< 2 Sarakuna 9 >

1 Sai Elisha ya kira wani daga cikin ƙungiyar annabawa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kwalabar mai ka je Ramot Gileyad.
UElisha umprofethi wasebiza omunye wamadodana abaprofethi wathi kuye: Bopha ukhalo lwakho, uthathe lumfuma wamafutha esandleni sakho, uye eRamothi-Gileyadi.
2 Da ka isa can, ka nemi Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi. Ka je wurinsa, ka ja shi gefe daga abokansa, ka shiga da shi ɗaki na ciki.
Nxa ufika khona udinge lapho uJehu indodana kaJehoshafathi indodana kaNimshi, ungene, umsukumise phakathi kwabafowabo, umngenise ekamelweni elingaphakathi.
3 Sa’an nan ka ɗauki kwalabar man ka zuba a kansa, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, na naɗa ka sarkin Isra’ila.’ Sa’an nan ka buɗe ƙofa ka ruga a guje; kada ka ɓata lokaci!”
Ubusuthatha umfuma wamafutha, uwathele ekhanda lakhe uthi: Itsho njalo iNkosi: Ngikugcobile ube yinkosi phezu kukaIsrayeli. Ubusuvula umnyango, ubaleke, ungaphuzi.
4 Sai saurayin nan, annabi, ya tafi Ramot Gileyad.
Lahamba-ke ijaha lelo, ijaha umprofethi, laya eRamothi-Gileyadi.
5 Da ya isa can, sai ya tarar da hafsoshin soji zaune a wuri guda. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka komanda.” Sai Yehu ya ce, “Wanne a cikinmu?” Sai ce, “Dominka, komanda.”
Ekufikeni kwalo, khangela, induna zebutho zazihlezi, lathi: Ngilombiko kuwe, nduna. UJehu wasesithi: Kubani phakathi kwethu sonke? Laselisithi: Kuwe, nduna.
6 Sai Yehu ya tashi ya shiga cikin gida. Sa’an nan annabin ya zuba wa Yehu mai a kā, ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na naɗa ka sarki a bisa jama’ar Ubangiji, wato, Isra’ila.
Wasesukuma, wangena endlini; laselithela amafutha ekhanda lakhe, lathi kuye: Itsho njalo iNkosi, uNkulunkulu kaIsrayeli: Ngikugcobile ukuthi ube yinkosi phezu kwabantu beNkosi, phezu kukaIsrayeli.
7 Za aka hallaka gidan Ahab maigidanka, zan kuma ɗauki fansar jinin bayina annabawa da kuma jinin dukan bayin Ubangiji da Yezebel ta zub da.
Njalo uzatshaya indlu kaAhabi inkosi yakho, ukuze ngiphindisele igazi lenceku zami abaprofethi, legazi lazo zonke inceku zeNkosi, esandleni sikaJezebeli.
8 Dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan kashe dukan’ya’yan Ahab maza a Isra’ila, bayi ko’yantattu.
Yonke-ke indlu kaAhabi izabhubha; njalo ngizaquma asuke kuAhabi ochamela emdulini, lovalelweyo lokhululekileyo koIsrayeli.
9 Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat da kuma kamar gidan Ba’asha ɗan Ahiya.
Njalo ngizakwenza indlu kaAhabi njengendlu kaJerobhowamu indodana kaNebati lanjengendlu kaBahasha indodana kaAhiya.
10 Game da Yezebel kuwa, karnuka za su cinye ta a fili a Yezireyel, ba kuwa wanda zai binne ta.’” Sa’an nan ya buɗe ƙofa ya ruga a guje.
Lezinja zizakudla uJezebeli esabelweni seJizereyeli, njalo kakuyikuba lomngcwabayo. Laselivula umnyango, labaleka.
11 Da Yehu ya koma wurin sauran hafsoshin sai ɗaya daga cikinsu ya tambaye shi, “Lafiya? Me ya kawo wannan mahaukaci a wurinka?” Sai Yehu ya ce, “Ka san mahaukacin nan da irin maganganunsa.”
Kwathi uJehu esephumele encekwini zenkosi yakhe, omunye wathi kuye: Kulungile yini? Luzeleni loluhlanya kuwe? Wasesithi kuzo: Liyamazi lumuntu lenkulumo yakhe.
12 Suka ce masa, “Ba gaskiya ba ne, ka dai faɗa mana.” Yehu ya ce, “Ga abin da ya ce mini, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, na naɗa ka sarki a bisa Isra’ila.’”
Zasezisithi: Manga! Sitshele khathesi. Wasesithi: Ukhulume ukuthi lokuthi kimi esithi: Itsho njalo iNkosi: Ngikugcobile ube yinkosi phezu kukaIsrayeli.
13 Sai suka yi sauri suka ɗauki rigunansu suka shimfiɗa a ƙasa, suka busa kakaki, suka yi ihu, suka ce, “Yehu ne sarki.”
Zaseziphangisa, zathatha, ngulowo lalowo isembatho sakhe, zazibeka ngaphansi kwakhe engqongeni yezikhwelo, zavuthela uphondo, zathi: UJehu uyinkosi!
14 Saboda haka, Yehu ɗan Yehoshafat, ɗan Nimshi, ya ƙulla wa Yoram maƙarƙashiya (To, Yoram da dukan Isra’ila suna kāre Ramot Gileyad daga Hazayel sarkin Aram,
Ngokunjalo uJehu indodana kaJehoshafathi indodana kaNimshi wamenzela ugobe uJoramu. (UJoramu wagcina-ke iRamothi-Gileyadi, yena loIsrayeli wonke, ngenxa kaHazayeli inkosi yeSiriya;
15 amma Sarki Yoram ya koma Yezireyel don yă farfaɗo daga raunukan da Arameyawa suka ji masa a wata gabzawar da ya yi da Hazayel sarkin Aram.) Yehu ya ce, “In haka kuke ji, kada ku bar wani yă sulluɓe daga birnin yă kai labarin Yezireyel.”
kodwa uJehoramu inkosi wayesebuyelele ukwelatshwa eJizereyeli ngamanxeba amaSiriya ayemtshaye wona ekulweni kwakhe loHazayeli inkosi yeSiriya.) UJehu wasesithi: Aluba kuyintando yenu, kakungaphumi ophunyukileyo emzini ukuyabika lokhu eJizereyeli.
16 Sai ya tashi ya ɗauki keken yaƙinsa ya tafi Yezireyel gama Yoram yana hutawa a can. Ga kuma Ahaziya sarkin Yahuda ya je don yă gan shi.
UJehu wasekhwela inqola, waya eJizereyeli, ngoba uJoramu wayelele khona, loAhaziya inkosi yakoJuda wayehle ukuthi abone uJoramu.
17 Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezireyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa’ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.” Sai Yoram ya umarta, “Nemi mahayin doki a aike shi yă tarye su, yă kuma tambaye su, ‘Lafiya?’”
Umlindi wayemi-ke emphotshongweni eJizereyeli, wabona ixuku likaJehu, yena esiza, wathi: Ngibona ixuku. UJehoramu wathi: Thatha umgadi webhiza umthume ukubahlangabeza, athi: Yikuthula yini?
18 Sai mahayin dokin ya hau, ya ruga, ya taryi Yehu, ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Sai Yehu ya ce masa, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.” Sai mai tsaron ya ce wa sarki, “Ɗan saƙon ya kai wurinsu, amma ba ya dawowa.”
Wasehamba umgadi webhiza ukumhlangabeza, wathi: Itsho njalo inkosi: Yikuthula yini? UJehu wasesithi: Ulani lokuthula? Phendukela ngemva kwami. Umlindi wasebika esithi: Isithunywa sesifikile kibo, kodwa kasiphenduki.
19 Saboda haka sarki ya sāke aika mahayin doki na biyu. Sa’ad da ya isa wurinsu sai ya ce, “Ga abin da sarki ya ce, ‘Lafiya?’” Yehu ya ce, “Ina ruwanka da zancen lafiya? Ka shiga layi.”
Yasithuma umgadi webhiza wesibili, wafika kibo wathi: Itsho njalo inkosi: Yikuthula yini? UJehu wasesithi: Ulani lokuthula? Phendukela ngemva kwami.
20 Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma shi ma ba ya dawowa. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa kamar mahaukaci.”
Umlindi wasebika wathi: Usefikile kibo, kodwa kaphenduki. Lokutshayela kufanana lokutshayela kukaJehu indodana kaNimshi, ngoba utshayela okohlanya.
21 Yoram ya umarta, “Haɗa mini keken yaƙi!” Da aka haɗa, sai Yoram sarkin Isra’ila, da Ahaziya sarkin Yahuda, suka hau suka tafi, kowa a keken yaƙinsa, don su taryi Yehu. Suka sadu da shi a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel.
UJehoramu wasesithi: Bophelani. Basebebophela inqola yakhe. UJehoramu inkosi yakoIsrayeli loAhaziya inkosi yakoJuda basebephuma, ngulowo lalowo enqoleni yakhe, baphuma ukuhlangabeza uJehu, bamthola esiqintini sikaNabothi umJizereyeli.
22 Sa’ad da Yoram ya ga Yehu sai ya tambaye shi, “Lafiya kuwa ka zo, Yehu?” Yehu ya ce, “Ina kuwa lafiya, da yake dukan bautar gumaka da bokancin mahaifiyarka Yezebel sun bazu ko’ina?”
Kwasekusithi uJehoramu ebona uJehu wathi: Yikuthula yini, Jehu? Wasesithi: Ukuthula bani, selokhu ukuwula kukaJezebeli unyoko lokuthakatha kwakhe kukunengi kangaka?
23 Yoram ya juya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Cin amana, Ahaziya!”
UJehoramu wasephendula izandla zakhe wabaleka, wathi kuAhaziya: Yinkohliso, Ahaziya!
24 Sai Yehu ya ja bakansa ya harbi Yoram a tsakanin kafaɗunsa. Kibiyar ta same shi a zuciyarsa sai ya fāɗi a cikin keken yaƙinsa.
UJehu wasedonsisisa idandili, watshaya uJehoramu phakathi kweziphanga zakhe, lomtshoko waphuma enhliziyweni yakhe, wasekhothama enqoleni yakhe.
25 Yehu ya ce wa Bidkar, hafsan keken yaƙinsa, “Ka ɗauke shi ka jefar a filin da yake na Nabot mutumin Yezireyel. Ka tuna yadda ni da kai muke a kekunan yaƙi a bayan Ahab mahaifinsa sa’ad da Ubangiji ya yi wannan annabci game da shi,
Wasesithi kuBidikari induna yakhe: Mphakamise, umphosele esiqintini sensimu kaNabothi umJizereyeli; ngoba khumbula mina lawe sigade sobabili ngemva kukaAhabi uyise, iNkosi yamethesa lumthwalo:
26 ‘Jiya na ga jinin Nabot da jinin’ya’yansa, in ji Ubangiji, kuma ba shakka zan ɗauki fansa a wannan fili, in ji Ubangiji.’ Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar da shi a bisa wannan fegi, bisa ga faɗin Ubangiji. Saboda haka, ka ɗauke shi ka jefar a filin, in ji Ubangiji.”
Ngibonile isibili izolo igazi likaNabothi legazi lamadodana akhe, itsho iNkosi, ngizaphindisela kuwe kulesisiqinti, itsho iNkosi. Ngakho-ke mphakamise umphosele kulesisiqinti, njengokwelizwi leNkosi.
27 Sa’ad da Ahaziya sarkin Yahuda ya ga abin da ya faru, sai ya haura hanyar Bet Haggan a guje. Yehu ya bi shi yana ihu, “A kashe shi, shi ma!” Suka ji masa rauni a keken yaƙinsa a hanya zuwa Gur, kusa da Ibileyam amma ya tsere zuwa Megiddo ya mutu a can.
UAhaziya inkosi yakoJuda esebonile lokhu wabaleka, ngendlela yendlu yesivande. UJehu wasexotshana laye, wathi: Mtshayeni laye enqoleni, emqansweni weGuri elingaseIbileyamu. Wasebalekela eMegido, wafela khona.
28 Barorinsa suka ɗauke shi cikin keken yaƙi zuwa Urushalima suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda.
Inceku zakhe zasezimthwala zamusa eJerusalema, zamngcwaba engcwabeni lakhe kuboyise emzini kaDavida.
29 (A shekara ta goma sha ɗaya ta Yoram ɗan Ahab, Ahaziya ya zama sarkin Yahuda.)
Ngomnyaka wetshumi lanye kaJoramu indodana kaAhabi, uAhaziya waba yinkosi phezu kukaJuda.
30 Sa’an nan Yehu ya je Yezireyel. Sa’ad da Yezebel ta sami labari, sai ta sha kwalliya ta gyara gashin kanta, ta zauna tana kallo daga taga.
UJehu esefikile eJizereyeli, uJezebeli wakuzwa. Wasecomba amehlo akhe, wacecisa ikhanda lakhe, walunguza ngewindi.
31 Yayinda Yehu ya shiga ƙofa, sai ta ce, “Lafiya, kai Zimri, mai kashe maigidansa?”
Lapho-ke uJehu engena esangweni, wasesithi: Yikuthula yini, Zimri, mbulali wenkosi yakho?
32 Sai ya ɗaga ido ya dubi tagan ya ce, “Wa yake gefena? Wane ne?” Sai bābānni biyu ko uku suka leƙo suka dube shi.
Wasephakamisela ubuso bakhe ewindini, wathi: Ngubani ongakimi? Ngubani? Kwasekulunguza kuye abathenwa ababili, abathathu.
33 Yehu ya ce musu, “Ku jefa ta ƙasa!” Sai suka jefar da ita, jininta ya fantsama a jikin bango da kuma a jikin dawakai yayinda suke tattaka ta.
Wasesithi: Mphoseleni phansi. Basebemphosela phansi; lelinye legazi lakhe lachaphakela emdulini lemabhizeni; wasemnyathelela phansi.
34 Yehu ya shiga ya ci, ya kuma sha. Ya ce, “Ku san yadda za ku yi da la’ananniyan nan, ku binne ta, gama’yar sarki ce.”
Wasengena wadla wanatha, wathi: Ake libone lo umqalekiswakazi limngcwabe, ngoba uyindodakazi yenkosi.
35 Amma sa’ad da suka je don su binne ta, ba su sami kome ba sai ƙoƙon kanta, ƙafafunta da kuma hannuwanta.
Basebesiyamngcwaba, kodwa kabaficanga lutho olwakhe ngaphandle kokhakhayi lenyawo lempama zezandla.
36 Suka komo suka faɗa wa Yehu, wanda ya ce, “Wannan ita ce maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin bawansa Iliya mutumin Tishbe. A fili, a Yezireyel, karnuka za su cinye naman Yezebel.
Ngakho babuyela bamtshela; wasesithi: Leli yilizwi leNkosi eyalikhuluma ngesandla senceku yayo uElija umTishibi lisithi: Esiqintini seJizereyeli izinja zizakudla inyama kaJezebeli;
37 Gawar Yezebel zai zama kamar juji a ƙasa, a fili, a Yezireyel, har ba wanda zai iya cewa, ‘Wannan Yezebel ce.’”
lesidumbu sikaJezebeli sizakuba njengomquba ebusweni bomhlabathi esiqintini seJizereyeli, ukuze bangathi: Lo nguJezebeli.

< 2 Sarakuna 9 >