< 2 Sarakuna 1 >
1 Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
Und Moab fiel von Israel ab nach dem Tode Achabs.
2 Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
Und Achasjah fiel durch das Gitter an seinem Söller in Samaria und ward krank; und er sandte Boten und sprach zu ihnen: Gehet hin und befragt Baal-Sebub, den Gott zu Ekron, ob ich von dieser Krankheit genesen werde?
3 Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
Und der Engel Jehovahs redete zu Elijah, dem Thischbiter: Mache dich auf, gehe hinauf, den Boten des Königs von Samaria entgegen und rede zu ihnen: Ist es, weil gar kein Gott in Israel ist, daß ihr geht und den Baal-Sebub, den Gott von Ekron, befragt?
4 Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
Darum aber spricht also Jehovah: Von dem Bette, darauf du gestiegen, sollst du nicht wieder herabkommen, denn du sollst des Todes sterben! Und Elijah ging hin.
5 Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
Und die Boten kehrten zu ihm zurück und er sprach zu ihnen: Warum kehrt ihr zurück?
6 Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
Sie aber sprachen zu ihm: Es kam ein Mann herauf, uns entgegen, und sprach zu uns: Gehet, kehret zurück zu dem König, der euch gesendet hat, und redet zu ihm: Also spricht Jehovah: Ist es, weil gar kein Gott in Israel ist, daß du sendest, den Baal-Sebub, den Gott von Ekron, zu befragen? Darum sollst du von dem Bette, darauf du hinaufgestiegen, nicht herabsteigen, sondern des Todes sterben.
7 Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
Und er redete zu ihnen: Was war die Weise des Mannes, der heraufkam, euch entgegen und diese Worte zu euch redete?
8 Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
Und sie sprachen zu ihm: Es war ein Mann mit langen Haaren, und mit einem ledernen Leibgurt an seinen Lenden gegürtet; und er sprach: Es ist Elijah, der Thischbiter.
9 Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
Und er sandte an ihn einen Obersten von fünfzig und seine Fünfzig; und er ging zu ihm hinauf, und siehe, er saß auf der Spitz des Berges, und er redete zu ihm: Mann Gottes, der König redet: Komm herab!
10 Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
Und Elijahu antwortete und redete zu dem Obersten der Fünfzig: Und wenn ich ein Mann Gottes bin, so komme Feuer vom Himmel herab und fresse dich und deine Fünfzig. Und Feuer kam vom Himmel herab und fraß ihn und seine Fünfzig.
11 Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
Und er sandte wiederum einen anderen Obersten von fünfzig und seine Fünfzig, zu ihm, und er antwortete und redete zu ihm: Mann Gottes, so spricht der König: Komm eilends herab!
12 Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
Und Elijah antwortete und redete zu ihnen: Wenn ich ein Mann Gottes bin, so komme Feuer vom Himmel herab und fresse dich und deine Fünfzig. Und es kam Feuer Gottes vom Himmel herab und fraß ihn und seine fünfzig.
13 Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
Und er sandte wiederum einen Obersten von fünfzig, den dritten, und seine Fünfzig. Und der dritte Oberst der Fünfzig zog hinauf und kam und beugte seine Knie gegen Elijahu, und flehte ihn an und redete zu ihm: Mann Gottes, laß doch meine Seele und die Seele deiner Knechte, dieser Fünfzig, kostbar sein in deinen Augen!
14 Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
Siehe, Feuer ist vom Himmel herabgekommen und hat die zwei Obersten der ersten fünfzig und ihre Fünfzig gefressen, und nun laß kostbar sein meine Seele in deinen Augen!
15 Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
Und es redete der Engel Jehovahs zu Elijahu: Gehe hinab mit ihm, fürchte dich nicht vor seinem Angesicht. Und er machte sich auf und ging mit ihm hinab zum König.
16 Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
Und er redete zu ihm: So spricht Jehovah: Weil du Boten sandtest, Baal-Sebub, den Gott von Ekron zu befragen, als wäre gar kein Gott in Israel, Sein Wort zu befragen, darum sollst du von dem Bett, darauf du gestiegen bist, nicht herabkommen, sondern des Todes sterben.
17 Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
Und er starb nach dem Worte Jehovahs, das Elijahu geredet. Und König ward Jehoram an seiner Stelle; im zweiten Jahre Jehorams, des Sohnes Jehoschaphats, König von Judah; denn er hatte keinen Sohn.
18 Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?
Und das übrige der Geschichten Achasjahus, was er getan, ist es nicht geschrieben in dem Buche der Tagesgeschichten der Könige Israels?