< 2 Bitrus 3 >
1 Abokaina ƙaunatattu, wannan ita ce wasiƙata ta biyu gare ku. Na rubuta su biyun su zama abin tuni don su faɗakar da ku ga tunani mai kyau.
This letter which I am now writing to you, dear friends, is my second letter. In both my letters I seek to revive in your honest minds the memory of certain things,
2 Ina so ku tuna da kalmomin da annabawa masu tsarki na dā suka faɗa da kuma umarnin da Ubangijinmu da Mai Cetonmu ya bayar ta wurin manzanninku.
so that you may recall the words spoken long ago by the holy Prophets, and the commandments of our Lord and Saviour given you through your Apostles.
3 Da farko dai, dole ku fahimci wannan cewa a kwanakin ƙarshe masu ba’a za su zo suna ba’a, suna bin mugayen sha’awace-sha’awacensu.
But, above all, remember that, in the last days, men will come who make a mock at everything--men governed only by their own passions,
4 Za su ce, “Ina wannan ‘dawowar’ da ya yi alkawari ne? Tun mutuwar kakanninmu, kome yana tafiya kamar yadda yake tun farkon halitta.”
and, asking, "What has become of His promised Return? For from the time our forefathers fell asleep all things continue as they have been ever since the creation of the world."
5 Amma da gangan suke manta cewa tun dā can ta wurin maganar Allah sammai suka kasance aka kuma yi ƙasa daga ruwa ta wurin ruwa kuma.
For they are wilfully blind to the fact that there were heavens which existed of old, and an earth, the latter arising out of water and extending continuously through water, by the command of God;
6 Ta wurin waɗannan ruwan ne aka nutsar, aka kuma hallakar da duniya ta wancan lokaci.
and that, by means of these, the then existing race of men was overwhelmed with water and perished.
7 Ta wurin wannan magana ce aka ajiye sammai da ƙasa na yanzu domin wuta, an ajiye su kuma don ranar hukunci da hallaka ta mutane marasa tsoron Allah.
But the present heavens and the present earth are, by the command of the same God, kept stored up, reserved for fire in preparation for a day of judgement and of destruction for the ungodly.
8 Amma kada ku manta da wannan abu guda ɗaya, abokaina ƙaunatattu. Ga Ubangiji kwana ɗaya kamar shekaru dubu ne, shekaru dubu kuma kamar kwana ɗaya ne.
But there is one thing, dear friends, which you must not forget. With the Lord one day resembles a thousand years and a thousand years resemble one day.
9 Ubangiji ba mai jinkiri ba ne wajen cika alkawarinsa, yadda waɗansunku suka fahimci jinkiri. Yana haƙuri da ku, ba ya so wani yă hallaka, sai dai kowa yă kai ga tuba.
The Lord is not slow in fulfilling His promise, in the sense in which some men speak of slowness. But He bears patiently with you, His desire being that no one should perish but that all should come to repentance.
10 Amma ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo. Sammai za su ɓace da ruri, abubuwan da suke cikinsu za su ƙone, ƙasa kuma da dukan abin da yake cikinta za su tonu.
The day of the Lord will come like a thief--it will be a day on which the heavens will pass away with a rushing noise, the elements be destroyed in the fierce heat, and the earth and all the works of man be utterly burnt up.
11 Da yake za a hallaka dukan abubuwa ta haka, waɗanne irin mutane ne ya kamata ku zama? Ya kamata ku yi rayuwar tsarki da ta tsoron Allah,
Since all these things are thus pre-destined to dissolution, what sort of men ought you to be found to be in all holy living and godly conduct,
12 yayinda kuke zuba ido ga zuwan ranar Allah kuna gaggauta zuwanta. Wannan rana za tă kawo wa sammai hallaka ta ƙunan wuta, abubuwa kuma za su narke don zafi.
eagerly looking forward to the coming of the day of God, by reason of which the heavens, all ablaze, will be destroyed, and the elements will melt in the fierce heat?
13 Amma bisa ga alkawarinsa muna zuba ido ga sabuwar sama da kuma sabuwar ƙasa, inda adalci zai yi zama.
But in accordance with His promise we are expecting new heavens and a new earth, in which righteousness will dwell.
14 Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kuna zuba ido ga wannan, sai ku yi matuƙar ƙoƙari don a same ku ba tabo, sai dai zaman salama da shi.
Therefore, dear friends, since you have these expectations, earnestly seek to be found in His presence, free from blemish or reproach, in peace.
15 Ku yi zaman sanin cewa haƙurin Ubangijinmu yana nufin ceto ne, kamar yadda ƙaunataccen ɗan’uwanmu Bulus ma ya rubuta muku da hikimar da Allah ya ba shi.
And always regard the patient forbearance of our Lord as salvation, as our dear brother Paul also has written to you in virtue of the wisdom granted to him.
16 Haka yake rubutu cikin dukan wasiƙunsa, yana magana a cikinsu a kan waɗannan al’amura. Wasiƙunsa sun ƙunshi waɗansu abubuwa masu wuyar fahimta, waɗanda jahilai da kuma waɗanda ba tsayayyu ba ne suke murɗe ma’anarsu, kamar yadda suke yi da sauran Nassosi, ta haka suke jawo wa kansu hallaka.
That is what he says in all his letters, when speaking in them of these things. In those letters there are some statements hard to understand, which ill-taught and unprincipled people pervert, just as they do the rest of the Scriptures, to their own ruin.
17 Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kun riga kun san wannan, sai ku zauna a faɗake don kada a ɗauke hankalinku ta wurin kuskuren marasa bin dokan nan har ku fāɗi daga matsayinku.
You, therefore, dear friends, having been warned beforehand, must continually be on your guard so as not to be led astray by the false teaching of immoral men nor fall from your own stedfastness.
18 Sai dai ku yi girma cikin alheri da sanin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka ta tabbata yanzu da har abada! Amin. (aiōn )
But be always growing in the grace and knowledge of our Lord and Saviour Jesus Christ. To Him be all glory, both now and to the day of Eternity! (aiōn )