< 2 Bitrus 2 >
1 Amma a dā akwai annabawan ƙarya a cikin mutane, kamar yadda za a sami malaman ƙarya a cikinku. A ɓoye za su shigar da karkataccen koyarwa mai hallaka, har ma su yi mūsun Ubangiji mai iko duka wanda ya saye su suna kawo wa kansu hallaka farat ɗaya.
Bývali pak i falešní proroci v lidu, jakož i mezi vámi budou falešní učitelé, kteříž chytře uvedou sekty zatracení, i toho Pána, kterýž je vykoupil, zapírajíce, uvodíce na sebe rychlé zahynutí.
2 Da yawa za su bi hanyoyinsu na rashin kunya su kuma sa a rena hanyar gaskiya.
A mnozí následovati budou jejich zahynutí, skrze něž cesta pravdy bude v porouhání dávána.
3 Cikin kwaɗayinsu waɗannan malaman ƙarya za su cuce ku da tatsuniyoyin da suka ƙaga. Hukuncinsu yana a rataye a kansu tun da daɗewa, hallakarsu kuma ba ta barci.
A lakomě skrze vymyšlené řeči vámi kupčiti budou; kterýchžto odsouzení již dávno nemešká, a zahynutí jejich nespí.
4 Gama in har Allah bai ƙyale mala’iku sa’ad da suka yi zunubi ba, amma ya tura su cikin lahira, domin a tsare su don hukunci; (Tartaroō )
Nebo poněvadžť Bůh andělům, kteříž zhřešili, neodpustil, ale strhna je do žaláře, řetězům mrákoty oddal, aby k odsouzení chováni byli, (Tartaroō )
5 in har bai ƙyale duniya ta dā ba sa’ad da ya kawo ambaliya a kan mutanenta marasa tsoron Allah, amma ya kiyaye Nuhu, mai wa’azin adalci, da kuma waɗansu bakwai;
I onomu prvnímu světu neodpustil, ale sama osmého Noé, kazatele spravedlnosti, zachoval, když potopu na svět bezbožníků uvedl.
6 in har ya hukunta biranen Sodom da Gomorra ta wurin ƙone su suka zama toka, ya kuma maishe su misali na abin da zai faru da marasa tsoron Allah;
A města Sodomských a Gomorských v popel obrátiv, podvrácením odsoudil, příklad budoucím bezbožníkům na nich ukázav,
7 in kuwa har ya ceci Lot, mai adalci, wanda ya damu ainun da ƙazamar rayuwar mutane marasa bin doka;
A spravedlivého Lota, ztrápeného těch nešlechetníků chlipným obcováním, vytrhl.
8 (adon kuwa abin da adalin nan ya yi, ya kuma gani, sa’ad da yake a cikinsu, sai kowace rana yakan ji ciwon aikinsu na kangara a zuciyarsa mai adalci)
Ten zajisté spravedlivý, bydliv mezi nimi, den ode dne hleděním i slyšením spravedlivou duši nešlechetnými jejich skutky trápil.
9 in haka ne, to, Ubangiji ya san yadda zai ceci mutane masu tsoron Allah daga gwaje-gwaje, yă kuma tsare marasa adalci don ranar hukunci, har yă zuwa ranar shari’a.
Umíť Pán zbožné z pokušení vytrhnouti, nepravých pak ke dni soudu potrestaných dochovati,
10 Wannan gaskiya ce musamman ga waɗanda suke bin sha’awace-sha’awacen lalaci na mutuntaka, suna kuma rena masu mulki. Da ƙarfin hali da kuma girman kai, waɗannan mutane ba sa tsoro kawo zargin ɓata sunan talikan sama;
A zvláště těch, jenž po těle v žádosti nečisté chodí, a vrchností pohrdají, jsou i smělí, sobě se zalibující, neostýchají se důstojnostem porouhati.
11 duk da haka ko mala’iku ma da suka fi su ƙarfi suka kuma fi su iko, ba sa kawo irin wannan zargi na ɓata suna game da waɗannan talikai a gaban Ubangiji.
Ješto andělé, jsouce větší v síle a v moci, nečiní proti nim přede Pánem potupného soudu.
12 Amma waɗannan mutane suna yin saɓo a kan abubuwan da ba su fahimta ba. Suna kama da dabbobi marasa hankali, halittun da suke bin abin da jikinsu ya faɗa musu kawai, waɗanda aka haifa don a kama a hallaka, kuma kamar dabbobi su ma za su hallaka.
Tito pak jako nerozumná hovada, kteráž za přirozením jdou, zplozená k zjímání a k zahynutí, tomu, čemuž nerozumějí, rouhajíce se, v tom svém porušení zahynou,
13 Za a yi musu sakamako da muguntar da suka yi. A ra’ayinsu jin daɗi shi ne a yi annashuwa da rana tsaka. Su ƙazamai ne marasa kunya, suna cike da jin daɗin sha’awace-sha’awacensu yayinda suke cin biki tare da ku.
A tak odplatu nepravosti své ponesou, jakožto ti, kteřížto sobě za rozkoš položili, aby se na každý den v libostech svých kochali, nejsouce než poskvrny a mrzkosti, ti, kteříž s vámi hodujíce, v svých lstech se kochají,
14 Idanunsu sun cike da zina, ba sa ƙoshi da yin zunubi; suna jarrabtar waɗanda ba tsayayyu ba; gwanaye ne a kan kwaɗayi, la’anannun iri!
Oči majíce plné cizoložstva, a bez přestání hřešící, přeluzujíce duše neustavičné, srdce majíce vycvičené v lakomství, synové zlořečenství.
15 Sun bar miƙaƙƙiyar hanya suka bauɗe suna bin hanyar Bala’am ɗan Beyor, wanda ya yi ƙaunar hakkin mugunta.
Kteříž opustivše cestu přímou, zbloudili, následujíce cesty Balámovy, syna Bozorova, kterýž mzdu nepravosti zamiloval.
16 Amma an tsawata masa saboda laifinsa ta wurin jaki, dabbar da ba ta magana, wadda ta yi magana da muryar mutum ta kuma kwaɓi haukan annabin.
Ale měl, od koho by pokárán byl pro svůj výstupek. Nebo jhu poddaná oslice němá, člověčím hlasem promluvivši, zbránila nemoudrosti proroka.
17 Waɗannan mutane maɓulɓulai ne babu ruwa da kuma hazon da guguwar iska take kora. An shirya matsanancin duhu dominsu.
Tiť jsou studnice bez vody, a mlhy vichrem zbouřené, jimžťo mrákota tmy chová se na věčnost. ()
18 Gama suna surutai banza na girman kai, ta wurin son bin fasikanci na mutuntaka, sukan jan hankulan mutanen da suke kuɓucewa daga waɗancan masu zama cikin kuskure.
Nebo přepyšně marné věci vypravujíce, žádostmi těla a chlipnostmi loudí ty, kteříž byli vpravdě utekli od těch, jenž bludu obcují,
19 Suna yin musu alkawarin’yanci, yayinda su kansu bayi ne ga aikin lalata gama mutum bawa ne ga duk abin da ya mallake shi.
Slibujíce jim svobodu, ješto sami jsou služebníci porušení, poněvadž od kohož kdo jest přemožen, tomu jest i v službu podroben.
20 In har sun kuɓuta daga lalacin duniya ta wurin sanin Ubangijinmu da kuma Mai Cetonmu Yesu Kiristi sai suka sāke koma a cikin lalacin, har ya rinjaye su, za su fi muni a ƙarshe fiye da farko.
Jestliže pak ti, jenž ušli poskvrn světa, skrze známost Pána a Spasitele Jezukrista, opět zase v to zapleteni jsouce, přemoženi byli, učiněn jest poslední způsob jejich horší nežli první.
21 Zai fi musu kyau da ba su taɓa sanin hanyar adalci ba, fiye da a ce sun sani sa’an nan su juya bayansu ga umarni mai tsarkin nan da aka ba su.
Lépe by zajisté jim bylo nepoznávati cesty spravedlnosti, nežli po nabytí známosti odvrátiti se od vydaného jim svatého přikázání.
22 A kansu karin maganan nan gaskiya ce, “Kare ya koma kan amansa,” da kuma, “Alade da aka yi wa wanka, ya koma birgimarsa cikin laka.”
Ale přihodilo se jim to, což se v přísloví pravém říkává: Pes navrátil se k vývratku svému, a svině umytá do kaliště bláta.