< 2 Sama’ila 1 >

1 Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
Stalo se pak po smrti Saulově, když se navrátil David od porážky Amalechitských, že pobyl v Sicelechu za dva dni.
2 A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
A aj, dne třetího přišel jeden z vojska Saulova, maje roucho roztržené a prach na hlavě své. Kterýž když přišel k Davidovi, padl na zemi a poklonil se.
3 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
I řekl jemu David: Odkud jdeš? Jemuž odpověděl: Z vojska Izraelského utekl jsem.
4 Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
Opět řekl jemu David: Cože se stalo? Medle, pověz mi. Kterýž odpověděl: To, že utekl lid z boje, a množství lidu padlo a zbito jest; též i Saul i Jonata syn jeho zbiti jsou.
5 Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
Řekl ještě David mládenci, kterýž mu to oznámil: Kterak ty víš, že umřel Saul i Jonata syn jeho?
6 Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
Odpověděl mládenec, kterýž to oznamoval jemu: Náhodou přišel jsem na horu Gelboe, a aj, Saul nalehl byl na kopí své, a vozové i jezdci postihali ho.
7 Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
Kterýžto ohlédna se zpátkem, uzřel mne a zavolal na mne. I řekl jsem: Aj, teď jsem.
8 “Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
Tedy řekl mi: Kdo jsi ty? Odpověděl jsem jemu: Amalechitský jsem.
9 “Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
I řekl mi: Přistup medle sem a zabí mne, nebo mne obklíčila úzkost, a ještě všecka duše má jest ve mně.
10 “Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
Protož stoje nad ním, zabil jsem ho, nebo jsem věděl, že nebude živ po svém pádu. A vzal jsem korunu, kteráž byla na hlavě jeho, i záponu, kteráž byla na rameni jeho, a teď jsem to přinesl ku pánu svému.
11 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
Tedy David uchytiv roucho své, roztrhl je; tolikéž i všickni muži, kteříž s ním byli.
12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
A nesouce smutek, plakali a postili se až do večera pro Saule a pro Jonatu syna jeho, i pro lid Hospodinův a pro dům Izraelský, že padli od meče.
13 Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
Řekl pak David mládenci, kterýž mu to oznámil: Odkud jsi ty? Odpověděl: Syn muže příchozího Amalechitského jsem.
14 Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
Opět mu řekl David: Kterak jsi směl vztáhnouti ruku svou, abys zahubil pomazaného Hospodinova?
15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
A zavolav David jednoho z mládenců, řekl jemu: Přistoupě, oboř se na něj. Kterýžto udeřil ho, tak že umřel.
16 Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
I řekl jemu David: Krev tvá budiž na hlavu tvou, neboť jsou ústa tvá svědčila na tebe, řkouce: Já jsem zabil pomazaného Hospodinova.
17 Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
Tedy naříkal David naříkáním tímto nad Saulem a nad Jonatou synem jeho,
18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
(Přikázav však, aby synové Judovi učeni byli stříleti z luku, jakož psáno v knize Upřímého.):
19 “Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
Ó kráso Izraelská, na výsostech tvých zraněni, jakť jsou padli udatní!
20 “Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
Neoznamujtež v Gát, ani toho ohlašujte na ulicích Aškalon, aby se neveselily dcery Filistinských, a neplésaly dcery neobřezaných.
21 “Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
Ó hory Gelboe, ani rosa, ani déšť nespadej na vás, ani tu buď pole úrodné; nebo tam jest povržen štít udatných, štít Saulův, jako by nebyl pomazán olejem.
22 “Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
Od krve raněných a od tuku udatných lučiště Jonatovo nikdy zpět neodskočilo, a meč Saulův nenavracoval se prázdný.
23 Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
Saul a Jonata milí a utěšení v životě svém, také při smrti své nejsou rozloučeni. Nad orlice bystřejší, nad lvy silnější byli.
24 “Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
Dcery Izraelské, plačte Saule, kterýž vás odíval červcem dvakrát barveným rozkošně, kterýž dával ozdoby zlaté na roucha vaše.
25 “Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
Ach, jakť jsou padli udatní u prostřed boje? Jonata na výsostech tvých zabit jest.
26 Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
Velice jsem po tobě teskliv, bratře můj Jonato. Byl jsi mi příjemný náramně; vzácnější u mne byla milost tvá nežli milost žen.
27 “Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”
Ach, jakť jsou padli udatní, a zahynula odění válečná.

< 2 Sama’ila 1 >