< 2 Sama’ila 1 >

1 Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
Da David efter Sauls Død var vendt tilbage fra Sejren over Amalek og havde opholdt sig to Dage i Ziklag,
2 A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
kom der Tredjedagen en Mand fra Hæren, fra Saul, med sønderrevne Klæder og Jord paa Hovedet, og da han kom hen til David, kastede han sig til Jorden og bøjede sig.
3 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
David spurgte ham: »Hvor kommer du fra?« Han svarede: »Jeg slap bort fra Israels Hær!«
4 Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
David sagde da til ham: »Hvorledes gik det? Fortæl mig det!« Han svarede: »Folket flygtede fra Kampen, og mange af Folket faldt og døde; ogsaa Saul og hans Søn Jonatan er døde.«
5 Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
Da sagde David til den unge Mand, som bragte ham Budet: »Hvoraf ved du, at Saul og hans Søn Jonatan er døde?«
6 Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
Den unge Mand, der bragte ham Budet, svarede: »Det traf sig, at jeg var paa Gilboas Bjerg, og se, Saul stod lænet til sit Spyd, medens Vognene og Rytterne trængte ham;
7 Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
og da han vendte sig om, fik han Øje paa mig og kaldte paa mig; og jeg sagde: Her er jeg!
8 “Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
Da spurgte han mig: Hvem er du? Og jeg svarede: Jeg er en Amalekit!
9 “Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
Saa sagde han til mig: Kom herhen og giv mig Dødsstødet! Thi Krampen har grebet mig, men jeg lever endnu!
10 “Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
Og jeg traadte hen til ham og gav ham Dødsstødet, thi jeg saa, at han ikke kunde leve, naar han faldt om. Saa tog jeg Diademet, han havde paa Hovedet, og et Armbaand, han bar paa Armen, og dem har jeg med hid til min Herre.«
11 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
Da tog David fat i sine Klæder og sønderrev dem, og ligesaa gjorde alle hans Mænd;
12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
og de holdt Klage, græd og fastede til Aften over Saul og hans Søn Jonatan og HERRENS Folk og Israels Hus, fordi de var faldet for Sværdet.
13 Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
Derpaa sagde David til den unge Mand, som havde bragt ham Budet: »Hvor er du fra?« Han svarede: »Jeg er Søn af en Amalekit, der bor her som fremmed.«
14 Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
Da sagde David: »Frygtede du dog ikke for at lægge Haand paa HERRENS Salvede og dræbe ham!«
15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
David kaldte saa paa en af sine Folk og sagde: »Kom herhen og stød ham ned!« Og han slog ham ihjel.
16 Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
Men David sagde til ham: »Dit Blod komme over dit eget Hoved! Thi din egen Mund vidnede imod dig, da du sagde: Jeg gav HERRENS Salvede Dødsstødet!«
17 Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
Da sang David denne Klagesang over Saul og hans Søn Jonatan.
18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
Den skal læres af Judas Sønner; den staar optegnet i de Oprigtiges Bog.
19 “Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
Din Pryd, Israel, ligger dræbt paa dine Høje. Ak, at dog Heltene faldt!
20 “Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
Forkynd det ikke i Gat, ej lyde der Glædesbud paa Askalons Gader, at ikke Filisternes Døtre skal fryde sig, de uomskaarnes Døtre juble!
21 “Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
Gilboas Bjerge! Ej falde Dug og Regn paa eder, I Dødens Vange! Thi Heltenes Skjolde vanæredes der; Sauls Skjold er ej salvet med Olie.
22 “Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
Uden faldnes Blod, uden Heltes Fedt kom Jonatans Bue ikke tilbage, Sauls Sværd ikke sejrløst hjem.
23 Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
Saul og Jonatan, de elskelige, hulde, skiltes ikke i Liv eller Død; hurtigere var de end Ørne, stærkere var de end Løver!
24 “Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
O, Israels Døtre, græd over Saul, som klædte eder yndigt i Purpur, satte Guldsmykker paa eders Klæder!
25 “Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
Ak, at dog Heltene faldt i Slagets Tummel — dræbt ligger Jonatan paa dine Høje!
26 Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
Jeg sørger over dig, Jonatan, Broder, du var mig saare kær; underfuld var mig din Kærlighed, mere end Kvinders Kærlighed.
27 “Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”
Ak, at dog Heltene faldt, Stridsvaabnene lagdes øde!

< 2 Sama’ila 1 >