< 2 Bitrus 3 >
1 Abokaina ƙaunatattu, wannan ita ce wasiƙata ta biyu gare ku. Na rubuta su biyun su zama abin tuni don su faɗakar da ku ga tunani mai kyau.
IET kisin likau kariau, me i inting wong komail, kompok kan, pwen kataman kin komail o kapirada ngen omail makelekel.
2 Ina so ku tuna da kalmomin da annabawa masu tsarki na dā suka faɗa da kuma umarnin da Ubangijinmu da Mai Cetonmu ya bayar ta wurin manzanninku.
Pwe komail en tamanda masan en saukop saraui kan, kusoned en Kaun o Saunkamaur, me wanporon oko, me pakadar wong komail, wa dong komail.
3 Da farko dai, dole ku fahimci wannan cewa a kwanakin ƙarshe masu ba’a za su zo suna ba’a, suna bin mugayen sha’awace-sha’awacensu.
O iet eta komail en asa, ni imwin ran akan aramas lalaue pan pwarado, me pan weweid ni pein ar inong sued.
4 Za su ce, “Ina wannan ‘dawowar’ da ya yi alkawari ne? Tun mutuwar kakanninmu, kome yana tafiya kamar yadda yake tun farkon halitta.”
Indada: Ia kilel en a pan kotido? Pwe sang ni ran o, sam akan melar kokodo lel met, meakaros kin dueta nin tapi o.
5 Amma da gangan suke manta cewa tun dā can ta wurin maganar Allah sammai suka kasance aka kuma yi ƙasa daga ruwa ta wurin ruwa kuma.
Pwe irail kin men ponsasa, me masia lang akan o sappa eu mia nan pil o, ap pwarada sang nan pil ki masan en Kot.
6 Ta wurin waɗannan ruwan ne aka nutsar, aka kuma hallakar da duniya ta wancan lokaci.
I me sappa en mas o okilar nolik lapalap.
7 Ta wurin wannan magana ce aka ajiye sammai da ƙasa na yanzu domin wuta, an ajiye su kuma don ranar hukunci da hallaka ta mutane marasa tsoron Allah.
Pil dueta lang akan o sappa en met nekinek kita masan ota ong kisiniai ni ran en kadeik o kampan aramas me san Kot akan.
8 Amma kada ku manta da wannan abu guda ɗaya, abokaina ƙaunatattu. Ga Ubangiji kwana ɗaya kamar shekaru dubu ne, shekaru dubu kuma kamar kwana ɗaya ne.
Kompok kan, iet eta komail en asa, me ran ta ieu o par kid ras pena ta ren Kaun o, o par kid o ran eu dupeneta.
9 Ubangiji ba mai jinkiri ba ne wajen cika alkawarinsa, yadda waɗansunku suka fahimci jinkiri. Yana haƙuri da ku, ba ya so wani yă hallaka, sai dai kowa yă kai ga tuba.
Kaun o sota kotin kapwandela inau o, duen akai kin kiki ong, pwe a kotin kanongama ong komail, pwe a sota kotin mauki, akai en lokidokila, pwe karos en wilikapala.
10 Amma ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo. Sammai za su ɓace da ruri, abubuwan da suke cikinsu za su ƙone, ƙasa kuma da dukan abin da yake cikinta za su tonu.
A ran en Kaun o pan pwarado dueta lipirap amen. I dokan lang akan pan mor pasang ni morong lapalap o tapipa kan pan pei pasang ki kisiniai kel, o sappa o a dipisou kan pan rongala.
11 Da yake za a hallaka dukan abubuwa ta haka, waɗanne irin mutane ne ya kamata ku zama? Ya kamata ku yi rayuwar tsarki da ta tsoron Allah,
Ari, ma mepukat karos pan ola, iaduen a pan re omail ni omail wiawia mau o lelapok,
12 yayinda kuke zuba ido ga zuwan ranar Allah kuna gaggauta zuwanta. Wannan rana za tă kawo wa sammai hallaka ta ƙunan wuta, abubuwa kuma za su narke don zafi.
Pwe komail kin auiaui o inong iong ran en Kot, me lang akan pan rong kila kisiniai, o tapipa kan pei pasang, pwe karakar muletok.
13 Amma bisa ga alkawarinsa muna zuba ido ga sabuwar sama da kuma sabuwar ƙasa, inda adalci zai yi zama.
A kitail kin auiaui lang kap akan o sappa kap, wasa me lamalam pung pan wiaui, duen a kotin inaukidar.
14 Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kuna zuba ido ga wannan, sai ku yi matuƙar ƙoƙari don a same ku ba tabo, sai dai zaman salama da shi.
Kompok kan, pweki omail auiaui mepukat, komail en nantiong, pwe komail en diarokada re a so samin, o so sapung ni popol.
15 Ku yi zaman sanin cewa haƙurin Ubangijinmu yana nufin ceto ne, kamar yadda ƙaunataccen ɗan’uwanmu Bulus ma ya rubuta muku da hikimar da Allah ya ba shi.
Pwe komail asa duen kanongama en atail Kaun, pwe i kamaur pa’mail, duen ri atail Paulus kompok inting wong komail er ni lolekong, me ko ong i.
16 Haka yake rubutu cikin dukan wasiƙunsa, yana magana a cikinsu a kan waɗannan al’amura. Wasiƙunsa sun ƙunshi waɗansu abubuwa masu wuyar fahimta, waɗanda jahilai da kuma waɗanda ba tsayayyu ba ne suke murɗe ma’anarsu, kamar yadda suke yi da sauran Nassosi, ta haka suke jawo wa kansu hallaka.
Duen a kasokasoi nan a kisin likau karos, a akai wasa me apwal en dedeki, me sololekong o so lolin akan kin kawukila, dueta ar pil kawukila masan tei kan, me pan kare ong irail pein ar lokidokila.
17 Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kun riga kun san wannan, sai ku zauna a faɗake don kada a ɗauke hankalinku ta wurin kuskuren marasa bin dokan nan har ku fāɗi daga matsayinku.
Kompok kan, pweki omail asa mepukat, komail kalaka, pwe komail der sapung kila padak en me sued akan, ap pupedi sang katengeteng komail.
18 Sai dai ku yi girma cikin alheri da sanin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka ta tabbata yanzu da har abada! Amin. (aiōn )
A komail kairida ni mak o lolekongki padak en atail Kaun o Saunkamaur Iesus Kristus. I me kon ong en ale wau metet o kokolata lel ong ni ran soutuk. (aiōn )