< 2 Bitrus 1 >

1 Siman Bitrus, bawa da kuma manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga waɗanda ta wurin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi sun sami bangaskiya mai daraja irin tamu.
Simon Peter, servant and apostle of Jesus Christ, unto them who have obtained, equally precious, faith, with us, in the righteousness of our God, and Saviour Jesus Christ,
2 Alheri da salama su zama naku a yalwace ta wurin sanin Allah da Yesu Ubangijinmu.
Favour unto you, and peace, be multiplied, in the personal knowledge of God and of Jesus our Lord; —
3 Ikonsa na Allahntaka ya ba mu kome da muke bukata don rayuwa da kuma tsoron Allah ta wurin sanin wanda ya kira mu ta wurin ɗaukakarsa da nagartarsa.
As, all things, suited for life and godliness his divine power, unto us, hath given, through the personal knowledge of him that hath called us through glory and excellence, —
4 Ta wurin waɗannan ya ba mu alkawaransa masu girma da kuma masu daraja, domin ta wurinsu ku iya yin tarayya cikin Allahntakarsa, ku kuma kuɓuta daga lalatar da take cikin duniya wadda mugayen sha’awace-sha’awace suke jawowa.
Through which, his precious, and very great, promises, have, unto us, been given, in order that, through these, ye might become sharers in a divine nature—escaping the corruption that is in the world by coveting.
5 Saboda haka, ku yi iyakar ƙoƙari ku ƙara wa bangaskiyarku nagarta; ga nagarta kuwa, ku ƙara mata sani;
And, for this very reason also—adding, on your part, all diligence, supply, in your faith, excellence, and, in your excellence, knowledge,
6 ga sani kuma ku ƙara masa kamunkai; ga kamunkai kuma ku ƙara da daurewa; ga daurewa kuwa ku ƙara da tsoron Allah;
And, in your knowledge, self-control, and, in your self-control, endurance, and, in your endurance, godliness,
7 ga tsoron Allah kuma ku ƙara da nuna alheri ga’yan’uwa; ga nuna alheri ga’yan’uwa kuma ku ƙara da ƙauna.
And, in your godliness, brotherly affection, and, in your brotherly affection, love.
8 Domin in kuna ƙaruwa a waɗannan halaye, za su kāre ku daga rashin tasiri da rayuwa na rashin amfani cikin saninku na Ubangijinmu Yesu Kiristi.
These things, unto you, belonging and abounding, neither idle nor unfruitful, constitute you, regarding the personal knowledge of our Lord Jesus Christ;
9 Amma in wani ba shi da su, ba shi da hangen nesa ke nan kuma makaho ne, ya kuma manta cewa an tsarkake shi daga zunubansa na dā.
For, he to whom these things are not present, is, blind, seeing only what is near, having come, to forget, his purification from his old sins.
10 Saboda haka’yan’uwana, ku ƙara aniya wajen tabbatar da kiranku da zaɓenku da aka yi. Gama in kuka yi waɗannan abubuwa, ba za ku taɓa fāɗuwa ba,
Wherefore, all the more, brethren, give diligence to be making, firm, your calling and election; for, these things, doing, in nowise shall ye stumble at any time,
11 za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. (aiōnios g166)
For, thus, shall richly be further supplied unto you—the entrance into the age-abiding kingdom of our Lord and Saviour Jesus Christ. (aiōnios g166)
12 Saboda haka kullum zan tuna muku da waɗannan, ko da yake kun sansu kun kuma kahu ƙwarai cikin gaskiyar da kuke da ita yanzu.
Wherefore, I shall be certain to be, always, putting you in remembrance concerning these things, —although, indeed, ye know them, and have become confirmed in the present truth;
13 A ganina ya dace in tunashe ku muddin ina raye cikin tentin wannan jiki,
Right, nevertheless, I account it—as long as I am in this tent, to be stirring you up by putting you in remembrance,
14 domin na sani na kusa in ajiye shi a gefe, yadda Ubangijinmu Yesu Kiristi ya nuna mini a sarari.
Knowing that, speedy, is the putting off of my tent—even as, our Lord Jesus Christ also, made clear to me:
15 Zan kuwa yi iyakacin ƙoƙari in ga cewa bayan rabuwata kullum za ku iya tuna da waɗannan abubuwa.
Yea, I will give diligence also, that, at every time, ye may be able, after my own departure, to be keeping up the remembrance of, these very things.
16 Ba mu bi tatsuniyoyin da aka ƙaga da wayo sa’ad da muka gaya muku game da ikon Ubangijinmu Yesu Kiristi da zuwansa ba, sai dai mu shaidu ne na ɗaukakarsa mai girma da muka gani da ido.
For, not as having followed, cleverly devised stories, made we known unto you the power and presence of our Lord Jesus Christ, but as having been made, spectators, of his majesty.
17 Gama ya sami girma da ɗaukaka daga Allah Uba sa’ad da murya ta zo masa daga Mafificiyar Ɗaukaka cewa, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; da shi nake jin daɗi ƙwarai.”
For, when he received from God the Father honour and glory, a voice, being borne to him such as this, by the magnificent glory—My Son, the beloved, is, this, in whom, I, delight,
18 Mu kanmu mun ji wannan muryar da ta zo daga sama sa’ad da muke tare da shi a kan dutse mai tsarki.
Even this voice, we, heard, when, out of heaven, it was borne, we being, with him, in the holy mount.
19 Muna kuwa da maganar annabawa da aka ƙara tabbatar mana, zai fi kyau in kuka lura da ita, kamar hasken da yake haskakawa a wuri mai duhu, har yă zuwa wayewar gari da kuma haskakawar tauraron asubahi a zukatanku.
And we have, more firm, the prophetic word; —whereunto ye are doing, well, to take heed, —as unto a lamp shining in a dusky place, —until, day, shall dawn, and, a day-star, shall arise in your hearts: —
20 Gaba da kome dai, dole ku gane cewa babu annabcin Nassin da ya fito daga fassarar annabi da kansa.
Of this, first, taking note—that, no prophecy of scripture, becometh, self-solving;
21 Gama annabci bai taɓa samo tushensa daga nufin mutum ba, sai dai mutane sun yi magana daga Allah yayinda Ruhu Mai Tsarki ya bishe su.
For not, by will of man, was prophecy brought in, at any time, but, as, by Holy Spirit, they were borne along, spake, men, from God.

< 2 Bitrus 1 >