< 2 Bitrus 2 >
1 Amma a dā akwai annabawan ƙarya a cikin mutane, kamar yadda za a sami malaman ƙarya a cikinku. A ɓoye za su shigar da karkataccen koyarwa mai hallaka, har ma su yi mūsun Ubangiji mai iko duka wanda ya saye su suna kawo wa kansu hallaka farat ɗaya.
Були ж і лжепророки між людьми, як і між вами будуть лжеучителї, котрі введуть єресї погибелі, і відцуравшись викупившого їх Владики, приведуть на себе скору погибіль.
2 Da yawa za su bi hanyoyinsu na rashin kunya su kuma sa a rena hanyar gaskiya.
І многі підуть за їх погибіллю, котрі дорогу правди хулити муть,
3 Cikin kwaɗayinsu waɗannan malaman ƙarya za su cuce ku da tatsuniyoyin da suka ƙaga. Hukuncinsu yana a rataye a kansu tun da daɗewa, hallakarsu kuma ba ta barci.
і в зажерливості придуманими словами вас підходити муть, для котрих суд з давнього часу не гаїть ся, і погибіль їх не дрімає.
4 Gama in har Allah bai ƙyale mala’iku sa’ad da suka yi zunubi ba, amma ya tura su cikin lahira, domin a tsare su don hukunci; (Tartaroō )
Бо коли Бог ангелів, що згрішили, не пощадив, а кинув їх в окови пекельної темряви, і передав, щоб хоронено їх на суд; (Tartaroō )
5 in har bai ƙyale duniya ta dā ba sa’ad da ya kawo ambaliya a kan mutanenta marasa tsoron Allah, amma ya kiyaye Nuhu, mai wa’azin adalci, da kuma waɗansu bakwai;
і коли первого сьвіта не пощадив, а самовосьмого Ноя, проповідника правди, охоронив, повідь на сьвіт нечестивих допустивши;
6 in har ya hukunta biranen Sodom da Gomorra ta wurin ƙone su suka zama toka, ya kuma maishe su misali na abin da zai faru da marasa tsoron Allah;
і коли городи Содому й Гоморру засудив на руїну, обернувши в попіл, і поставивши, яко приклад для будучих безбожників,
7 in kuwa har ya ceci Lot, mai adalci, wanda ya damu ainun da ƙazamar rayuwar mutane marasa bin doka;
а ізбавив праведного Лота, омерзенного розпустним життєм безбожників;
8 (adon kuwa abin da adalin nan ya yi, ya kuma gani, sa’ad da yake a cikinsu, sai kowace rana yakan ji ciwon aikinsu na kangara a zuciyarsa mai adalci)
(живучи бо між ними праведник той, дивлячись і слухаючи про беззаконні діла, день в день мучив праведну душу; )
9 in haka ne, to, Ubangiji ya san yadda zai ceci mutane masu tsoron Allah daga gwaje-gwaje, yă kuma tsare marasa adalci don ranar hukunci, har yă zuwa ranar shari’a.
то й знав Господь побожних з покуси вибавляти, неправедних же хоронити про судний день на муки,
10 Wannan gaskiya ce musamman ga waɗanda suke bin sha’awace-sha’awacen lalaci na mutuntaka, suna kuma rena masu mulki. Da ƙarfin hali da kuma girman kai, waɗannan mutane ba sa tsoro kawo zargin ɓata sunan talikan sama;
найбільше ж тих, що ходять в слїд за тілом в нечистому хотінню, і зневажають начальство; що сьміливі, самолюбні, не лякають ся хулити власть,
11 duk da haka ko mala’iku ma da suka fi su ƙarfi suka kuma fi su iko, ba sa kawo irin wannan zargi na ɓata suna game da waɗannan talikai a gaban Ubangiji.
хоч ангели, кріпостю і силою більшими бувши, не приносять проти них перед Господа докоряючого суду.
12 Amma waɗannan mutane suna yin saɓo a kan abubuwan da ba su fahimta ba. Suna kama da dabbobi marasa hankali, halittun da suke bin abin da jikinsu ya faɗa musu kawai, waɗanda aka haifa don a kama a hallaka, kuma kamar dabbobi su ma za su hallaka.
Сї ж як безсловесні зьвірі, природні, що родять ся на лови і забиттє, хулять, чого не розуміють, і в зотлїнню своїм загинуть,
13 Za a yi musu sakamako da muguntar da suka yi. A ra’ayinsu jin daɗi shi ne a yi annashuwa da rana tsaka. Su ƙazamai ne marasa kunya, suna cike da jin daɗin sha’awace-sha’awacensu yayinda suke cin biki tare da ku.
і нагороду неправди приймуть. Солодкими вважають вони дочасні розкоші; вони самий сором і беззаконнє, розкошують в обманьстві своїм, їдаючи з вами;
14 Idanunsu sun cike da zina, ba sa ƙoshi da yin zunubi; suna jarrabtar waɗanda ba tsayayyu ba; gwanaye ne a kan kwaɗayi, la’anannun iri!
очі мають повні прелюбодїяння і неперестаючого гріха, надять душі неутверджені; серце в них навчене до зажерливосте, се - діти прокляття;
15 Sun bar miƙaƙƙiyar hanya suka bauɗe suna bin hanyar Bala’am ɗan Beyor, wanda ya yi ƙaunar hakkin mugunta.
котрі, опустивши праву дорогу, заблудили, йдучи дорогою Валаама, сина Восорового, що полюбив неправедну нагороду,
16 Amma an tsawata masa saboda laifinsa ta wurin jaki, dabbar da ba ta magana, wadda ta yi magana da muryar mutum ta kuma kwaɓi haukan annabin.
тільки ж мав кару за своє беззаконнє, бо підяремник нїмий, проговоривши чоловічим голосом, остановив нерозум пророка.
17 Waɗannan mutane maɓulɓulai ne babu ruwa da kuma hazon da guguwar iska take kora. An shirya matsanancin duhu dominsu.
Се жерела безводні, хмари, хуртовиною гонимі, котрим чорна темрява на віки захована. ()
18 Gama suna surutai banza na girman kai, ta wurin son bin fasikanci na mutuntaka, sukan jan hankulan mutanen da suke kuɓucewa daga waɗancan masu zama cikin kuskure.
Промовляючи бо великими і марними словами, принаджують хотїннєм тїла та розпустою тих, що ледво утїкли від живучих в блудї,
19 Suna yin musu alkawarin’yanci, yayinda su kansu bayi ne ga aikin lalata gama mutum bawa ne ga duk abin da ya mallake shi.
обіцяючи їм волю, самі бувши слуги зотлїння; хто бо ким подужаний, того він і невольник.
20 In har sun kuɓuta daga lalacin duniya ta wurin sanin Ubangijinmu da kuma Mai Cetonmu Yesu Kiristi sai suka sāke koma a cikin lalacin, har ya rinjaye su, za su fi muni a ƙarshe fiye da farko.
Коли бо, утїкши від нечистоти сьвіта через пізнаннє Господа і Спаса Ісуса Христа, однакож, знов замотавшись, бувають подужані, то останнє їх - гірше первого.
21 Zai fi musu kyau da ba su taɓa sanin hanyar adalci ba, fiye da a ce sun sani sa’an nan su juya bayansu ga umarni mai tsarkin nan da aka ba su.
Лучче би їм було не пізнати дороги правди, як, пізнавши, одвернутись від переданої їм сьвятої заповіди.
22 A kansu karin maganan nan gaskiya ce, “Kare ya koma kan amansa,” da kuma, “Alade da aka yi wa wanka, ya koma birgimarsa cikin laka.”
Довело ся ж їм по правдивій приповістї: "Пес вертаєть ся до своєї блювотини", а свиня, скупавшись, (іде) валятись у калюжу.