< 2 Bitrus 2 >
1 Amma a dā akwai annabawan ƙarya a cikin mutane, kamar yadda za a sami malaman ƙarya a cikinku. A ɓoye za su shigar da karkataccen koyarwa mai hallaka, har ma su yi mūsun Ubangiji mai iko duka wanda ya saye su suna kawo wa kansu hallaka farat ɗaya.
aparaM pUrvvakAlE yathA lOkAnAM madhyE mithyAbhaviSyadvAdina upAtiSThan tathA yuSmAkaM madhyE'pi mithyAzikSakA upasthAsyanti, tE svESAM krEtAraM prabhum anaggIkRtya satvaraM vinAzaM svESu varttayanti vinAzakavaidharmmyaM guptaM yuSmanmadhyam AnESyanti|
2 Da yawa za su bi hanyoyinsu na rashin kunya su kuma sa a rena hanyar gaskiya.
tatO 'nEkESu tESAM vinAzakamArgaM gatESu tEbhyaH satyamArgasya nindA sambhaviSyati|
3 Cikin kwaɗayinsu waɗannan malaman ƙarya za su cuce ku da tatsuniyoyin da suka ƙaga. Hukuncinsu yana a rataye a kansu tun da daɗewa, hallakarsu kuma ba ta barci.
aparanjca tE lObhAt kApaTyavAkyai ryuSmattO lAbhaM kariSyantE kintu tESAM purAtanadaNPAjnjA na vilambatE tESAM vinAzazca na nidrAti|
4 Gama in har Allah bai ƙyale mala’iku sa’ad da suka yi zunubi ba, amma ya tura su cikin lahira, domin a tsare su don hukunci; (Tartaroō )
IzvaraH kRtapApAn dUtAn na kSamitvA timirazRgkhalaiH pAtAlE ruddhvA vicArArthaM samarpitavAn| (Tartaroō )
5 in har bai ƙyale duniya ta dā ba sa’ad da ya kawo ambaliya a kan mutanenta marasa tsoron Allah, amma ya kiyaye Nuhu, mai wa’azin adalci, da kuma waɗansu bakwai;
purAtanaM saMsAramapi na kSamitvA taM duSTAnAM saMsAraM jalAplAvanEna majjayitvA saptajanaiH sahitaM dharmmapracArakaM nOhaM rakSitavAn|
6 in har ya hukunta biranen Sodom da Gomorra ta wurin ƙone su suka zama toka, ya kuma maishe su misali na abin da zai faru da marasa tsoron Allah;
sidOmam amOrA cEtinAmakE nagarE bhaviSyatAM duSTAnAM dRSTAntaM vidhAya bhasmIkRtya vinAzEna daNPitavAn;
7 in kuwa har ya ceci Lot, mai adalci, wanda ya damu ainun da ƙazamar rayuwar mutane marasa bin doka;
kintu taiH kutsitavyabhicAribhi rduSTAtmabhiH kliSTaM dhArmmikaM lOTaM rakSitavAn|
8 (adon kuwa abin da adalin nan ya yi, ya kuma gani, sa’ad da yake a cikinsu, sai kowace rana yakan ji ciwon aikinsu na kangara a zuciyarsa mai adalci)
sa dhArmmikO janastESAM madhyE nivasan svIyadRSTizrOtragOcarEbhyastESAm adharmmAcArEbhyaH svakIyadhArmmikamanasi dinE dinE taptavAn|
9 in haka ne, to, Ubangiji ya san yadda zai ceci mutane masu tsoron Allah daga gwaje-gwaje, yă kuma tsare marasa adalci don ranar hukunci, har yă zuwa ranar shari’a.
prabhu rbhaktAn parIkSAd uddharttuM vicAradinanjca yAvad daNPyAmAnAn adhArmmikAn rOddhuM pArayati,
10 Wannan gaskiya ce musamman ga waɗanda suke bin sha’awace-sha’awacen lalaci na mutuntaka, suna kuma rena masu mulki. Da ƙarfin hali da kuma girman kai, waɗannan mutane ba sa tsoro kawo zargin ɓata sunan talikan sama;
vizESatO yE 'mEdhyAbhilASAt zArIrikasukham anugacchanti kartRtvapadAni cAvajAnanti tAnEva (rOddhuM pArayati|) tE duHsAhasinaH pragalbhAzca|
11 duk da haka ko mala’iku ma da suka fi su ƙarfi suka kuma fi su iko, ba sa kawo irin wannan zargi na ɓata suna game da waɗannan talikai a gaban Ubangiji.
aparaM balagauravAbhyAM zrESThA divyadUtAH prabhOH sannidhau yESAM vaiparItyEna nindAsUcakaM vicAraM na kurvvanti tESAm uccapadasthAnAM nindanAd imE na bhItAH|
12 Amma waɗannan mutane suna yin saɓo a kan abubuwan da ba su fahimta ba. Suna kama da dabbobi marasa hankali, halittun da suke bin abin da jikinsu ya faɗa musu kawai, waɗanda aka haifa don a kama a hallaka, kuma kamar dabbobi su ma za su hallaka.
kintu yE buddhihInAH prakRtA jantavO dharttavyatAyai vinAzyatAyai ca jAyantE tatsadRzA imE yanna budhyantE tat nindantaH svakIyavinAzyatayA vinaMkSyanti svIyAdharmmasya phalaM prApsyanti ca|
13 Za a yi musu sakamako da muguntar da suka yi. A ra’ayinsu jin daɗi shi ne a yi annashuwa da rana tsaka. Su ƙazamai ne marasa kunya, suna cike da jin daɗin sha’awace-sha’awacensu yayinda suke cin biki tare da ku.
tE divA prakRSTabhOjanaM sukhaM manyantE nijachalaiH sukhabhOginaH santO yuSmAbhiH sArddhaM bhOjanaM kurvvantaH kalagkinO dOSiNazca bhavanti|
14 Idanunsu sun cike da zina, ba sa ƙoshi da yin zunubi; suna jarrabtar waɗanda ba tsayayyu ba; gwanaye ne a kan kwaɗayi, la’anannun iri!
tESAM lOcanAni paradArAkAgkSINi pApE cAzrAntAni tE canjcalAni manAMsi mOhayanti lObhE tatparamanasaH santi ca|
15 Sun bar miƙaƙƙiyar hanya suka bauɗe suna bin hanyar Bala’am ɗan Beyor, wanda ya yi ƙaunar hakkin mugunta.
tE zApagrastA vaMzAH saralamArgaM vihAya biyOraputrasya biliyamasya vipathEna vrajantO bhrAntA abhavan| sa biliyamO 'pyadharmmAt prApyE pAritOSikE'prIyata,
16 Amma an tsawata masa saboda laifinsa ta wurin jaki, dabbar da ba ta magana, wadda ta yi magana da muryar mutum ta kuma kwaɓi haukan annabin.
kintu nijAparAdhAd bhartsanAm alabhata yatO vacanazaktihInaM vAhanaM mAnuSikagiram uccAryya bhaviSyadvAdina unmattatAm abAdhata|
17 Waɗannan mutane maɓulɓulai ne babu ruwa da kuma hazon da guguwar iska take kora. An shirya matsanancin duhu dominsu.
imE nirjalAni prasravaNAni pracaNPavAyunA cAlitA mEghAzca tESAM kRtE nityasthAyI ghOratarAndhakAraH sanjcitO 'sti| ()
18 Gama suna surutai banza na girman kai, ta wurin son bin fasikanci na mutuntaka, sukan jan hankulan mutanen da suke kuɓucewa daga waɗancan masu zama cikin kuskure.
yE ca janA bhrAntyAcArigaNAt kRcchrENOddhRtAstAn imE 'parimitadarpakathA bhASamANAH zArIrikasukhAbhilASaiH kAmakrIPAbhizca mOhayanti|
19 Suna yin musu alkawarin’yanci, yayinda su kansu bayi ne ga aikin lalata gama mutum bawa ne ga duk abin da ya mallake shi.
tEbhyaH svAdhInatAM pratijnjAya svayaM vinAzyatAyA dAsA bhavanti, yataH, yO yEnaiva parAjigyE sa jAtastasya kigkaraH|
20 In har sun kuɓuta daga lalacin duniya ta wurin sanin Ubangijinmu da kuma Mai Cetonmu Yesu Kiristi sai suka sāke koma a cikin lalacin, har ya rinjaye su, za su fi muni a ƙarshe fiye da farko.
trAtuH prabhO ryIzukhrISTasya jnjAnEna saMsArasya malEbhya uddhRtA yE punastESu nimajjya parAjIyantE tESAM prathamadazAtaH zESadazA kutsitA bhavati|
21 Zai fi musu kyau da ba su taɓa sanin hanyar adalci ba, fiye da a ce sun sani sa’an nan su juya bayansu ga umarni mai tsarkin nan da aka ba su.
tESAM pakSE dharmmapathasya jnjAnAprApti rvaraM na ca nirddiSTAt pavitravidhimArgAt jnjAnaprAptAnAM parAvarttanaM|
22 A kansu karin maganan nan gaskiya ce, “Kare ya koma kan amansa,” da kuma, “Alade da aka yi wa wanka, ya koma birgimarsa cikin laka.”
kintu yEyaM satyA dRSTAntakathA saiva tESu phalitavatI, yathA, kukkuraH svIyavAntAya vyAvarttatE punaH punaH| luThituM karddamE tadvat kSAlitazcaiva zUkaraH||