< 2 Sama’ila 1 >
1 Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
Forsothe it was doon, after that Saul was deed, that Dauid turnede ayen fro the sleyng of Amalech, and dwellide twei daies in Sichelech.
2 A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
Forsothe in the thridde dai a man apperide, comynge fro the castels of Saul with the cloth to-rent, and his heed spreynt with dust; and as he cam to Dauid, he felde on his face, and worschipide.
3 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
And Dauid seide to hym, Fro whennus comest thou? Which seide to Dauid, Y fledde fro the castels of Israel.
4 Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
And Dauid seide to hym, What is the word which is doon; schewe thou to me. And he seide, The puple fledde fro the batel, and many of the puple felden, and ben deed; but also Saul, and Jonathas, his sonne, perischyden.
5 Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
And Dauid seide to the yong man, that telde to hym, Wherof woost thou, that Saul is deed, and Jonathas, his sonne?
6 Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
And the yong man seide, that telde to hym, Bi hap Y cam in to the hil of Gelboe, and Saul lenyde on his spere; forsothe charis and knyytis neiyiden to hym;
7 Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
and he turnede bihynde his bak, `and siy me, and clepide. To whom whanne Y hadde answeride, Y am present; he seide to me, Who art thou?
8 “Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
And Y seide to hym, Y am a man of Amalech.
9 “Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
And he spak to me, Stonde thou on me, and sle me; for angwischis holden me, and yit al my lijf is in me.
10 “Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
And Y stood on hym, and Y killide hym; for Y wiste that he myyte not lyue aftir the fallyng; and Y took the diademe, that was in his heed, and the bye fro his arm, and Y brouyte hidur to thee, my lord.
11 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
Forsothe Dauid took and to-rente hise clothis, and the men that weren with hym;
12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
and thei weiliden, and wepten, and fastiden `til to euentid, on Saul, and Jonathas, his sone, and on the puple of the Lord, and on the hows of Israel, for thei hadden feld bi swerd.
13 Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
And Dauid seide to the yong man, that telde to him, Of whennus art thou? And he answeride, Y am the sone of a man comelyng, of a man of Amalech.
14 Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
And Dauid seide to him, Whi dreddist thou not to sende thine hond, that thou schuldist sle the crist of the Lord?
15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
And Dauid clepide oon of hise children, and seide, Go thou, and falle on hym. Which smoot that yong man, and he was deed.
16 Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
And Dauid seide to hym, Thi blood be on thin heed; for thi mouth spak ayens thee, and seide, Y killide the crist of the Lord.
17 Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
Forsooth Dauid biweilide sych a weilyng on Saul, and on Jonathas, his sone;
18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
and comaundide, that thei schulden teche the sones of Juda weilyng, as it is writun in the Book of Just Men. And Dauid seyde, Israel, biholde thou, for these men that ben deed, woundid on thin hiye placis;
19 “Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
the noble men of Israel ben slayn on thin hillis.
20 “Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
Hou felden stronge men? nyle ye telle in Geth, nether telle ye in the weilottis of Ascolon; lest perauenture the douytris of Filisteis be glad, lest the douytris of vncircumcidid men `be glad.
21 “Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
Hillis of Gelboe, neither dew nethir reyn come on you, nether the feeldis of firste fruytis be; for the scheeld of stronge men was cast awey there, the scheeld of Saul, as `if he were not anoyntid with oile.
22 “Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
Of the blood of slayn men, of the fatnesse of strong men, the arewe of Jonathas yede neuer abak, and the swerd of Saul turnede not ayen void.
23 Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
Saul and Jonathas amyable, and fair in her lijf, weren not departid also in deeth; thei weren swiftere than eglis, strongere than liouns.
24 “Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
Douytris of Israel, wepe ye on Saul, that clothide you with fyn reed colourid in delicis, that yaf goldun ournementis to youre atyre.
25 “Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
Hou `felden doun stronge men in batel?
26 Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
Jonathas was slayn in the hiye places. Y make sorewe on thee, my brother Jonathas, ful fair, `and amyable more than the loue of wymmen; as a modir loueth oon aloone sone, so Y louyde thee.
27 “Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”
Hou therfor `felden doun stronge men, and armeris of batel perischide?