< 2 Bitrus 3 >

1 Abokaina ƙaunatattu, wannan ita ce wasiƙata ta biyu gare ku. Na rubuta su biyun su zama abin tuni don su faɗakar da ku ga tunani mai kyau.
Ljubljeni, pišem evo već drugu poslanicu. U objema opomenom budim vaš zdrav razbor
2 Ina so ku tuna da kalmomin da annabawa masu tsarki na dā suka faɗa da kuma umarnin da Ubangijinmu da Mai Cetonmu ya bayar ta wurin manzanninku.
da se sjetite riječi što ih prorekoše sveti proroci i zapovijedi apostola vaših, zapovijedi Gospodinove i Spasiteljeve.
3 Da farko dai, dole ku fahimci wannan cewa a kwanakin ƙarshe masu ba’a za su zo suna ba’a, suna bin mugayen sha’awace-sha’awacensu.
Znajte ponajprije ovo: u posljednje će se dane pojaviti podrugljivi izrugivači; povoditi će se za svojim požudama
4 Za su ce, “Ina wannan ‘dawowar’ da ya yi alkawari ne? Tun mutuwar kakanninmu, kome yana tafiya kamar yadda yake tun farkon halitta.”
i pitati: “Što je s obećanjem njegova Dolaska? Jer i otkad Oci pomriješe, sve ostaje kao što bijaše od početka stvorenja.”
5 Amma da gangan suke manta cewa tun dā can ta wurin maganar Allah sammai suka kasance aka kuma yi ƙasa daga ruwa ta wurin ruwa kuma.
Ta oni naumice zaboravljaju da nebesa bijahu odavna i da zemlja na Božju riječ posta iz vode i po vodi.
6 Ta wurin waɗannan ruwan ne aka nutsar, aka kuma hallakar da duniya ta wancan lokaci.
Na isti način ondašnji svijet propade vodom potopljen.
7 Ta wurin wannan magana ce aka ajiye sammai da ƙasa na yanzu domin wuta, an ajiye su kuma don ranar hukunci da hallaka ta mutane marasa tsoron Allah.
A sadašnja nebesa i zemlja istom su riječju pohranjena za oganj i čuvaju se za Dan suda i propasti bezbožnih ljudi.
8 Amma kada ku manta da wannan abu guda ɗaya, abokaina ƙaunatattu. Ga Ubangiji kwana ɗaya kamar shekaru dubu ne, shekaru dubu kuma kamar kwana ɗaya ne.
Jedno, ljubljeni, ne smetnite s uma: jedan je dan kod Gospodina kao tisuću godina, a tisuću godina kao jedan dan.
9 Ubangiji ba mai jinkiri ba ne wajen cika alkawarinsa, yadda waɗansunku suka fahimci jinkiri. Yana haƙuri da ku, ba ya so wani yă hallaka, sai dai kowa yă kai ga tuba.
Ne kasni Gospodin ispuniti obećanje, kako ga neki sporim smatraju, nego je strpljiv prema vama jer neće da tko propadne, nego hoće da svi prispiju k obraćenju.
10 Amma ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo. Sammai za su ɓace da ruri, abubuwan da suke cikinsu za su ƙone, ƙasa kuma da dukan abin da yake cikinta za su tonu.
Kao tat će doći Dan Gospodnji u koji će nebesa trijeskom uminuti, počela se, užarena, raspasti, a zemlja i djela na njoj razotkriti.
11 Da yake za a hallaka dukan abubuwa ta haka, waɗanne irin mutane ne ya kamata ku zama? Ya kamata ku yi rayuwar tsarki da ta tsoron Allah,
Kad se sve tako ima raspasti, kako li treba da se svi vi ističete u svetu življenju i pobožnosti
12 yayinda kuke zuba ido ga zuwan ranar Allah kuna gaggauta zuwanta. Wannan rana za tă kawo wa sammai hallaka ta ƙunan wuta, abubuwa kuma za su narke don zafi.
iščekujući i pospješujući dolazak Dana Božjega u koji će se nebesa, zapaljena, raspasti i počela, užarena, rastaliti.
13 Amma bisa ga alkawarinsa muna zuba ido ga sabuwar sama da kuma sabuwar ƙasa, inda adalci zai yi zama.
Ta po obećanju njegovu iščekujemo nova nebesa i zemlju novu, gdje pravednost prebiva.
14 Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kuna zuba ido ga wannan, sai ku yi matuƙar ƙoƙari don a same ku ba tabo, sai dai zaman salama da shi.
Zato, ljubljeni, dok to iščekujete, uznastojte da mu budete neokaljani i besprijekorni, u miru.
15 Ku yi zaman sanin cewa haƙurin Ubangijinmu yana nufin ceto ne, kamar yadda ƙaunataccen ɗan’uwanmu Bulus ma ya rubuta muku da hikimar da Allah ya ba shi.
A strpljivost Gospodina našega spasenjem smatrajte, kako vam i ljubljeni brat naš Pavao napisa po mudrosti koja mu je dana.
16 Haka yake rubutu cikin dukan wasiƙunsa, yana magana a cikinsu a kan waɗannan al’amura. Wasiƙunsa sun ƙunshi waɗansu abubuwa masu wuyar fahimta, waɗanda jahilai da kuma waɗanda ba tsayayyu ba ne suke murɗe ma’anarsu, kamar yadda suke yi da sauran Nassosi, ta haka suke jawo wa kansu hallaka.
Tako u svim poslanicama gdje o tome govori. U njima ima ponešto nerazumljivo, što neupućeni i nepostojani iskrivljuju, kao i ostala Pisma - sebi na propast.
17 Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kun riga kun san wannan, sai ku zauna a faɗake don kada a ɗauke hankalinku ta wurin kuskuren marasa bin dokan nan har ku fāɗi daga matsayinku.
Vi dakle, ljubljeni pošto ste upozoreni, čuvajte se da ne biste, zavedeni bludnjom razularenika, otpali od svoje postojanosti.
18 Sai dai ku yi girma cikin alheri da sanin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka ta tabbata yanzu da har abada! Amin. (aiōn g165)
A rastite u milosti i spoznanju Gospodina našega i Spasitelja Isusa Krista! Njemu slava i sada i do u dan vječnosti! Amen! (aiōn g165)

< 2 Bitrus 3 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water