< 2 Bitrus 1 >
1 Siman Bitrus, bawa da kuma manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga waɗanda ta wurin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi sun sami bangaskiya mai daraja irin tamu.
Simon Peter, a bondservant and Apostle of Jesus Christ: To those to whom there has been allotted the same precious faith as that which is ours through the righteousness of our God and of our Saviour Jesus Christ.
2 Alheri da salama su zama naku a yalwace ta wurin sanin Allah da Yesu Ubangijinmu.
May more and more grace and peace be granted to you in a full knowledge of God and of Jesus our Lord,
3 Ikonsa na Allahntaka ya ba mu kome da muke bukata don rayuwa da kuma tsoron Allah ta wurin sanin wanda ya kira mu ta wurin ɗaukakarsa da nagartarsa.
seeing that His divine power has given us all things that are needful for life and godliness, through our knowledge of Him who has appealed to us by His own glorious perfections.
4 Ta wurin waɗannan ya ba mu alkawaransa masu girma da kuma masu daraja, domin ta wurinsu ku iya yin tarayya cikin Allahntakarsa, ku kuma kuɓuta daga lalatar da take cikin duniya wadda mugayen sha’awace-sha’awace suke jawowa.
It is by means of these that He has granted us His precious and wondrous promises, in order that through them you may, one and all, become sharers in the very nature of God, having completely escaped the corruption which exists in the world through earthly cravings.
5 Saboda haka, ku yi iyakar ƙoƙari ku ƙara wa bangaskiyarku nagarta; ga nagarta kuwa, ku ƙara mata sani;
But for this very reason--adding, on your part, all earnestness-- along with your faith, manifest also a noble character: along with a noble character, knowledge;
6 ga sani kuma ku ƙara masa kamunkai; ga kamunkai kuma ku ƙara da daurewa; ga daurewa kuwa ku ƙara da tsoron Allah;
along with knowledge, self-control; along with self-control, power of endurance;
7 ga tsoron Allah kuma ku ƙara da nuna alheri ga’yan’uwa; ga nuna alheri ga’yan’uwa kuma ku ƙara da ƙauna.
along with power of endurance, godliness; along with godliness, brotherly affection; and along with brotherly affection, love.
8 Domin in kuna ƙaruwa a waɗannan halaye, za su kāre ku daga rashin tasiri da rayuwa na rashin amfani cikin saninku na Ubangijinmu Yesu Kiristi.
If these things exist in you, and continually increase, they prevent your being either idle or unfruitful in advancing towards a full knowledge of our Lord Jesus Christ.
9 Amma in wani ba shi da su, ba shi da hangen nesa ke nan kuma makaho ne, ya kuma manta cewa an tsarkake shi daga zunubansa na dā.
For the man in whom they are lacking is blind and cannot see distant objects, in that he has forgotten that he has been cleansed from his old sins.
10 Saboda haka’yan’uwana, ku ƙara aniya wajen tabbatar da kiranku da zaɓenku da aka yi. Gama in kuka yi waɗannan abubuwa, ba za ku taɓa fāɗuwa ba,
For this reason, brethren, be all the more in earnest to make sure that God has called you and chosen you; for it is certain that so long as you practise these things, you will never stumble.
11 za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. (aiōnios )
And so a triumphant admission into the eternal Kingdom of our Lord and Saviour Jesus Christ will be freely granted to you. (aiōnios )
12 Saboda haka kullum zan tuna muku da waɗannan, ko da yake kun sansu kun kuma kahu ƙwarai cikin gaskiyar da kuke da ita yanzu.
For this reason I shall always persist in reminding you of these things, although you know them and are stedfast believers in truth which you already possess.
13 A ganina ya dace in tunashe ku muddin ina raye cikin tentin wannan jiki,
But I think it right, so long as I remain in the body, my present dwelling-place, to arouse you by such reminders.
14 domin na sani na kusa in ajiye shi a gefe, yadda Ubangijinmu Yesu Kiristi ya nuna mini a sarari.
For I know that the time for me to lay aside my body is now rapidly drawing near, even as our Lord Jesus Christ has revealed to me.
15 Zan kuwa yi iyakacin ƙoƙari in ga cewa bayan rabuwata kullum za ku iya tuna da waɗannan abubuwa.
So on every possible occasion I will also do my best to enable you to recall these things after my departure.
16 Ba mu bi tatsuniyoyin da aka ƙaga da wayo sa’ad da muka gaya muku game da ikon Ubangijinmu Yesu Kiristi da zuwansa ba, sai dai mu shaidu ne na ɗaukakarsa mai girma da muka gani da ido.
For when we made known to you the power and Coming of our Lord Jesus Christ, we were not eagerly following cleverly devised legends, but we had been eye-witnesses of His majesty.
17 Gama ya sami girma da ɗaukaka daga Allah Uba sa’ad da murya ta zo masa daga Mafificiyar Ɗaukaka cewa, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; da shi nake jin daɗi ƙwarai.”
He received honour and glory from God the Father, and out of the wondrous glory words such as these were spoken to Him, "This is My dearly-loved Son, in whom I take delight."
18 Mu kanmu mun ji wannan muryar da ta zo daga sama sa’ad da muke tare da shi a kan dutse mai tsarki.
And we ourselves heard these words come from Heaven, when we were with Him on the holy mountain.
19 Muna kuwa da maganar annabawa da aka ƙara tabbatar mana, zai fi kyau in kuka lura da ita, kamar hasken da yake haskakawa a wuri mai duhu, har yă zuwa wayewar gari da kuma haskakawar tauraron asubahi a zukatanku.
And in the written word of prophecy we have something more permanent; to which you do well to pay attention--as to a lamp shining in a dimly-lighted place--until day dawns and the morning star rises in your hearts.
20 Gaba da kome dai, dole ku gane cewa babu annabcin Nassin da ya fito daga fassarar annabi da kansa.
But, above all, remember that no prophecy in Scripture will be found to have come from the prophet's own prompting;
21 Gama annabci bai taɓa samo tushensa daga nufin mutum ba, sai dai mutane sun yi magana daga Allah yayinda Ruhu Mai Tsarki ya bishe su.
for never did any prophecy come by human will, but men sent by God spoke as they were impelled by the Holy Spirit.