< 2 Sama’ila 1 >
1 Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
After the death of Saul, when Dauid was returned from the slaughter of the Amalekites and had beene two dayes in Ziklag,
2 A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
Behold, a man came the third day out of the host from Saul with his clothes rent, and earth vpon his head: and when hee came to Dauid, he fell to the earth, and did obeisance.
3 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
Then Dauid saide vnto him, Whence commest thou? And he said vnto him, Out of the host of Israel I am escaped.
4 Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
And Dauid saide vnto him, What is done? I pray thee, tell me. Then he said, that the people is fled from the battel, and many of the people are ouerthrowen, and dead, and also Saul and Ionathan his sonne are dead.
5 Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
And Dauid saide vnto the yong man that tolde it him, Howe knowest thou that Saul and Ionathan his sonne be dead?
6 Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
Then the yong man that tolde him, answered, As I came to mount Gilboa, behold, Saul leaned vpon his speare, and loe, the charets and horsemen followed hard after him.
7 Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
And when he looked backe, he saw me, and called me. And I answered, Here am I.
8 “Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
And he said vnto me, Who art thou? And I answered him, I am an Amalekite.
9 “Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
Then saide hee vnto me, I pray thee come vpon mee, and slay me: for anguish is come vpon me, because my life is yet whole in me.
10 “Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
So I came vpon him, and slewe him, and because I was sure that hee coulde not liue, after that hee had fallen, I tooke the crowne that was vpon his head, and the bracelet that was on his arme, and brought them hither vnto my lord.
11 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
Then Dauid tooke hold on his clothes, and rent them, and likewise al the men that were with him.
12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
And they mourned and wept, and fasted vntil euen, for Saul and for Ionathan his sonne, and for the people of the Lord, and for the house of Israel, because they were slaine with the sword.
13 Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
Afterward Dauid saide vnto the yong man that tolde it him, Whence art thou? And hee answered, I am the sonne of a stranger an Amalekite.
14 Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
And Dauid said vnto him, How wast thou not afrayd, to put forth thine hand to destroy the Anoynted of the Lord?
15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
Then Dauid called one of his yong men, and said, Goe neere, and fall vpon him. And hee smote him that he dyed.
16 Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
Then said Dauid vnto him, Thy blood be vpon thine owne head: for thine owne mouth hath testified against thee, saying, I haue slaine the Lords Anoynted.
17 Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
Then Dauid mourned with this lamentation ouer Saul, and ouer Ionathan his sonne,
18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
(Also he bade them teach the children of Iudah to shoote, as it is written in the booke of Iasher)
19 “Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
O noble Israel, hee is slane vpon thy hie places: how are the mightie ouerthrowen!
20 “Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
Tell it not in Gath, nor publish it in the streetes of Ashkelon, lest the daughters of the Philistims reioyce, lest the daughters of the vncircumcised triumph.
21 “Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
Ye mountaines of Gilboa, vpon you be neither dewe nor raine, nor be there fieldes of offrings: for there the shielde of the mightie is cast downe, the shielde of Saul, as though he had not bene anointed with oyle.
22 “Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
The bow of Ionathan neuer turned backe, neither did the sword of Saul returne emptie from the blood of the slaine, and from the fatte of the mightie.
23 Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
Saul and Ionathan were louely and pleasant in their liues, and in their deaths they were not deuided: they were swifter then eagles, they were stronger then lions.
24 “Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
Yee daughters of Israel, weepe for Saul, which clothed you in skarlet, with pleasures, and hanged ornaments of gold vpon your apparel.
25 “Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
Howe were the mightie slaine in the mids of the battel! O Ionathan, thou wast slaine in thine hie places.
26 Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
Wo is me for thee, my brother Ionathan: very kinde hast thou bene vnto me: thy loue to me was wonderfull, passing the loue of women:
27 “Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”
howe are the mightie ouerthrowen, and the weapons of warre destroyed!