?” diye sordu. Adam, “Ben yabancıyım, bir Amalekli'nin oğluyum” dedi.
14 Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
Davut, “RAB'bin meshettiği kişiye el kaldırıp onu yok etmekten korkmadın mı?” diye sordu.
15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
Sonra adamlarından birini çağırıp, “Git, öldür onu!” diye buyurdu. Böylece adam Amalekli'yi vurup öldürdü.
16 Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
Davut Amalekli'ye, “Kanından sen kendin sorumlusun” demişti, “Çünkü ‘RAB'bin meshettiği kişiyi ben öldürdüm’ demekle kendine karşı ağzınla tanıklıkta bulundun.”
17 Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
Davut Saul'la oğlu Yonatan için ağıt yaktı.
18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
Sonra Yaşar Kitabı'nda yazılan Yay adındaki ağıtın Yahuda halkına öğretilmesini buyurdu:
19 “Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
“Ey İsrail, senin yüceliğin yüksek tepelerinde yok oldu! Güçlüler nasıl da yere serildi!
20 “Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
Haberi ne Gat'a duyurun, Ne de Aşkelon sokaklarında yayın. Öyle ki, ne Filistliler'in kızları sevinsin, Ne de sünnetsizlerin kızları coşsun.
21 “Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
Ey Gilboa dağları, Üzerinize ne çiy ne de yağmur düşsün. Ürün veren tarlalarınız olmasın. Çünkü güçlünün kalkanı, Bir daha yağ sürülmeyecek olan Saul'un kalkanı Orada bir yana atıldı!
22 “Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
Yonatan'ın yayı yere serilmişlerin kanından, Yiğitlerin bedenlerinden hiç geri çekilmedi. Saul'un kılıcı hiç boşa savrulmadı.
23 Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
Saul'la Yonatan tatlı ve sevimliydiler, Yaşamda da ölümde de ayrılmadılar. Kartallardan daha çevik, Aslanlardan daha güçlüydüler.
24 “Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
Ey İsrail kızları! Sizi al renkli, süslü giysilerle donatan, Giysinizi altın süslerle bezeyen Saul için ağlayın!
25 “Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
Güçlüler nasıl da yere serildi savaşta! Yonatan senin yüksek tepelerinde ölü yatıyor.
26 Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
Senin için üzgünüm, kardeşim Yonatan. Benim için çok değerliydin. Sevgin kadın sevgisinden daha üstündü.
27 “Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”
Güçlüler nasıl da yere serildi! Savaş silahları yok oldu!”

< 2 Sama’ila 1 >