< 2 Bitrus 3 >
1 Abokaina ƙaunatattu, wannan ita ce wasiƙata ta biyu gare ku. Na rubuta su biyun su zama abin tuni don su faɗakar da ku ga tunani mai kyau.
Voilà déjà la seconde lettre que je vous écris, mes bien-aimés, dans celle-ci, comme dans la première, je tâche de réveiller vos bons sentiments;
2 Ina so ku tuna da kalmomin da annabawa masu tsarki na dā suka faɗa da kuma umarnin da Ubangijinmu da Mai Cetonmu ya bayar ta wurin manzanninku.
je vous rappelle les prédictions des saints prophètes, et les préceptes de notre Seigneur et Sauveur transmis par vos apôtres.
3 Da farko dai, dole ku fahimci wannan cewa a kwanakin ƙarshe masu ba’a za su zo suna ba’a, suna bin mugayen sha’awace-sha’awacensu.
Sachez surtout ceci: pendant les derniers jours viendront des moqueurs pleins d'ironie, qui ne se laisseront conduire que par leurs propres passions,
4 Za su ce, “Ina wannan ‘dawowar’ da ya yi alkawari ne? Tun mutuwar kakanninmu, kome yana tafiya kamar yadda yake tun farkon halitta.”
et qui diront: «Eh bien! que devient la promesse de son apparition? Depuis que nos pères sont morts, tout continue à se passer comme depuis le commencement du monde!»
5 Amma da gangan suke manta cewa tun dā can ta wurin maganar Allah sammai suka kasance aka kuma yi ƙasa daga ruwa ta wurin ruwa kuma.
Ils affectent d'ignorer qu'il y a eu autrefois des cieux et une terre sortis de l'eau, et formés au moyen de l'eau sur la parole de Dieu;
6 Ta wurin waɗannan ruwan ne aka nutsar, aka kuma hallakar da duniya ta wancan lokaci.
par suite, le monde d'alors périt submergé dans l'eau.
7 Ta wurin wannan magana ce aka ajiye sammai da ƙasa na yanzu domin wuta, an ajiye su kuma don ranar hukunci da hallaka ta mutane marasa tsoron Allah.
Quant aux cieux et à la terre actuels, ils sont conservés sur cette même parole de Dieu, et réservés pour le feu qui s'allumera le jour du jugement et de la destruction des impies.
8 Amma kada ku manta da wannan abu guda ɗaya, abokaina ƙaunatattu. Ga Ubangiji kwana ɗaya kamar shekaru dubu ne, shekaru dubu kuma kamar kwana ɗaya ne.
Il est une chose que vous ne devez pas oublier, bien-aimés, c'est qu'un jour, devant le Seigneur, est comme mille années et que «Mille années sont comme un jour».
9 Ubangiji ba mai jinkiri ba ne wajen cika alkawarinsa, yadda waɗansunku suka fahimci jinkiri. Yana haƙuri da ku, ba ya so wani yă hallaka, sai dai kowa yă kai ga tuba.
Le Seigneur n'est pas en retard pour l'exécution de sa promesse; certaines personnes croient qu'il y a du retard; mais il use de patience envers vous, voulant que personne ne périsse, mais que tous arrivent à la repentance.
10 Amma ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo. Sammai za su ɓace da ruri, abubuwan da suke cikinsu za su ƙone, ƙasa kuma da dukan abin da yake cikinta za su tonu.
Le jour du Seigneur viendra comme un voleur; alors les cieux disparaîtront avec fracas; les éléments embrasés se fondront, et la terre et tout ce qu'elle renferme sera consumé.
11 Da yake za a hallaka dukan abubuwa ta haka, waɗanne irin mutane ne ya kamata ku zama? Ya kamata ku yi rayuwar tsarki da ta tsoron Allah,
Puisque tout doit se fondre ainsi, quelle sainte conduite, quelle, piété ne devez-vous pas montrer,
12 yayinda kuke zuba ido ga zuwan ranar Allah kuna gaggauta zuwanta. Wannan rana za tă kawo wa sammai hallaka ta ƙunan wuta, abubuwa kuma za su narke don zafi.
attendant et hâtant la venue du jour de Dieu (c'est à cause de ce jour que les cieux se seront fondus dans le feu, et que les éléments embrasés se seront dissous).
13 Amma bisa ga alkawarinsa muna zuba ido ga sabuwar sama da kuma sabuwar ƙasa, inda adalci zai yi zama.
Quant à nous, nous attendons, selon sa promesse, des cieux nouveaux et une terre nouvelle où la justice habitera!
14 Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kuna zuba ido ga wannan, sai ku yi matuƙar ƙoƙari don a same ku ba tabo, sai dai zaman salama da shi.
C'est pourquoi, bien-aimés, pleins de cette attente, faites des efforts pour qu'il vous trouve en paix, sans tache, sans reproche;
15 Ku yi zaman sanin cewa haƙurin Ubangijinmu yana nufin ceto ne, kamar yadda ƙaunataccen ɗan’uwanmu Bulus ma ya rubuta muku da hikimar da Allah ya ba shi.
considérez la patience que montre notre Seigneur comme chose fort propre à notre salut, ainsi que notre bien-aimé frère Paul, selon la sagesse qui lui a été donnée,
16 Haka yake rubutu cikin dukan wasiƙunsa, yana magana a cikinsu a kan waɗannan al’amura. Wasiƙunsa sun ƙunshi waɗansu abubuwa masu wuyar fahimta, waɗanda jahilai da kuma waɗanda ba tsayayyu ba ne suke murɗe ma’anarsu, kamar yadda suke yi da sauran Nassosi, ta haka suke jawo wa kansu hallaka.
vous l'a aussi écrit; il le fait d'ailleurs dans toutes les lettres où il parle de ces sortes de choses, lettres dans lesquelles certains passages sont difficiles à comprendre, dont les ignorants et les esprits mobiles tordent le sens, comme, du reste, les autres Écritures, pour leur propre perdition.
17 Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kun riga kun san wannan, sai ku zauna a faɗake don kada a ɗauke hankalinku ta wurin kuskuren marasa bin dokan nan har ku fāɗi daga matsayinku.
Vous voilà prévenus, bien-aimés; soyez donc sur vos gardes, de peur que, entraînés, vous aussi, par les séductions de ces misérables, vous ne veniez à déchoir, à perdre votre fermeté.
18 Sai dai ku yi girma cikin alheri da sanin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka ta tabbata yanzu da har abada! Amin. (aiōn )
Croissez dans la grâce et dans la connaissance de notre Seigneur et Sauveur Jésus-Christ. A lui soit la gloire maintenant et jusqu'au jour de l'éternité! (aiōn )