< 2 Bitrus 3 >

1 Abokaina ƙaunatattu, wannan ita ce wasiƙata ta biyu gare ku. Na rubuta su biyun su zama abin tuni don su faɗakar da ku ga tunani mai kyau.
Consider, most beloved, this second epistle which I am writing to you, in which I stir up, by admonition, your sincere mind,
2 Ina so ku tuna da kalmomin da annabawa masu tsarki na dā suka faɗa da kuma umarnin da Ubangijinmu da Mai Cetonmu ya bayar ta wurin manzanninku.
so that you may be mindful of those words that I preached to you from the holy prophets, and of the precepts of the Apostles of your Lord and Savior.
3 Da farko dai, dole ku fahimci wannan cewa a kwanakin ƙarshe masu ba’a za su zo suna ba’a, suna bin mugayen sha’awace-sha’awacensu.
Know this first: that in the last days there will arrive deceitful mockers, walking according to their own desires,
4 Za su ce, “Ina wannan ‘dawowar’ da ya yi alkawari ne? Tun mutuwar kakanninmu, kome yana tafiya kamar yadda yake tun farkon halitta.”
saying: “Where is his promise or his advent? For from the time that the fathers have slept, all things have continued just as they were from the beginning of creation.”
5 Amma da gangan suke manta cewa tun dā can ta wurin maganar Allah sammai suka kasance aka kuma yi ƙasa daga ruwa ta wurin ruwa kuma.
But they willfully ignore this: that the heavens existed first, and that the earth, from water and through water, was established by the Word of God.
6 Ta wurin waɗannan ruwan ne aka nutsar, aka kuma hallakar da duniya ta wancan lokaci.
By water, the former world then, having been inundated with water, perished.
7 Ta wurin wannan magana ce aka ajiye sammai da ƙasa na yanzu domin wuta, an ajiye su kuma don ranar hukunci da hallaka ta mutane marasa tsoron Allah.
But the heavens and the earth that exist now were restored by the same Word, being reserved unto fire on the day of judgment, and unto the perdition of impious men.
8 Amma kada ku manta da wannan abu guda ɗaya, abokaina ƙaunatattu. Ga Ubangiji kwana ɗaya kamar shekaru dubu ne, shekaru dubu kuma kamar kwana ɗaya ne.
Yet truly, let this one thing not escape notice, most beloved, that with the Lord one day is like a thousand years, and a thousand years is like one day.
9 Ubangiji ba mai jinkiri ba ne wajen cika alkawarinsa, yadda waɗansunku suka fahimci jinkiri. Yana haƙuri da ku, ba ya so wani yă hallaka, sai dai kowa yă kai ga tuba.
The Lord is not delaying his promise, as some imagine, but he does act patiently for your sake, not wanting anyone to perish, but wanting all to be turned back to penance.
10 Amma ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo. Sammai za su ɓace da ruri, abubuwan da suke cikinsu za su ƙone, ƙasa kuma da dukan abin da yake cikinta za su tonu.
Then the day of the Lord shall arrive like a thief. On that day, the heavens shall pass away with great violence, and truly the elements shall be dissolved with heat; then the earth, and the works that are within it, shall be completely burned up.
11 Da yake za a hallaka dukan abubuwa ta haka, waɗanne irin mutane ne ya kamata ku zama? Ya kamata ku yi rayuwar tsarki da ta tsoron Allah,
Therefore, since all these things will be dissolved, what kind of people ought you to be? In behavior and in piety, be holy,
12 yayinda kuke zuba ido ga zuwan ranar Allah kuna gaggauta zuwanta. Wannan rana za tă kawo wa sammai hallaka ta ƙunan wuta, abubuwa kuma za su narke don zafi.
waiting for, and hurrying toward, the advent of the day of the Lord, by which the burning heavens shall be dissolved, and the elements shall melt from the heat of the fire.
13 Amma bisa ga alkawarinsa muna zuba ido ga sabuwar sama da kuma sabuwar ƙasa, inda adalci zai yi zama.
Yet truly, in accord with his promises, we are looking forward to the new heavens and the new earth, in which justice lives.
14 Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kuna zuba ido ga wannan, sai ku yi matuƙar ƙoƙari don a same ku ba tabo, sai dai zaman salama da shi.
Therefore, most beloved, while awaiting these things, be diligent, so that you may be found to be immaculate and unassailable before him, in peace.
15 Ku yi zaman sanin cewa haƙurin Ubangijinmu yana nufin ceto ne, kamar yadda ƙaunataccen ɗan’uwanmu Bulus ma ya rubuta muku da hikimar da Allah ya ba shi.
And let the longsuffering of our Lord be considered salvation, as also our most beloved brother Paul, according to the wisdom given to him, has written to you,
16 Haka yake rubutu cikin dukan wasiƙunsa, yana magana a cikinsu a kan waɗannan al’amura. Wasiƙunsa sun ƙunshi waɗansu abubuwa masu wuyar fahimta, waɗanda jahilai da kuma waɗanda ba tsayayyu ba ne suke murɗe ma’anarsu, kamar yadda suke yi da sauran Nassosi, ta haka suke jawo wa kansu hallaka.
just as he also spoke in all of his epistles about these things. In these, there are certain things which are difficult to understand, which the unlearned and the unsteady distort, as they also do the other Scriptures, to their own destruction.
17 Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kun riga kun san wannan, sai ku zauna a faɗake don kada a ɗauke hankalinku ta wurin kuskuren marasa bin dokan nan har ku fāɗi daga matsayinku.
But since you, brothers, know these things beforehand, be cautious, lest by being drawn into the error of the foolish, you may fall away from your own steadfastness.
18 Sai dai ku yi girma cikin alheri da sanin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka ta tabbata yanzu da har abada! Amin. (aiōn g165)
Yet truly, increase in grace and in the knowledge of our Lord and Savior Jesus Christ. To him be glory, both now and in the day of eternity. Amen. (aiōn g165)

< 2 Bitrus 3 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water