< 2 Bitrus 1 >

1 Siman Bitrus, bawa da kuma manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga waɗanda ta wurin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi sun sami bangaskiya mai daraja irin tamu.
Simon Pierre, serviteur et apôtre de Jésus-Christ, à ceux qui, par la justice de notre Dieu et du Sauveur Jésus-Christ, ont reçu en partage une foi de même prix que la nôtre:
2 Alheri da salama su zama naku a yalwace ta wurin sanin Allah da Yesu Ubangijinmu.
Que la grâce et la paix vous soient multipliées par la connaissance de Dieu et de Jésus, notre Seigneur!
3 Ikonsa na Allahntaka ya ba mu kome da muke bukata don rayuwa da kuma tsoron Allah ta wurin sanin wanda ya kira mu ta wurin ɗaukakarsa da nagartarsa.
Sa divine puissance nous a fait don de tout ce qui contribue à la vie et à la piété, en nous faisant connaître Celui, qui nous a appelés par sa gloire et par sa vertu;
4 Ta wurin waɗannan ya ba mu alkawaransa masu girma da kuma masu daraja, domin ta wurinsu ku iya yin tarayya cikin Allahntakarsa, ku kuma kuɓuta daga lalatar da take cikin duniya wadda mugayen sha’awace-sha’awace suke jawowa.
— et, par elles, nous avons été mis en possession des plus précieuses et des plus grandes promesses, afin que, par leur moyen, vous deveniez participants de la nature divine, en fuyant la corruption qui règne dans le monde par la convoitise.
5 Saboda haka, ku yi iyakar ƙoƙari ku ƙara wa bangaskiyarku nagarta; ga nagarta kuwa, ku ƙara mata sani;
Faites donc aussi, de votre côté, tous vos efforts pour joindre à votre foi la vertu, à la vertu la science,
6 ga sani kuma ku ƙara masa kamunkai; ga kamunkai kuma ku ƙara da daurewa; ga daurewa kuwa ku ƙara da tsoron Allah;
à la science la tempérance, à la tempérance la patience, à la patience la piété,
7 ga tsoron Allah kuma ku ƙara da nuna alheri ga’yan’uwa; ga nuna alheri ga’yan’uwa kuma ku ƙara da ƙauna.
à la piété l'amour fraternel, et à l'amour fraternel la charité.
8 Domin in kuna ƙaruwa a waɗannan halaye, za su kāre ku daga rashin tasiri da rayuwa na rashin amfani cikin saninku na Ubangijinmu Yesu Kiristi.
En effet, si ces grâces se trouvent en vous et si elles y abondent, elles ne vous laisseront ni oisifs, ni stériles dans la connaissance de notre Seigneur Jésus-Christ.
9 Amma in wani ba shi da su, ba shi da hangen nesa ke nan kuma makaho ne, ya kuma manta cewa an tsarkake shi daga zunubansa na dā.
Mais celui à qui elles manquent est un homme qui a la vue courte, un aveugle; il a oublié la purification de ses péchés d'autrefois.
10 Saboda haka’yan’uwana, ku ƙara aniya wajen tabbatar da kiranku da zaɓenku da aka yi. Gama in kuka yi waɗannan abubuwa, ba za ku taɓa fāɗuwa ba,
Appliquez-vous donc, frères, à affermir votre vocation et votre élection. En faisant cela, vous ne broncherez jamais;
11 za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. (aiōnios g166)
et ainsi vous sera largement accordée l'entrée dans le royaume éternel de notre Seigneur et Sauveur Jésus-Christ. (aiōnios g166)
12 Saboda haka kullum zan tuna muku da waɗannan, ko da yake kun sansu kun kuma kahu ƙwarai cikin gaskiyar da kuke da ita yanzu.
Voilà pourquoi je ne cesserai pas de vous faire ressouvenir de ces choses, quoique vous les connaissiez bien et que vous soyez affermis dans la vérité présente.
13 A ganina ya dace in tunashe ku muddin ina raye cikin tentin wannan jiki,
Je regarde néanmoins comme mon devoir, aussi longtemps que je suis dans cette tente, de vous tenir en éveil par mes avertissements;
14 domin na sani na kusa in ajiye shi a gefe, yadda Ubangijinmu Yesu Kiristi ya nuna mini a sarari.
car je sais que je dois bientôt quitter cette tente, comme notre Seigneur Jésus-Christ me l'a déclaré.
15 Zan kuwa yi iyakacin ƙoƙari in ga cewa bayan rabuwata kullum za ku iya tuna da waɗannan abubuwa.
Mais j'aurai soin qu'après mon départ, vous puissiez toujours conserver le souvenir de ce que je vous ai dit.
16 Ba mu bi tatsuniyoyin da aka ƙaga da wayo sa’ad da muka gaya muku game da ikon Ubangijinmu Yesu Kiristi da zuwansa ba, sai dai mu shaidu ne na ɗaukakarsa mai girma da muka gani da ido.
En effet, ce n'est pas en suivant des fables habilement composées, que nous vous avons fait connaître la puissance et l'avènement de notre Seigneur Jésus-Christ; c'est pour avoir vu sa majesté de nos propres yeux.
17 Gama ya sami girma da ɗaukaka daga Allah Uba sa’ad da murya ta zo masa daga Mafificiyar Ɗaukaka cewa, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; da shi nake jin daɗi ƙwarai.”
Car il reçut honneur et gloire de la part de Dieu, son Père, lorsque la Majesté suprême lui adressa cette parole: «Celui-ci est mon Fils bien-aimé, en qui j'ai mis toute mon affection.»
18 Mu kanmu mun ji wannan muryar da ta zo daga sama sa’ad da muke tare da shi a kan dutse mai tsarki.
Nous-mêmes, nous avons entendu cette voix venant du ciel, quand nous étions avec lui sur la sainte montagne.
19 Muna kuwa da maganar annabawa da aka ƙara tabbatar mana, zai fi kyau in kuka lura da ita, kamar hasken da yake haskakawa a wuri mai duhu, har yă zuwa wayewar gari da kuma haskakawar tauraron asubahi a zukatanku.
Et nous tenons pour d'autant plus certaine la parole des prophètes, — à laquelle vous faites bien de prêter attention, comme à une lampe qui brille dans un lieu obscur, jusqu'à ce que le jour commence à luire et que l'étoile du matin se lève dans vos coeurs.
20 Gaba da kome dai, dole ku gane cewa babu annabcin Nassin da ya fito daga fassarar annabi da kansa.
Avant tout, sachez bien que nulle prophétie de l'Écriture n'est affaire d'interprétation privée.
21 Gama annabci bai taɓa samo tushensa daga nufin mutum ba, sai dai mutane sun yi magana daga Allah yayinda Ruhu Mai Tsarki ya bishe su.
Car jamais aucune prophétie n'est procédée de la volonté d'un homme; mais c'est poussés par l'Esprit saint que des hommes ont parlé de la part de Dieu.

< 2 Bitrus 1 >