< 2 Sarakuna 1 >

1 Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
After King Ahab died, [the country of] Moab rebelled against Israel.
2 Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
One day, Ahaziah, [the new king of Israel, ] fell through the wooden slats/boards around the edge of the flat roof [of his palace] in Samaria. He was badly injured, so he summoned some messengers and told them, “Go to Ekron [city in Philistia], and ask their god Baalzebub whether I will (recover/become well).”
3 Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
But an angel from Yahweh said to Elijah, the prophet from Tishbe [town], “The king of Samaria [is sending] some messengers [to Ekron]. Go and meet them and say to them, ‘Is it because there is no God in Israel that you are going to Ekron to ask Baalzebub, the god of those people, [whether you will recover]?
4 Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
Yahweh says [that you should tell King Ahaziah] that he will not recover from his being injured; he will surely die.’”
5 Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
[So Elijah went to meet] the messengers [and told that to them, and they] returned to the king [instead of going to Ekron]. The king asked them, “Why did you return [so soon]?”
6 Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
They replied, “A man came to meet us, and said to us, ‘Return to the king who sent you and tell him that Yahweh says, “(Is it because there no God in Israel that you are sending [messengers] to Ekron to consult Baalzebub, their god?/You seem to think there is no God in Israel, with the result that you are sending [messengers] to Ekron to ask Baalzebub, their god, [whether you will recover].) [RHQ] [Go tell the king that] he will not recover from being injured; instead, he will surely die.”’”
7 Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
The king said to them, “The man who came to meet you and told that to you, what did he look like?”
8 Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
They replied, “He was a hairy man and he had a [wide] leather belt around his waist.” The king exclaimed, “That was Elijah!”
9 Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
Then the king sent an officer with 50 soldiers to seize Elijah. They found Elijah sitting on the top of a hill. The officer called out to him, “Prophet, the king commands that you come down here!”
10 Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
But Elijah replied, “I am a prophet; so, I command that fire come down from the sky and burn up you and your 50 soldiers!” Immediately, fire came down from the sky and completely burned up the officer and his 50 [soldiers].
11 Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
[When the king found out about that, ] he sent another officer with 50 more soldiers. They went [to where Elijah was], and the officer called out to him, “Prophet, the king commands that you come down immediately!”
12 Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
But Elijah replied, “I am a prophet; [to prove that, ] I command that fire come down from the sky and kill you and your soldiers!” Then a fire from God came down from the sky and killed the officer and his soldiers.
13 Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
[When the king heard about that] he sent another officer with 50 more soldiers. [They went to where Elijah was], and the officer prostrated himself in front of Elijah, and said to him, “Prophet, I plead with you, be kind to me and my 50 soldiers, and (do not kill us/allow us to remain alive)!
14 Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
[We know that] two times fire came down from the sky and killed officers and the 50 soldiers who were with them. So now, please be kind to me!”
15 Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
Then the angel from Yahweh said to Elijah, “Go down [and go] with him. Do not be afraid of him.” So Elijah went with them to the king.
16 Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
[When Elijah arrived, ] he said to the king, “This is what Yahweh says: ‘You sent messengers to go to Ekron to ask Baalzebub, their god, [whether you would recover]. You acted as though [RHQ] there is no God in Israel to consult. So you will not recover from being injured; instead, you are going to die!’”
17 Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
So Ahaziah died, which is what Yahweh told Elijah would happen. Ahaziah’s [younger] brother Joram became the new king, when Jehoram, the son of Jehoshaphat, had been ruling Judah for almost two years. Ahaziah’s brother became the king because Ahaziah had no son [to become the king].
18 Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?
[If you want to know about] all the other things that Ahaziah did, they are [RHQ] written in the scroll called ‘The History of the Kings of Israel’.

< 2 Sarakuna 1 >