< 2 Sama’ila 1 >

1 Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
And it cometh to pass, after the death of Saul, that David hath returned from smiting the Amalekite, and David dwelleth in Ziklag two days,
2 A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
and it cometh to pass, on the third day, that lo, a man hath come in out of the camp from Saul, and his garments [are] rent, and earth on his head; and it cometh to pass, in his coming in unto David, that he falleth to the earth, and doth obeisance.
3 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
And David saith to him, 'Whence comest thou?' and he saith unto him, 'Out of the camp of Israel I have escaped.'
4 Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
And David saith unto him, 'What hath been the matter? declare, I pray thee, to me.' And he saith, that 'The people hath fled from the battle, and also a multitude hath fallen of the people, and they die; and also Saul and Jonathan his son have died.'
5 Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
And David saith unto the youth who is declaring [it] to him, 'How hast thou known that Saul and Jonathan his son [are] dead?'
6 Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
And the youth who is declaring [it] to him saith, I happened to meet in mount Gilboa, and lo, Saul is leaning on his spear; and lo, the chariots and those possessing horses have followed him;
7 Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
and he turneth behind him, and seeth me, and calleth unto me, and I say, Here [am] I.
8 “Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
And he saith to me, Who [art] thou? and I say unto him, An Amalekite I [am].'
9 “Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
'And he saith unto me, Stand, I pray thee, over me, and put me to death, for seized me hath the arrow, for all my soul [is] still in me.
10 “Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
And I stand over him, and put him to death, for I knew that he doth not live after his falling, and I take the crown which [is] on his head, and the bracelet which [is] on his arm, and bring them in unto my lord hither.'
11 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
And David taketh hold on his garments, and rendeth them, and also all the men who [are] with him,
12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
and they mourn, and weep, and fast till the evening, for Saul, and for Jonathan his son, and for the people of Jehovah, and for the house of Israel, because they have fallen by the sword.
13 Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
And David saith unto the youth who is declaring [it] to him, 'Whence [art] thou?' and he saith, 'Son of a sojourner, an Amalekite, I [am].'
14 Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
And David saith unto him, 'How wast thou not afraid to put forth thy hand to destroy the anointed of Jehovah?'
15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
And David calleth to one of the youths, and saith, 'Draw nigh — fall upon him;' and he smiteth him, and he dieth;
16 Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
and David saith unto him, 'Thy blood [is] on thine own head, for thy mouth hath testified against thee, saying, I — I put to death the anointed of Jehovah.'
17 Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
And David lamenteth with this lamentation over Saul, and over Jonathan his son;
18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
and he saith to teach the sons of Judah 'The Bow;' lo, it is written on the book of the Upright: —
19 “Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
'The Roebuck, O Israel, On thy high places [is] wounded; How have the mighty fallen!
20 “Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
Declare [it] not in Gath, Proclaim not the tidings in the streets of Ashkelon, Lest they rejoice — The daughters of the Philistines, Lest they exult — The daughters of the Uncircumcised!
21 “Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
Mountains of Gilboa! No dew nor rain be on you, And fields of heave-offerings! For there hath become loathsome The shield of the mighty, The shield of Saul — without the anointed with oil.
22 “Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
From the blood of the wounded, From the fat of the mighty, The bow of Jonathan Hath not turned backward; And the sword of Saul doth not return empty.
23 Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
Saul and Jonathan! They are loved and pleasant in their lives, And in their death they have not been parted. Than eagles they have been lighter, Than lions they have been mightier!
24 “Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
Daughters of Israel! for Saul weep ye, Who is clothing you [in] scarlet with delights. Who is lifting up ornaments of gold on your clothing.
25 “Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
How have the mighty fallen In the midst of the battle! Jonathan! on thy high places wounded!
26 Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
I am in distress for thee, my brother Jonathan, Very pleasant wast thou to me; Wonderful was thy love to me, Above the love of women!
27 “Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”
How have the mighty fallen, Yea, the weapons of war perish!'

< 2 Sama’ila 1 >